ta fada tana murmusawa kafin ta cigaba
‘’’’aisha ina son ki daukeni a matsayin uwa kamar yanda su salima suka daukeni, inason ki cire kunya ki saki jikinki anan gidan kinji ko?,’’
‘’insha allah’’ amra ta fada tana sunkuyar da kanta fuskanta dauke da dan murmushi
‘’masha allah, yanxu inason naji ta bakinki, ki fada gaskia karki boye min komai, wani irin zama kukayi keda Muhammad achan dubai’’
Gaban amra ne ya fadi dammm,samun kanta tayi da kasa cewa komai har saida ammah tace ‘’karkiji tsoro kinji ki fada min komai, shin zamanku da Muhammad bayan yarjejeniya da kukayi babu komai tsakanin ku?’’
‘girgiza kai kawai amra tayi ta kasa cewa komai saida ammah ta sake cewa ‘’yace kin buqaci ya sakeki?,har yanxu kina son ya sakeki ne?koda kuwa shi baya son yin haka?’’
Kasa motsi amra tayi balle ta dago ta bata amsa sai , ammah na ganin haka ta gane tana da matsanancin kunya don haka kai tsaye ba tare da wani kwana kwana ba tace ‘’kina sonshi?’’
Shuru amra tayi hawaye na gangarowa akan fuskanta, koda ace bai dauki kannenta bay a kula dasu ba bazata taba iya kallon mahaifiyarshi tace mata bata son zama dashi ba,
Ammah na ganin haka ta sauke ajiyar zuciya tace ‘’bazanyi forcing dinky ki fada min ba aisha, but kiyi tuanni akai kinji, zan dawo anjima zamu sake maganar nan, ‘’
Tana kaiwa nan ta fuce daga dakin…
Daki ammah ta wuce tayi mata order kayan sawa ready made, dukda bata san size dint aba haka ta bayar ayi mata kafin ta zuwa dan wani lokacin idan komai ya lafa sai suje a dauka size dinta, tana gama waya da designer dinta wato zetatelia fashion house, wayar amar ta soma kira, don tana sane dashi kwana biyu yanda yake doging dinta,ringing daya biyu ya daga wayar yana dagawa tace ‘’kana ina?’’
Magana yayi daga chan bangaren kafin tace ‘’ina son ka dawo da wuri inada Magana dakai’’ tana kaiwa nan ta akshe wayar,mikewa tayi ta shiga dakin closet dinta, abubuwan amfani daga kan sprays, mayukan shafawa masu tsada turarruka, haka ta kwaso ta wuce dakin amra dasu, akwance ta taddata don haka tana shiga tace daughter ga wannan ki fara amfani dashi kafin zuwa nextweek saimuje shopping ko’’
Sunkuyarvdakai amra tayi ta mata godiya kafin ta fuce.
Kallon abubuwan amra tayi, wani irin dadi taji aranta son dama taba buqatar su sosai.
Karfe shida takwas daidai ya shigo cikin gidan saida ya fara tsayawa a masallaci yayi sllah kafin ya wuce cikin gida, direc t dakinshi ya wuce bai tsaya komai
bay a watsa ruwa ya sauya kaya kafin ya fuce daga dakin, hawa stair ya fara yi ya tunkari part din ammah, bai kaiga karasawa ya jiyo muryar amra
‘’salima don allah ki kulani, wannan silent treatment din da kike bani is killing me, wallahi azeem bazan taba abandoning dinku ba kiyi hakuri ki yafe min’’
Kallonta salima tayi don daman tazo kiran salim ne don suje suci dinner shine amra ta tare ta da tambayr meysa salim baya Magana, tambayar ta bata mata rai sosai, don idanda tana tare dasu ay zata san dalilin rashin maganar nashi, abunda yafi bata mata rai Kenan, don haka cikin kuka ta soma Magana harshly ‘’wallahi adda bazan taba yarda da maganr ki ba, shekara hudu fah?tunda kika tafi baki waigo mu ba sai yanxu, lokacin da muke buqatarki ay baki zoba sai lokacin da bama buqatarki,yanxu dan allah bakiji kunyar tambayar dalilin rashin Magana da salim keyi ba?are you not feeling ashamed?, tunda tun farko baki damu da sanin halin da muka shiga ba maysa yanxu zaki damu, kibarmu yanda kika ganmu’’ ta karaseh tana kuka wiwi, itama amra kukan takeyi tana jin zafi da kunan rai, amar dai daga nesa yake hangosu don suna bakin kofa, tsaki kawai yayi ya shige dakin ammah, yana shiga ya taddata tana sallah kan sallaya, karassawa yayi cikin dakin ya zauna kan ottoman harta idar ta shafa, kallon inda yake tayi kafin ta miqe tsaye ta karaso inda yake ta zauna bakin gado, cikin nastuwa yace ‘’barka da dare ammah’’
kallonshi tayi a kamilance tace ‘’kaga dam aka dawo gida da wuri yau?, ko ince k agama kauce kaucen naka?’’
shuru yayi ya kasa dagowa,
‘’muhammad’’ ammah ta kirashi
Dan dagowa yayi ya kalleta yace ‘’naam’’
‘’da wayonka da hankalinka basaina fada maka maanar hakki ba, na lura da kana son ka nuna min kai ka girma ko?,’’
Ta fada tana kallonshi, saurin dagowa yayi yace ‘’ammah ba haka bane…’’
Kallonshi ta sakeyi tace ‘’so? Gardama zakayi min Kenan?’’
Sunkuyar da kanshi yayi kasa ya kasa cewa komai, saida tace ‘’maysa kake son sakin ta?’’
Kamar jira ko yake tayi tambayar yace ‘’ammah babu amfanin auren, aside from that wannan auren wallahi ban daukeshi a matsayin komai ba, yarjejeniya ne kuma its over, wallahi ammah bana buqatar mace a rayuwana, I have a lot on my he…’’
Kasa karasawa yayi ganin yanda fushi ya bayyana a fuskanta karara azafafe tace ‘’ta gama maka amfani Kenan muhammad wato bari ka sake ta baka buqatar mace arayuwarka, to bari kaji, wallahi wallahi ka roki allah kada yarinyar nan tace itama batason auren don wallahi youll regret it, kai ina tunaninka, im not trying to be selfish over here don zan tambayeta dakaina idan har tace batason auren zan barku kuyi abunda kukeso but inason ka sani, a zamanin nan babu macen da zata zauna da namijin da baya haihuwa duk kyawunka da arzikinka da mukamun ka da kake takama dashi , maysa bazakayi wannan tunanin ba?’’
Hade rai yayi ranshi adan bace aranshi yana jin zafin abunda ammah tace wai babu macen da zata iya zama dashi Kenan saboda baya haihuwa duk ajin shi da arxikinshi, shi abunda yafi bata mashi rai shine yanda ammah ke mashi fada akan wannan yarinyar’
Dan dagowa yayi idanunshi yayi jaa ya kalli amma muryarshi a kasa yace ‘’ammah please….you have to understand, nine bana buqata, I don’t mind nayi rayuwana a haka, bayan wannan ma ita da kanta ma ta buqaci sakin koda kuwa bata buqata ba ma zan bata dakaina saboda batada wani amfani a wajena, shes not my type, yarinya ce karama ammah, shes just 22,’’
Rai abace ammah ta miqe don kwata kwata kamar ma bai gane maganganun da yakeyi ne suke hasala ta ba ‘’muhammd idan kai ka haifeni zan sani idan kuma nice na tsugunna na haifeka to dole kayi abunda nace, now get out my room,’’
‘’ammah please I don’t mean to upset you, don allah karkiyi fushi’’
Ya fada anatse
‘’muhammd get up, karna kara ganin fuskanka’’ ta fada idanunta a rufe don ranta ya baci, daman ance mai hakuri bai iya fushi ba
Yana ganin haka gabanshi ya fadi hankali atashe ya rike hannunta ya zaunar da ita cikin sanyin murya yace ‘’ammah na, please calm down, don allah kiyi hakuri wallahi zanyi duk abunda kike so dan allah kar kiyi fushi dani please, me kikeso ayi yanxu?bakya son na saketa right? Shikenan zanyi abunda kike so’’
Bata kalleshi ba tace ‘’zan kwanta’’
Yana jin haka ya miqe jiki a mace yayi mat sallama ya fito rai abace, azafafe ya wuce dakin amra yana zuwa ya bude kofar a zafafe, a durkushe ya taddata ta rike ciki tana kuka, rai abace ya karaso dakin ya kalleta yace ‘’keeeee!!!’’
Yanda ya fada saida dakin ya amsa, da sauri ta miqe tana muzurai gabanta na faduwa,kallon fuskanshi tayi ganin yanda ya karade yayi jaaa kamar bashi ba yasa gabanta faduwa,bata ankare ba ta ganshi gadan gadan yayo kanta, kan kace me nan take ta sulale a sume, dan tsaywa yayi yana kallon ikon allah, yama rasa abunda zaiyi yana huci kamar zaki, juyawa yayi ya doka tsaki yabar dakin, kasa ya wuce zuwa dakinshi wuce ya zame kayan jikinshi ya shige bathroom, cold shiwer ya sakarma kanshi don hot temper dinshi yah au sosai, ya dade sosai saida yaji zuciyarshi ta lafa kafin ya fito anatse kugunshi daure da towel, closet dinshi ya shiga ya zaro kayan barci kafin ya shirya, gadon shi ya hau yayi rub da ciki, ya dauka kusan minti talatin ahaka hanakli ya soma jin yunwa don haka ya miqe ya zura bedroom slippers dinshi ya fuce daga dakin, fitowa yayi daga dakin cikin kamewa yawuce dining, nan ya tadda salima zaune da plate din indomie agabanta, kallonta yayi tana ganinshi itama tayi saurin miqewa tace ‘’ina wuni ya muhammad’’
Ataqaice ya amsa ta ‘’lafiya’’ kafin ya janyo kujera ya zauna, kallon wall clorck din dake gaban dining din yayi ganin kusan goma da rabi yasa yace ‘’why are you eating late’’
Sunkuyar da kanta tayi tace ‘’dazun ne kaina ke ciwo saina kwanta’’
Shuru ya danyi yana wani nazari kafin yace ‘’bring me coffee’’
Da sauri ta miqe ta hado mashi coffee cikin coffee maker tana gamawa ta kawo mashi tace ‘’bismillah ya muhammd’’
Karba yayi yace ‘’thanks’’
Tana ganin haka ta dauke plate din indomie ta wuce kitchen dashi ta karasa tana gamawa ta fito hannunta rike da bottle water,’’good night ya muhammad’’
Dagowa yayi ya kalleta azafafe yac e’’zo nan’’
Anatse ta juyo gabanta na faduwa ta karaso wajen dining din tace ‘’gani’’
Yana sipping coffee din ba tare da ya kalleta bay ace ‘’why where you talking to your elder sister harshly? Ita sa’arki ce?’’
Shuru salima tayi hawaye na zubo mata ta kasa cewa komi saida yace ‘’clean those tears and answer me, ita sa’arki ce?’’
‘’ah ah’’ salima ta fada ahankali tana goge hawayen
‘’who told you tayi abandoning dinku?you better get your head staright, you don’t owe her explation saboda I recall na fada maku cewa saboda ita nasan ku, I don’t have to repeat my self duk halin da kuka shiga ita kinsan wani hali ta shiga ne? kince kunsha wahala tayi abandoning dunku lokacin da kuke buqatarta right? Ita kinsan halin da ta shiga saboda ku day and night? kinsan abunda ta jefa kanta saboda ku?’’ ya karashe a fadace yana kallonta har saida tadan furgita
‘’im sorry ya muhammd’’ salima ta fada tana shesheka, ‘’bani zaki bama hakuri ba, you should be ashamed of your self for being selfish, and this should be the last time da zaki sake mata Magana babu respect understood’’
Da sauri salima ta daga kai jiki na bari tace ‘’insha allah yaya’’
‘’go and sleep’’ ya fada yana aje empty cup din, da sauri kuwa ta juya ta wuce sama.
Tana tafiya shima ya miqe ya wuce dakinshi hankali kwance….
The next morning….
Sai wajen karfe biyar amra ta farfado, bakinta dauke da salati t miqe, duk jikinta ya gam tsami, saida ta zauna ta tuna da abunda ya faru, kamar a mafarki, mikewa tayi ta wuce bathroom tayi wanka ta dauo alwala, tana fitowa ta dora bayarta data zo da ita gida ta saka hija ta tada sallah tana idarwa tayi azkar, sai wajen karfe shida ta miqe ta koma kan gado ta kwanta, bacci ne ya dauketa sai wajen karfe tara ta tashi, tana tashi ta wuce bathroom ta wanko bakinta ta fito, gaban dresser ta tsaya tana karema kanta kallo, ta dan rame, duban kanta tayi dake buqatan gyara sosai don har tsinkewa ykeyi, nannadeshi tayi daga daurewar datayi da ribbom,ahankali ta tura annunta cikin gashi kafin ta fiddashi, hankalinta ne yadan tashi ganin gashi ya biyo hannunta,saurin annnade gashin tayi jin anyi knocking, salima ce ta shigo kanta a kasa tace ‘’good morning adda’’
Da mamki amra ta jyo ta kalleta, murmushi tayi ta tako har inda salima take tace ‘’salima, good morning kin tashi lafiya’’ yanda take Magana kamar itace
kanwar salimar, ba tare da ta kalleta ba salima tace ‘’ammah tace ki sauko muyi breakfast’’ tana kaiwa nan ta juya ta fuce daga dakin.
Jikin amra ne yayi sanyi sosai, haka ta jawo veil din abayr tata ta maidashi kanta tayi rolling kafin ta sauko kasan, direct wajen dining ta nufa tana zuwa daidai hanyar gabamta ya soma faduwa, runtse idanu tayi ta karaso cikin dining din tace ‘’sallam alaikum’’ gaba daya juyowa sukayi suka kallet hara mar dake zaune kafin ya hade rai wanda hakan akan idanunta yayi,saurin sunkuyar da kanta tayi ta karaso wajen dining din, ammah na ganinta tace ‘’zoki zauna nan kusa dani daughter’’
Gaban wajen da ammah ke nuna mata ta karaso don dayan side din da mar ke zaune ne sai ya zamana sun sakashi a tsakiya, anatse amra ta zauna kanta kasa tace ‘’ina kwana ammah’’ da sauri ammah tace ‘’lpy lau dota how was your night’’
‘’alhamdulillah amra ta amsa
Murmushi ammah tayi ta kalli salima tace ‘’yan mata na a fara serving dinmu tunda kowa ya zauna’’
Mikewa salima tayi ta fara serving sai alokacin amra ta lura da wanda kekusa da ita, daga chan gefe, ahanakli ta kalli aman tace ‘’ina kwana’’ murmushi yayi mata yace ‘’lafiya kalua sister inlaw’’
Da sauri salima t dago ta kalleshi ta galla mashi harara don duk a tunaninta yaa referring to her ne amatsayin yayar budurwarshi nan ko bata san shi ya fadi hakan ne saboda matsayin amra na matar amar, kallon gefen amar tayi daya hade rai yayi kamar ba a yi ruwanta a wajen ba, kanta a kasa tace ‘’ina kwana’’
Banza yayi da ita kamar baisan dashi take ba wanda hakan akan idanun ammah, ‘’muhammd bakaji ana gaisheka bane?’’ ammah ta fada
Dan waigowa yayi ya mata wani irin mugun kallo ataqaice yace ‘’lafiya’’
Kauda kai amma tayi ta basar, ba tare da tace komi ba.
Lantana ce ta karso dining din ta ajema ammah green juice dinta kafin ta koma kitchen.
Anaste suka fara cin abunci har kowa ya gama amra dai kasa ci tayi sai juya cokali takeyi, ammah na ganin haka tace ‘’daughter ko kina buqatan wani abun ne?’’
Saurin girgiza kai amra tayi tace ‘’ah ah wannan ma yayi’’
Murmushi kawai ammah tayi ta cigaba da cin abuncinta, amar ne ya fara miqewa yace ‘’ammah zan fita’’
‘’ókay adawo lafiya’’ ta bashi amsa yana fucewa aman ma ya wuce office,suna gamawa salima ta mike ta fara kwashewa, amra na ganin haka itama ta mike suka kai plates din kitchen atare, murmushi kawai ammah keyi tana kallonsu su biyu.
Karfe biyu aka kawo kayan da ammah tayima amra order na ready made, da kanta ta shiga dakin don kai mata, tana shiga dakin lokacin amra na toilet, saida ta jira har ta fito.
Da sauri amra ta karaso inda ammah take zaune kanta kasa tace ‘’barka da rana ammah’’
Murmushi ammah tayi tace ‘’thank you dear, ga kayanan kafin mu samu time mu shiga kasuwa,allah yasa suyi maki daidai,’’
Kallon inda ammah ke nuna mata tayi kafin tace ‘’allah ya saka da alkairi ya kara budi’’
‘’ameen ya allah’’ ammah ta fada tana kallonta kafin tce ‘’zoki zauna nan daughter muyi magana’’
Anatse amra ta tako har inda ammah ke zaune dan nesa da ita bakin gadon ta zauna kanta a kasa, nunfasawa ammah tayi tace’’ daughter fatan kinyi tunani akan abunda na fada maki,’’ anaste amra tace ‘’eh’’
Kallonta amma tayi kafin tadan nunfasa tace ‘’kafin naji daga bakinki ina son nayi wata mahimmiyar Magana dake saboda bana tauyema kowa hakki, muhammd ya fada min auren yarjejeniya da kukayi inda kika buqaci citizenship wato katin kasa ta karkashinsa don ki kawo qannenki kusa dake yanxu dai inason naji daga bakinki shin kinsan dalilin da yasa shi Muhammad ya aureki’’
Shuru amra tayi don bata kwata kwata all this while tunani daya ke zuwan mata akan dalilin aurenta da yayi which is saboda jikinta ya aureta,batayi yunkurin tambayrshi ba ko jin ta bangarenshi dalilin aurenta da yayi, itadai tayi concluding saboda yana shaawar jikinta ne shiyasa ya aureta har ya kaita asibiti aka gwadata don ya tabbatar da bata da ciki don ya saketa, runtse idanunta tayi ta nunfasa tace ‘’ah ah ban sani ba’’
Shuru ammah tayi don tayi tunanin hakan, saida ta danyi wani nazari kafin tace ‘’kinsan oligospermia?’’ Ammah ta tambayeta tana kallonta,
Dagowa amra tayi tadan aklleta kafin ta sauke kanta kasa tace ‘’eh na sani’’
‘’masha allah, Muhammad yana da oligospermia 3rd stage ya aureki ne saboda he has last chance of producing a child’’
Dan nunfasawa ammah tayi muryanta na breaking ta cigaba,’’wannan ne dalili da yasa ya aureki saboda daga wannan last chance din idan bai samu haihuwa ba bazai taba haihuwa ba’’
Da sauri amra ta dago idanunta fal da hawaye, innalillahi ta wa inna ilaihi rajiun ta fara maimaitawa aranta, maganar ammah ce ta katseta ‘’wannan ne dalilin dayasa nace kafin naji daga bangaren inason muyi Magana, duk abunda kika yanke daughter shi za ayi, don anytime muhammd zai iya sakin ki indai kina so,idan kuma bakya ra ayin hakan, ni an tsaya mashi’’
Anatse ammah ta share hawayen fuskanta daya zubo mata tace ‘’my dear babu macen da zata zauna da namijin da baya haihuwa shiyasa bazanyi forcing dinky akan ki zauna dashi ba, idan har bkyaso zai sakeki kinji ko?’’
Kallonta amra tayi hawaye na zarya a fuskanta, tama kasa cewa komai, tausayin ammah y agama dabaibaiye ta sosai, idanunta sunyi jaa sosai wato all this while
tayi mashin muguwar fassara, bait aba shaawar jikinta ba ko sau daya, hasalima ya aureta ne saboda that was his lat chance of haihuwa, hawaye ne ya soma yi mata zarya a fuska, sai yanxu take regretting magan ganun data dunga fadamashi, da yanda take cewa ta gode ma allah daya bata dauki cikinshi ba, yanda take jinshi aranta yanxu ya wuce musali, ya samu wani babban gurbi a zuciyarta, dashi da mahaifiyars.
Ammah na ganin haka ta miqe tace ‘’daughter zan barki kiyi shawara kinji ko’’
Tana kaiwa nan ta fuce tana goge hawayen da take boye, salima dake labe bakin kofar su tayi saurin komawa da baya ta boye gefen flower vase, tana ganin ammah ta wuce daki ta fito, idanunta itama ya cika da