labaran “yau shekara takwas kenan muka tsinci labaran a hanyarmu ta zuwa katsina daga abuja, does that mean…”?
Kasa karashe kalamanta tayi saboda jin furucin Salim for the first time, Har lokacin yana maqale a jikinta, yana rawar sanyi kamar mai zazzabi, don dazu gaba daya basu Lura ma da maganar da yayi ba sai yanxu suka tabbatar da bakinshi ya bude.
“Da..ddy…ne ya sa a kashe su, daddy ne naji lokacin, kullum sainayi mafarki, daddy ne….” Yana kaiwa nan ya fashe da kuka yana stammering muryanshi na breaking kamar dan koyo, kallonshi Amar yayi ya soma mashi magana cikin natsuwa “dama kana magana? Meysa Ka rufe bakinka?”
Sauke kanshi kasa yayi yana hawaye “ban…san..ina..iya..mag..na ..ba”
Shuru Amar yayi yana nazari kafin yace “zaka iya tuna abunda ya faru?”
“Yace zai kasheni idan na fada…” Salim ya fada yana stammering
“Waye yace hakan?” Amar ya sake tambayarshi
“Dad…ddy ne” Salim ya amsa shi
Kallon amra Amar yayi yace “waye daddy?”
“Uncle dinmu ne kuma marikin mu wan Abban mu” ta amsa shi kanta a kasa.
Hannu Amar ya miqa mashi ya tako inda yake ya zauna gefenshi “karkiji tsoro, babu abunda zaiyi maka I will protect you, now fada min abunda Ka sani”
Shuru Salim kanshi a kasa kamar mai tsoron magana yace “ranar ne daddy zaije airport zai dauko su abba, Ina son naje Amma Ina tsoro kar a hanani shine na shiga bayan motarshi na boye a kasan motar bai sani ba, Muna cikin tafiya ya tsayar da motar yana waya, na manta abunda ya faru but na…naji lokacin da yake cewa su kashe abba da mami,”
Yana kaiwa nan ya fashe da kuka saida Amar ya bubbuga bayanshi kafin ya cigaba, “inajin haka shine na fito daga bayan motar, nan naga ya fito daga motar tashi, a gabana ina kallo wata trailer tazo ta hau kan wata mota, bansan su waye a cikin motar ba don saida motar ta kama da wuta na hango abba da mami acikin motar…”
Shuru ya sake yi yana nazari kafin ya cigaba “shine daddy ya dawo motar nan ya kamani, yana ganina ya gane naga abunda ya faru don naga Yana bama mai trailer din daya buge motar wani envelop bayan ya buge motar harta kama da wuta kafin ya gudu don kan titin express ne babu mutane sosai, shine daga nan yace min nima zai kasheni, nan ya buga min… wani abu bansan menene ba ya bugamin…uhm na manta daga nan me ya faru don adda tace min nakai wata biyu a kwance ban Tashi ba, amma shine ya kashe abba na gani da idona”
Yana karasowa ya fashe da kuka, shuru sukayi gaba dayansu kowanne jiki shi ya mutu sosai babu sautin dake Tashi a parlorn sai kukan amra da salima,
“Innalillahi wa inna ilaihi rajiun” amra ta furta tana dagowa tana kallonsu, “Wallahi da gaske ne, bazan mantaba lokacin da abun ya faru, bayan fitar dady zaije airport daukan su abba, ni banma san Salim ya bishi ba don saidaga baya yake ce mana Ay tare suka tafi dashi inda akan idanunshi yaga accident din wanda hakan yasa Salim ya fadi saboda razanar da yayi lokacin da aka futo da gawar su don mu bamu samu munga gawar ba,”
Nunfasawa tayi tana ajiyar zuciya kafin ta cigaba, “daga nan ne mukayi kusan wata biyu a asibiti Salim bai Tashi ba kwata kwata, saidaga baya Allah yasa ya Tashi, koda ya tashi bayan mun koma gida da muka tambayeshi incident din, nan ya nuna mana ya manta bazai iya tunawa ba, bayan mun dawo gidan komai ya dan lafa nan muka fara Ganin sauyi a wajen daddy da Yan gidan ma baki daya, mun zama ware a cikin su, wajen kwanciyar mu daban ne dana Yan gidan don bamu da maraba da Yan aikin gidan, ahankali ahankli salim ya fara samun ciwon zuciya wanda koda mukaje asibiti da daddy nan doctor ya shaida Akwai abunda ke damunshi saboda a shekarun shi bai kamata ace ya samu ciwon zuciya ba da depression dole Akwai abunda ke damun shi, nan doctor ya
bashi magunguna muka dawo gida, bayan mun dawo Duk wata daddy zai kawo mana magani a bashi, a maimakon muga sauyi sai mukaga abun nashi yana gaba sosai, kullum cikin jinya yake Har takaiga muka hakura da bashi maganin ma bayan wasu Yan shekaru harna tafi karatu na barsu a gidan.”
Tana kaiwa nan ta fashe da kuka tana hawaye, kafin salima ta cigaba “bayan tafiyar adda, mu kadai muka rage ma juna, munsha wahala sosai inda Har
takaiga bama futa ko Ina kullum Muna daki kamar prisoners, harta school dady yace bazamu yiba saboda…. Saboda na bugama ya Ibrahim kwalba akai saboda yayi kokarin raping dina, shine ya kashe mana zuwa school sannan yace karmu sake mu dunga fitowa daga dakin mu saboda baya son Ganin mu, sau daya suke bamu abunci, babu sabulun wanka, babu kayan kirki ruwan wanka ma gagarar mu yake saboda fanfon toilet din daya lalace ba a gyara ba, babu wanda ke zuwa dubamu kullum Muna zaune a daki, babu hasken fitila saboda globe din ya mutu, Har na fara loosing sight dina na tsawon shekara biyu , karshe dai Har muka fara rashin lafiya, inda Salim baya iya ko motsawa, jikinshi Duk ya shanye, Duk dare sainayi kuka don ban saka ran zai wayi gari da nunfashi ba, ranar da hakan ta faru kuwa da safe bayan mun Tashi naga baya nunfashi, hankalina ya Tashi sosai nan na futo parlor hankali na atashe, koda nazo parlorn ma kallon mahaukaciya sukayi min don gaba daya na futa gayyaci na, allah yaso ya muhammd ya dawo gidan don dana rokesu akan su taimake ni salim zai mutu babu wanda ya kalleni, sai ya Muhammad ne kawai ya iya shugowa dakin mu, shine ma ya kaimu asibiti, daga nan ne bansan inda kaina yake ba saida na Tashi, inda ya Muhammad ya shaida mun aiki da akayi mana nida Salim, kullum shike kula damu Har na tsawon sati biyu, kwatsam sai kuma tafiyar gaggawa tazo mashi inda ya tafi bayan ya shiada min driver zaizo ya maidamu katsina wajen kaka don na rokeshi akan karya maidamu gidan daddy, washe gari kuwa da safe wajen karfe goma saiga galaxy driver yazo, drivern gidan ne, yana zuwa ya daukemu muka kama hanya ta zuwa gida don mu diba kayan mu, Muna kan hanya mummy (hajiya kareema) ta kirashi a waya,bamuyi ne take ce mashi abu saidai naji yana ta rokonta akan zai kawo mu gida kafin ya wuce inda ta umarceshi, karshe dai sai parking yayi yace mu sauka, bayan mun sauka ya shaida mana mu jira shi anan zaije ya dawo karmu taci ko’ina, haka muka zauna muka jirashi na tsawon awa hudu, shuru babu shi babu labarin sa Har yamma tayi, haka muka dunga yawo akan titi Muna kuka babu inda zamuje, cikin ikon Allah Muna zaune wani mutumi yazo yace mana ya muhammd ne ya turo shi akan ya tafi damu, da farko naji tsoro sai daga baya da naji bayanin da yayi na yarda dashi nan muka shiga motarshi muka kama hanya harya kawomu nan gidan wajen ammah, saida muka zo nan ne muka samu kwanciyar hankali saboda ammah bata sanmu ba ta karbe mu hannu bibiyu ta bamu ci ta bamu sha ta suturta mu sannan ya muhammd ya saka Muna school muka cigaba da karatu,” tana karashe ta fashe da matsanancin kuka sosai kamar ranta zai futa
Tunda salima ta fara magana amra ta runtse idanu ta tana hawaye bata taba imaging wahalar da suka sha ba sai yanxu, kuka sosai suka dungayi Harda malam labaran saya dafe kanshi shima yana hawaye, dukda memory dinshi bai dawo ba gaba daya, don Har lokacin komai blurry yake zuwan mashi akanshi,tabbas waennan yayanshi ne yana ji a jikinshi ko ba a fada mashi ba, jininshi ne su.
Amar ne ya katse su da nashi bayanin “bayan Allah ya hadani da aisha a uae inda aure ya hadamu na yarjejeniya akan zata samu katin kasa don ta kawo kannenta nan kasar, da farko ban yarda ba wanda hakan yasa nayi kwakwaran buncike akan ta da kannenta, a bunciken da nayi tabbas ba a yi declaring mutuwar iyayen ta ba,saidai an barshi blank inda akace sunyi accident sun kone, da farko naso nayi buncike saidai kuma daga baya na ajiye don ba hurumin a bane saboda da kanta ta shaida mun iyayenta sun mutu, sannan banma san waye muhammd din da suke magana akai ba saidai nayi amfanin dashi don na kubutar dasu daga cikin wahalar da suka shiga inda matar shi alhaji Mustapha tasa a zubar dasu su shiga duniya, wannan dalilin yasa na kawo su nan gurin ammah”
Shuru kowa yayi babu abunda sukeyi sai hawaye Harda ammah ma dake zaune tana jin wannan masifa irin haka,ace Wai dan uwanka jininka yayi maka wannan rashin imanin, koda yake abun bai girgizasu ba ita da Amar saboda kusan similar abunda sukayi facing kenan watannin da suka wuce achan baya,
Dagowa malam labaran yayi yana hawaye sosai yace “tabbas ko ba a fada min ba waennan yaya na ne, kuka jini na ne, ban mutu ba da raina, dukda Allah bai bayyana min komai ba akan rayuwar da nayi a baya ba, kuzo nan”
Ya karashe yana Mika masu hannu yana hawaye,
Mikewa salima tayi daman kamar jira take tare da Salim suka taho inda yake zaune suna zama ya rungumosu gaba dayansu zuwa jikinshi babu abunda yake furtawa sai “Allah na gode maka,”
Amra dai na zaune kanta a kasa Har lokacin bayanin salima na cinta sosai, babu abunda takeyi sai blaming kanta sosai.
Kuka sosai suka dungayi a jikin malam labaran, ammah ma na daga zaune tana kallonsu tana hawaye Amar dai sauke kanshi yayi kasa bai ce komai ba jikinshi shima ya mutu, suna maqale a jikin malam labaran ya sauko kasa kan knees dinshi yana shirin dukawa kasa, “hajiya bansan da wani baki Zan gode maki ba keda yallabai, kunyi min komai a duniyar nan, bayan ni da kika taimaka Harda yayana marayu, babu abunda Zan iya saka maki dashi saidai nayi maku fatan Alkhairi keda yallabai, Nagode Nagode Nagode yallabai”
Cikin sauri Amar ya miqe tsaye ya taho gabanshi ya daga shi sama ya maidashi kan kujerar ya zauna dashi “dan Allah Kar Ka duka mana ka daina gode mana,dan Allah”
Ammah ce ta share hawayenta ta kalleshi itama tace “ malam labaran Ka daina gode mana ka godewa Allah shine ya kaddara Duk wani abunda ya faru harya hadamu dakai muka taimakeka kuma shine ya hada aisha da Muhammad Har ta sanadiyar hakan ya taimaki kannenta”
Kanshi a kasa ya kasa kallonsu ammah yace “hajiya bazan fasa gode maku ba, dole na gode maku, Kun yi min abunda bazan taba mancewa ba Har naje ga mahallaccina, Kun gama min komai hajiya,”
Komawa Amar yayi mazauninsa ya dan nunfasa yana kallon inda amra take kafin ya kauda kanshi gefe ya fara magana
“Alhamdulillah godiya ta tabbata ga Allah daya bayyana komai, Allah ubangiji ya kauda Duk wata tsautsayi da masifa, zanyi dogon buncike akan wannan alamarin kuma dole justice must be served ”
“Ah ah yallabai karkiyi buncike, na bar su da Allah Duk wanda ya cucemu, bana fatan past memory na ya dawo saboda babu abunda ke ciki sai baqin ciki, wannan ma kadai ya isheni, na barshi da Allah kawai”
Nunfasawa Duk sukayi Har lokacin kan amra a kasa yake gaba daya ta zama weak, kunyar dagowa ma take ta kalli Abban nasu da su salima,
“Zo aisha” malam labaran ya fada yana kallonta yana hawaye, don yafi jinta sosai aranshi akan sauran yaran, hakan ya tabbatar mashi da yafi kusanci da ita sosai, shuru ta kasa dagowa ta kalleshi saida ammah ta kirata
“Aisha!!! Kije mahaifinki na kiranki”
Dan dagowa tayi idanunta yayi jaa sosai kafin ta sauke kan nata kasa ta mike jiki a mace, tana zuwa gabanshi ta durkusa ta fashe da kuka, saurin kamo hannunta yayi ya rungumeta yana hawaye shima, ya rasa wasu kalamai zaiyi using, tana da wani babban furgice a zuciyarshi, daman soyayyar dan fari dabance a zuciyar uba, sun dade sosai tana hawaye yana hawaye saida sukayi mai isarsu suma su salima suka rungumeshi, gaba Dayan su Ganin abun suke kamar a mafarki, abbansu bai mutu ba yana raye a Doran kasar tsawon shekarun nan ba tare sun sani ba, ashe suna cikin inuwa daya dashi, lallai daddy ya cucesu yayi masu cutarda Allah kadai ne zai saka masu, for the past years ya raba su da iyayen su sannan ya wulaqanta su saboda wani dalili nashi chan da basu sani ba.
Aman daya shigo tun bayan shugowar salim tun bai kaiga karasowa bama bakin kofar kunnenshi suka jiyo mashi Duk bayan nan da suke yi, da farko bai gane wani labaran din suke magana ba saida ammah tayi bayanin yanda suka taimakeshi akan hanyarsu lokacin da sukayi tafiya shida ita, nan take ya gano wani labaran din suke magana, hankalinshi ba karamin Tashi yayi ba don yaci mutuncin malam labaran sosai achan baya, musamman idan yake kai mahai taki chan gona don Akwai lokacin daya zageshi ma ya bishi da kalamai marasa dadi, tunda ya taaya jikinshi ke bari ya kasa takawa ya shugo parlorn kunya ta gama lulubeshi yanxu ya salima zataji idan ta gano irin cin muguncin dayayi ma ubanta don Har wankin mota saida ya saka shi, yana nan tsaye kamar ya Dora hannu aka haka yake ji, bayan wannan bayanin da salima tayi shima ya girgiza shi sosai na wahalar da suka sha, tausayi ya da kaunarta na ninkuwaa zuciyarshi he wish shine ya taimake su ba Amar ba qila da wannan zaisa malam labaran ya yafe mashi akan abunda yayi mashi, dukda yanzu he’s a changed man.
Amra na gefen Abban nasu ya shafa kanta yace “Aisha Allah yayi maki albarka,kin kula da kannenki ki saka su as your top priority, allah yayi maku albarka ku duka”
Gaba daya suka amsa da Ameen..
***Auren katin kasa***
Romantic love story
written by QUEENMARH
Chapter 150
Update
Unedited page.
Murmusawa ammah tayi tana kallonsu tace ‘’kunga wani ikon allah ko? Ashe malam labaran kai surukin mu ne ikon allah, allah ubangiji ya dauwamar damu cikin farin ciki ya kade mana duk wata musiba da bala’I’’
Atare duk suka amsa da ameen gaba dayan su, salim ce ta kalli abban nasu don tana daga zaune a gefenshi tace ‘’abba yanxu baka tuna da lokacin da kake koyamin zane ba ko?’’
‘’zan tuna wata rana insha allah’’ ya amsata yana dariya, salim ma waigowa yayi inda yake yace ‘’abba toh idan kaine abban mu shi wanchan abban daya kone fah? Don akan idanuna naga motar ta fara ci da wuta’’
Girgiza mashi kai labaran yayi ya kasa bashi amsa saida ammah ta kallesu tukunnata tace ‘’yaron kirki, ikon allah Kenan karka sa abbanku ya shiga rudu, idan ya tuna da kanshi zai bada labarin yanda akayi allah ya kubutar dashi, daughter miko mashi jariran ya gansu yasa masu albarka’’
Mikewa salima tayi cikin jin dadi ta dauka baby hamra ta mika mashi, kallonta malam labaran yayi yana mai jin dadi acikin ranshi sosai kafin ya kalli ammah yace ‘’ubangiji allah ya raya mana su ya sanya su zamo mahaddatan alqur’ani ameen’’
Haka salima ta dunga daukansu daya bayan daya tana mika mashi su yana kallonsu yana jin dadi aranshi sosai yana mamakin wannan jikokinshi ne,’’
Amra dai na daga zaune a gefenta har lokacin tana jin abun banbarakwai kamar a film, amar dai yana daga zaune shima yana kallonta ta gefen idanu jefi jefi,
Ammah ne ta dan nunfasa kafin ta soma magana‘’yanxu inason kuje sama zamuyi wata yar Magana da abban naku’’
Mikewa sukayi gaba dayansu, salima ne ta dauki hamra while amra ta dauki hamad, tana shirin daukan hamid amar yayi saurin mikewa ya kalleta yace ‘’kije zan kawoshi saman’’
Bata kalleshi ba ta wuce sama abunta jiki a mace, gaba daya ta zama wata iri lokaci guda, suna hawa sama ta kwantar dasu akan gadon su anan dakin ammah, kafin ta zauna baking ado ta hada uban tagumi, suma su salima tagumin suka doka kowannen su yayi shuru, ‘’adda yanxu wannan abban mu?, kodai mai
kama dashi ne? yace bai tuna damu ba ammah yana ji ajikinsa mu yayanshi ne, kuma duk kusan abunda ya faru ranar da su mami suka rasu shima a lokacin ammah tace ta tsinceshi’’
Salima ta karashe tana kallon amra, waigowa amra tayi ta kalleta tace ‘’salima ni bansan tunanin da zanyi ba kwata kwata, kaina ya toshe, inaji a jikina abban mu ne wannan, ammah abun yana da wuyar amincewa, zuciyata ta amince da hakan saidai jikina yana bani kamar ba hakan bane ba,’’
‘’nima adda wallahi inajin wani iri wallahi agaban idanuna daddy yasa aka kasha abba, naga motar ta kone’’ salim ya fada yana kallonsu
Waigwa sukayi suna kallonshi inda salima ta galla mashi harara tace ‘’kai yaron nan ashe kai munafuki ne? dama chan kana Magana shine ka qunshe bakinka yau kusan shekara daya kenan’’
Kallonta amra tayi muryanta chan kasa tace ‘’karkiga laifinshi salima’’
Girgiza mata kai salima tayi tace‘’toh yanxu ya zamu gane ko shine abban mu ko bashi bane ba?’’
‘’wallahi ban sani ba salima ban sani ba kaina ya kulle,’’ suna cikin tattaunawan su amar ya bude kofar dakin ya shugo hannunshi rike da hamid, yana shugowa salima da salim suka mike tsaye suka bashi waje ya kwantar da hamid, yana kwantar dashi ya kallesu daya bayan daya bayan ya hade hannunshi akan kirjinshi, ‘’kuna tantama ne koshi mahaifikun ne ko bashi bane?’’
Saurin girgiza mashi kai su salima sukayi, amra dai bata dago ba kanta a kasa saidai tana jinsu, ‘’okay daman babanku yana da twin ne? ‘’
‘’ah ah shi kadai ne wajen kakarmu sai baba ali da daddy’’ su salima suka bashi amsa a tare
‘’toh meysa