daya ta juya ta nufi hanyar futa “Nagode yaya Allah ya Raya mana triplet,”
Juyowa yayi ya mata murmushi kamar bashi ba yace “thank you”
Jinjina kai kawai salima tayi ta fito daga dakin ta wuce sama tana mamaki, tana haura wa sama dakin ammah ta wuce, tana shiga ammah tace “Ina babyn kuma?”
“Ya Muhammad yace ban iya rikewa ba shi zai kawo”
Tabe baki ammah tayi kafin ta dan murmusa, bataga laifinshi ba,tsananin farin cikin da yake ciki ne.
Kallon inda amra ke kwance tayi da babies din data kwantar mata daga gefe don ta basu zamzam sunsha saboda ruwan Nono bai zoba tukunna Har suka koma barci abunsu.
Fitowa ammah tayi daga dakin don zuwa kitchen saboda ta Dora mata pepper soup din kayan ciki da kanta da kunun gyada saboda su zatafi buqata ayanxu.
Tana fitowa corridor saiga Aman shima yana hauro wa, “ah ah kaga su second daddy”
Dariya aman yayi ya kalli ammah yace “Wallahi ammah Bakiji yanda nake ji ba, kamar ni akayi ma haihuwar nan,gidan namu yau Har ya Kara haske “
“Son ba dole ba, Ay dole gida ya Kara haske an haifo min mazaje Har biyu”
Kyal kya cewa sukayi da dariya, waigowa sukayi gaba Dayan su don jin kukan baby, amar ne rike da baby number 2 jikinshi har Rawa yake fuskanshi kamar zaiyi kuka, ammah na Ganin haka Tayi sauri karasowa ta amshi babyn don ya karaso saman, “ammah meysa yake kuka? Ko mu koma asibiti”
“Kawoshi kaga, yunwa yake ji ne shiyasa” ammah ta karashe tana jijiga babyn, “Toh ina abincin a bashi”
Wani irin kallo ammah tayi mashi yayi saurin sauke kanshi kasa yana murmushi, “yauwa Aman, prescription din na hannuna ko? Kaje ka amso sauran magungunan daga nan Ka taho da peak din new borns saboda asamu a basu” ammah ta fada tana kallon aman,
Amar ne yayi saurin katseta “Bari naje na sayo madaran”
Girgiza kai kawai ammah tayi Ganin yanda yake rawar jiki, abunda ya dan tsaya mata arai shine tambayar amra da baiyi ba, itama bata ce mashi komai ba don zuba mashi idanu tayi taga yanda zaiyi.
“No kaida Ka dawo jiya, ga gajiya a tattare dakai, Ka bari ya sayo tunda Harda magungunan da bath karba ba a pharmacy din asibitin zai sayo”
Shugowa Aman yayi ya kalleshi kafin ya miqa mashi hannu for the first time yace “congratulations bro, Allah ya Raya mana yasa su zama mahaddatan alqurani”
Cikin sauri Amar ya amshe hannunshi bakinsa yaqi rufuwa yace “thank you so much brother, thank thank you”
Murmushi ammah tayi tana jin dadin ganinsu a haka “Ay dole kayi amshi godiya kuwa don dashi akayi labour, shi ya dunga dawainiyar kai kawo a cikin asibitin”
Wani irin dadi Amar yaji dayasashi cewa “jibi monday ko? you’ll resume as managing director”
Gwalo idanu Aman yayi, cikin mamaki “wow muma hardamu kenan, mun ci albarkacin angels ammah a tayani godiya”
Dariya Duk sukayi gaba Dayan su kafin aman ya sauka kasa.
Kallonta Amar tayi kafin ya maida kallonshi ga babyn da Har yayi barci abunsa, yana son tambayarta abu ammah yana jin kunya, da kyar ya tattara courage dinshi yace “Zan ita ganin ta?”
Kanshi a kasa ya karashe magana, kallonshi ammah tayi kafin ta dan tabe baki tace “no, tana hutawa yanxu saidai anjima”
Ya dauka ko haushinsa taji daya tambaya don haka yace “Ammah please…..”
“Sai yanxu Ka tuna da uwar tasu? Dazu da kake zumudi ba mantawa kayi da ita ba, kaje sai zuwa anjima saikazo ka ganta “
Jiki a mace ya amsata da “tohm” yana kaiwa nan ya juya ya sauka kasa yana waigowa gaba kallon babyn.
Yana wucewa ammah ta dan murmusa kafin ta wuce daki ta ajiye baby no 3 kusa da maman shi shima.
Koda ya koma daki shima kasa yin komi yayi yama manta ko wanka baiyi ba balle brush don pjs dinshi ne a jikinshi, cikin zumudi ya shige bathroom Har yana Yan wake yayi wanka agurguje ya fito yana waqa “I’m a father, father of triplets”
Haka ya dunga waka shi kadai yana juyi, fuskanshi Har lokacin dauke da murmushi, saida ya gama wakarshi kafin ya shirya.
Yana gama shiri ya janyo key dinshi tare da wayarshi ya fuce daga dakin.
Koda ya fito daga sitting room babu kowa anan kasa don haka ya wuce sama direct don bazai iya jiraba soyake ya ganta kawai.
Yana karasowa saman ya tsaya bakin kofar bedroom din, ahankali ya soma bude kofar, yana bude wa ya rufe ahanakli, salima ya gani a zaune ta dauka jaririn a hannu tana jijiga shi saboda ya Tashi, tana ganinshi kuwa tace “ya muha…”
Saurin maqale maganar Tata tayi Ganin yanda ya mata alamu datayi shuru.
Ahankali ya soma takowa ya karaso bakin gado, tunda ya fara takowa gabanshi ke faduwa Har lokacin daya tsaya bakin gadon, kwance take ta juya ma kofa baya don baya Ganin fuskanta, sanye take da doguwar Riga ta Shan iska tana barci, gefenta baby 1 da little princess dinshi daya lakaba mata ne, wani irin murmushi ne ya kufce mashi daya sa kumatunshi lobawa, salima dai kasa dauke idanunta tayi akanshi tana nanata wato ya Muhammad yana murmushi daman aranta.
Ya dade a tsaye yana kallon bayan amra kafin ya dan Rankwafo daidai kunnenta ya soma mata magana yanda babu wanda zaiji don ko salima dake zaune gefen gadon bataji me yake cewa ba.
Yana gamawa ya miqe tsaye ya kalli salima ya soma mata magana ahankali “take care of my little okay?”
Girgiza mashi kai salima tayi kafin ya fuce daga dakin.
Yana futowa ya sauka kasa direct wajen motarshi ya shige ciki, yana kokarin tada motarshi baba mai gadi ya taho yana mashi barka, yanda baba me gadi ke zuzutashi yana ce mashi “Allah ya Raya Yan uku baban yan uku” abun ya mashi dadi sosai don Har wrapper guda ya zaro ta Yan dubu dubu daga cikin darsh board dinshi ya bashi.
Amra bata Tashi ba sai wajen karfe hudu na yamma, tana Tashi ammah jata zuwa bathroom ta gasa ta sosai saboda danyen jikinta, tana gamawa ta futo ta bata wuri don ta samu tayi wanka, tana fitowa kuwa ta tadda already ammah ta ajiye mata kayan da zata saka.
Kallon kayan tayi don akan gado ta ajiye mata su gefe guda kuma jariran ne a kwance an chanza masu kaya da alamu har ammah tayi masu wani wankan, wani irin lausassan murmushi ta sauke don sai yanxu ta samu kuzarin kallonsu
da kyau, agurguje ta shirya ta feshe jikinta da turare mai kamshi na ammah kafin ta koma kan gadon ta zauna, tana zama tayi bismillah ta dauka baby number one ta shafa kanshi, barci yakeyi hankali kwance sai kuma yan matsu mutsu da yakeyi, fatar hannunshi ta shafa tana kallon fuskanshi sai irin ta ubanshi, mamaki takeyi sosai yanxu waennan duka yayanta ne kuma daga cikinta suka futo, idan ta tuna wannan wani irin dadi yake ji mata misaltuwa, gaba daya kamar rayuwar ta ta masu gida biyu don gaba daya ayanxu hankalinta da tunanin ta ya koma ga yayan.
Bata taba tsammanin Allah zai bata yaya har uku ba lokaci guda dukda tasha wahalar labour dinsu don haihuwar su tazo mata da sauqi da wahala at the same time don lokaci guda suka dinga fitowa after 2 mins,
Sumbatar kumatun babyn tayi kafin ta fara karanto mashi addua a kunnenshi, haka ta dunga yi masu daya bayan daga tana yi tan ajiyesu, saida tazo kan jaririyar ne ta kaga mata idanu, wasu irin hawaye ne suka fara zubo mata don tana Ganin jaririyar ta tuni da mahaifiyarta, wato haka iyaye ke jin da zarar sun haihu, farin cikin wannan yanayin Mara misaltuna ne.
Ammah ne ta shigo dakin da sallama hannunta rike da flask sai salima dake biye da ita da katon tray da aka Dora kayan tea akai, suna shugowa saiga maids ma sun shugo da warmers, anan tsakiyan dakin ammah tasa suka ajiye, amra na dagowa ta kallesu su duka tace “sannu da aiki ammah, sannunku duka”
Maid dinne sukayi saurin amsawa tare da congratulating dinta kafin su fuce.
Zama ammah tayi gefenta while salima ta wuce wajen little princesss ta dauketa don bata gajiya da daukanta
“Sannu daughter ya jiki? Hope yanxu bakyajin kasalan ko?”
Sauke kanta kasa tayi tace “Alhamdulillah ammah babu kasalan saidai abunda baza a rasa ba”
“Sannu allah ya biyaki da gidan aljanna”
Salima ne Tayi saurin amsawa “Ameen grandma ammah”
Dariya dukkansu sukayi gaba daya kafin ammah tace “kwarai kuwa fadi ki kara, na zama grandma”
Dariya suka sakeyi Harda amra, nan baby boy ya fara tsala kuka, kallon inda yake ammah tayi tace “oh ni maryama, wannan miji Nawa Akwai kukan yunwa dazun nan fa na baka madara”
“Laa ammah ya akai kike ganesu?” Salima ta tambaya tana jijiga little princess
“Ya za ayi bazan gane su ba, kinga wannan” tayi nuni da wanda yake tsala kukan
“Shine mijina na farko don shine ya fara zuwa duniya haka doctor yace. Kuma inkin lura zakiga ya danfi dan uwansa chubbiness kamar mamanshi”
Dariya sukayi gaba dayansu, amra dai kasa daukan babyn tayi dake tsala kuka wai ita kunya, ammah na Ganin haka ta daukeshi ta fara jijigashi “salima ajiye
princess ki zubama daughter pepper soup dinnan da kunu ta sha, da zafi zafin shi”
“Tohm ammah” salima ta amsa tana ajiye little princess.
Karfe takwas da rabi daidai yayi parking, yana gama parking ya futo daga motar, fuskanshi tarr sai annuri take, kiran securities yayi gaba dayansu, suna zuwa ya bude bayan motarshi,cike motar take maqilda manya manyan ledoji da kwalaye gaba da baya, haka yasa suka dunga jidar kayannnan suna shiga dashi cikin gida suna gamawa ya rufe motar ya shige gidan, ammah dake saukowa daga sama salima na biye da ita da princess a baya suna saukowa suka ga uban tulin kaya a parlor, sallamarshi ce ta katse su, “barka da dare ammah”
Ya fada fuskanshi wa sai kamar mai yallabai Maclean
“Son kaine kayi wannan uban sayyayan?”
Girgiza mata kai kawai yayi kafin ya kalli inda salima take, bai Lura da princess dake bayanta ba saida ammah tace “jeki dauko min flask sun a kitchen”
Tana juyawa ya hango princess “heyy!!! What’s that? Wannan abun bazaiyi suffocating little princess ba?”
Kallonshi ammah tayi aranta tace “oh basa banba kenan”
Kafin ta maida idanunta kan salima da yake nuni da bayanta.
“Wuce ke abunki” ammah ta fada mata kafin ta maido da kanta gareshi
“Banson iyayi fah, wani irin suffocating, you muhammd tun daga yanxu har Ka fara suaucewa akan yaya? Toh Wallahi idanuna idonka Ka kiyayeni “
Sauke kanshi yayi kasa baice komai ba, “meke sayo ne haka kuka cika mana parlor”
Cikin zumudi ya kalli ammah yace “kaya ne for my littles”
“Ahh Masha Allah Toh Allah ya kara budi, Ay daka fada min zakayi sayyaya dana ce Ka bari saboda mun saya komai saidai kawai basusan triplet zata haifa bane”
Zama sukayi anan parlor ammah ta soma duduba kayan daya sayo, ganin kayan suna da yawa don shima kanshi baisan aradun abubuwan da ya sayo ba yasa yace ma ammah “let me fresh up ammah”
“Okay son” ta amsa shi
Yana shige wa dakin Aman ya dawo shima da nashi ledojin.
Karfe Tara da rabi ya fito daga bedroom, yayi wanka ya sauya kaya, fuskanshi Har lokacin dauke da murmushi gaba daya gajiyar daya kwaso ta operation tabi jiki don haka manta da wani operation.
Lokacin daya futo babu kowa a kasa don haka ya wuce sama direct, part din ammah ya shige da sallama, yana shiga sitting room dinta ya tadda salima
kwance akan couch tana waya baima bi ta kanta ba ya wuce cikin bedroom din anatse.
Ahanakli ya soma bude kofar dakin bakinsa dauke da sallama cikin kamewa, ammah ne kawai a zaune bakin gado tana petting angel don yan uwanta sunyi barci, duban dakin ya soma yi ganin amra bata nan yasa ya karaso cikin dakin ya zauna gefen gadon inda ammah ke zaune.
“Barka da dare ammah”
“Barka dai son,”
Kallon boys dinshi ya fara yi da suke ta barci abunsu acikin wani haddaden baby net sunsha kayan gayu, kallonsu kawai da yayi kara sanya ya mashi zuciya yayi.
Kallon inda yake kallo ammah tayi kafin ta maida kallonta gareshi, “oh Anya Muhammad zaka barmu mu sarara kuwa”
Sauke kanshi yayi kasa yana dan murmusa baice komai ba kafin ya maida idanunshi kan kofar bathroom jin alamun Ana shirin fitowa daga ciki.
Ahankali ta bude kofar bathroom din ta shugo kanta a kasa tana dan dingisawa, sanye take da wasu kayan daban ba na dazun ba saboda sukayi wankan dare inda ammah ta taimaka mata, batama kura dashi ba kwata kwata daya kafeta da idanu sai muryar ammah dataji
“Toh Ka Tashi Ka bata waje ta zauna ko?” Ammah ta fada tana kallon Amar dake zaune bakin gado ya kafe amra da idanu ko kiftawa bayayi, he missed her a lot, her stubbornness da komai ma, don lokacin da ya tafi operation nan ya tabbatar da feelings dinshi akanta, sai gashi kuka abunda ya dawo ya tarar na haifa mashi triplet da tayi, mukamin data samu a cikin zuciyarshi babba ne sosai wanda baya jin zai iya kallon mace bayan ita,yana jin kamar Duk futar nunfashinsa da sunan amra yake fita, ayanxu ya gama deciding bazai sake danne what he has for her ba, to hell with the ego, haka yake fada ma kanshi kullum don idan yace baya son ta yayi karya.
Saurin dagowa tayi nan idanunta ya sauka cikin nashi, kwata kwata bata san ya dawo ba sai yanxu da take Ganin shi bazata, saurin kauda kanta tayi gefe fuskanta a hade harya karaso, tana karasowa ya mike tsaye ya bata waje, koda ya matsa saida ta dan dago ta kalleshi kafin ta kauda kanta, mamaki ne ya gama cikata, Anya wannan general data sani ne, wanda ta sani murmushi ma wuya yake balle dariya,
Tana zama ammah ta mike don yanda ya kafe amra da idanu tasan idan har ba waje ta bashi ba zai iya yin rashin kunya ma agabanta wanda batada kuzarin Ganin hakan, don yanda yake kallon amra kamar zai cinyeta anan tsaye.
Mikewa ammah tayi ta ajiye mata princess a kan cinyanta ta fuce daga dakin don ta basu waje.
Ammah na futa kamar jira yake ya karaso kusa da ita ya dan rankwafo daidai fuskanta idanunshi na kan princess, Ganin tana barci yasa yayi pecking kumatun ta yana murmushi, amra dai mutuwar zaune tayi don gaba daya ya gama cikata da mamaki, bata gama tunani ba saida taji ya dauke princess ya kwantar da ita gefen gado kusa da Yan uwanta, yana kwantar da ita ya dawo inda amra ke zaune gaba daya mamaki ya gama cikata don Har sakin bakinta tayi batama san tayi ba,
Sanyin lausassan hannunshi dataji akan fatar hannunta ne yasa ta dago da idanunta ta sauke akanshi, baiyi wata wata ba ya matso ya rungumeta a jikinshi ya saqalo da kanshi tsakanin wuyanta, sun dauka kusan minti biyar a haka, itakam tunda ya rungumeta ta kasa motsawa, abunda yafi bata mamaki shine yanda taji saukan wani abu kamar ruwa akan wuyanta, bata san mene ne saidai tana jin saukan abun akan skin dinta,
Ahanakli ya soma magana cikin wata irin murya kamar ba Tashi ba “Aisha, aisha Allah yayi maki albarka, Allah ya faranta maki yanda kika faranta min, Allah yayi maki albarka, bansan da wani irin words zanyi using ba wajen gode maki, kin gama yimin komai a duniya, thank you so so much,”
Yana kaiwa nan ya saketa ya dago da fiskanta, abunda ya daure nata kai shine Ganin ruwa ruwa kamar hawaye akan fuskanshi, kwata kwata bata kawo hawaye bane don tasan that’s impossible don haka ta kauda kanta ta hade rai don daman tasan hakan zai kasance, Duk wannan abunda yakeyi akan yayanshi ne, ba akanta ba saboda ta haifa mashi yaya,
“Now tell me , me kike so a duniyar nan fada min Duk abunda kike so zanyi maki shi”
Babu tsoro ko fargaba ta dago ta kalleshi “ka sake ni,”
Da mamaki yake kallonta son bai gane me yake nufi ba din haka ya saki shoulder dinta daya rike, ganin kamar bai gane abunda yake nufi ba yasa ta sake cewa “I mean divorce me, ban son aurenka akaina”
Saurin mikewa yayi tsaye idanunshi sun danyi jaa ya kalleta “what do you mean?”
“I mean Ka bani takardata, bana so…”
“Shut the fuck up..” ya daka mata tsawa
“Karki sake wannan maganar, babu saki a tsakaninmu never, musamman yanxu da zuria ta shiga tsakanin mu”
Rai abace amra ta dago ta kalleshi “wow, finally Ka nuna komai basai nayi tunani ba, saboda yayanka ko”
Da sauri ya koma ya zauna kusa da ita “no aisha Karkiyi wannan tunanin please, I want you by my side ba yaranmu kadai ba, I want us to clear the air between us komai ya wuce”
Fashe wa amra tayi da kuka tana jin wani takaicin zancenshi
“Just like that? So it’s easy for you to say that Komai ya wuce? Ka manta abubuwan da Ka dunga yimin? Ay Wallahi babu abunda zaka fada min da Zan yarda yanxu, ni kaje kaina yana ciwo”
“Aisha please!!!” Ya fada yana kallonta fuskanshi harta sauya
Da sauri ta dago ta kalleshi har wani sauke murya yake.
Tabe baki kawai tayi bata sake kallon Ind a yake ba, ammah ce ta shugo dakin don taji ihun nasu daga parlor,
Yana ganin ammah kuwa ya mike ya wuce wajen yayanshi yayi kissing dinsu daya bayan daya kafin ya dawo gaban amra, babu zato babu tsammani taji lebenshi a kumatunta agaban ammah, wani irin haushi da takaicin shi ne ya turniketa, ga kunyan ammah data turniketa.
Ammah Dia kauda kanta tayi gefe tace “saida safe ko”
Juyawa yayi ya fuce “saida safe”
Washe gari da asuba ma haka ya shigo dakin kafin ya wuce