Sarki Sameer 2 Wasa Farin Girki By Yaya Azeema

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   57 / 74

168K to 171K   out of 221K words

gaye ba gayen arziƙi bane yafi ƙarfin ajinki da tunanin ki,

cike da zafin rai da masifa Rasheeda kamar ta rufe ta da duka tace ta daka mata tsawa da cewa momy ya isa haka nace ya isheki haka afaɗin garin nan ke harkina da bakin cewa wani yafi ƙarfin ajina ki kalle ni da kyau meye bani da shi da akesonshi ajikin mace wanda bani dashi idan kuɗi kike magana kekinsan ko ni wacece basai angaya miki ba dan haka wallahi naƙara jin kinfaɗi kalmar da bata dace ba sai nayi ƙasa ƙasa dake agunnan nidaman nasan baƙin ciki ne da hassada ne suka hanaki magana tunɗazu sai yanzu da kika kasa riƙewa hassadar tafi ƙarfinki kinkasa jurewa sai yanzu zaki bayyana ta daman ana gayamin kina min zagon ƙasa bana yarda sai yau da kika nuna min halinki a fili nagane hakan to zansan zaman da zanyi dake daga yau,

murmushin ta ƙaice momy tasaki sannan tace kinsan ai da halina ne hassada da tuni kin sani waɗanda suke zuwa suce miki ina miki zagon ƙasa saidai idan su suke miki amma bani ba ni bana mufurci bana yin zancen wani abayan idon sa kana min ba daidai ba zan gaya maka kayi min ba daidai ba danni banga abunda wani ya isa yamin ba wanda Allah baiyi min ba shiyasa banajin tsoron mutum da zan kasa cewa wani abu gaban sa ba indai kinga nayi zancen wani abayan idon to na tabbatar zan iya yi agaban sa koma na riga nafara gaya masa kafin inje wani wajen inyi dan haka ki adana kalamanki ba akain yakama kiyi suba kije kiyi a inda ake munafurtar taki amma ba waje naba, ɗan dakatawa tayi sannan ta juga ta kalli sauran ƙawayen tace Inma acikin kune wasu suke faɗa mata haka to kuci gaba kunriga da kunsan halina wallahi duk wacce nakama tana min munafurcin abun da banyi ba to ta kuka dakanta dan ba wacce zan ɗagawa ƙafa kunfi kowa sanin halina kunsan kuma ko ni wacece dan haka muzuba mugani wata ta buɗi baki zatai magana Rasheeda tayi saurin dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannun,

wacce suka kira da momy Rasheeda ta shiga bi da kallon banza tunda ga sama har ƙasa sannan tace kingama borin kunyar taki daman ance tabar mar  kunya da hauka ake naɗai ta saboda ankama ki ƙiriƙiri kina min hassada da baƙin ciki shine kike wannan zubar to kodan saboda ke nikuma zan nunamiki iyakata zannun miki ajina yawuce nasa saina kawo miki shi har gabanki sai yazama atafin hannu na sai najuyasa yanda nakeso sai nasa ya mutu akan sona idan kin isa ke kuma ki dakatar,

wata mahaukaciyar dariya momy ta saki da har saida ta ɗan basu tsoro suka fara tunanin me yame damun ta kodai ba ita kaɗai bace,

saida tayi mai isarta sannan tashiga nuna Rasheeda da hannu wata dariyar na ƙara cinta da ƙyar ta daure tace wai kijuya sa lalle wannan mutumin ne zakisa ya mutu akan sonki ko to Allah yabawa me rabo sa'a da nayi niyar sanar dake ko shiɗin waye amma tunda ta haka kika biyo zan barki kije jiki magayi domin wance mutumin ba irin mutanen da kika sani bane idan nace miki nasanshi bazaki yarda ba amma idan kun haɗu dashi kyafi yarda dani sannan kuma nima zan ƙara miki ƙarin bayani akansa duk iskan cina da jiji da kaina da surutu na kika ga nayi shiru ai kinsan ba ƙalau ba saboda tunda muke daku nasan baku taɓa ganin hakan daga gare ni ba kamata yayi ku tambayeni dalili amma kuma alaƙanta hakan da hassada nake to naji muje ahakan bazan ƙara ƙoƙarin dakatar daku ba sai kundawo danni nan ko ta hanyar da yafita bazan fita tanan ba zanbi ta hanyar baya intafi insamawa kaina lafiya da kwanciyar hankali dan wallahi duk wannan maganar ma danake muku dauriya ce kawai amma ba adaidai nake ba idan naje gida nasamu nutsuwa zan kiraku adawo lafiya Mrs MEER in antashi biki zan tayaki murna koda ta wayane amma bazan zoba saboda ina kishi dake ga hassada da baƙin ciki da sukayi min yawa kamar yanda kikace kuje Allah bawa mai rabo sa'a Allah ya haɗaku kuma idan ya haɗaku kar yarabaku sannan kuma karma wani yarabaku Allah yabarku tare dan wallahi wannan gayen da kike gani babu abun da baidashi domin irinsu aduniya basu da yawa basufi su ukuba shiɗin na musamman ne gashi kema ta musamman ba ƙaramin dacewa kukayi bafa badan badan ba dana tsaya naga yanda zaku bada kala idan kun haɗu nasan ba ƙaramin matching zakuyi ba hmmm kar na cikaki da surutu bari inbarki haka ni kinga tafiya ta daga nan kuma sai gidan mu taba kaiwa nan bata jira cewar su ba ta juya tabar wajen da suri daya daga cikin su tayi saurin tarar gabanta tace momy dan Allah ki gaya mana abun dake faruwa mana ya kike mana magana me harshen damo nidai daman bance kina hassada ba amma kada kibari kawarmu ta cutu idan kinsan mutumin nan da wani mugun hali ki sanar da ita kawai,

waima dan Allah intambayeki a ina kikasan wannan mutumin nidai tunada nake dake bantaba ganin saba kuma bantaba jin kin bamu labarin saba yakamata ki sanat damu inda kika sansa nasanki da shige shige watakil awajen shige shihgen naki kika gano sa yayiwa wani rashin mutunci shiyasa kema kika tsorata dashi dan na fuskanci kamar kina tsoron sa,

Rasheedace ta daka mata tsawa tace ke bibi ki rabu da ita akan me zaki dakatar da ita ki barta ta tafi taje duk inda zata kuma bana bukatar sanin komai daga gare ta indai akan wannan guy din ne tagama haukan ta ta tafi nikuma zan bata mamaki sai na nuna mata ko wacece ni,

dan murmushi momy tayi sannan ta kalli yarinyar da ta dakatar da ita sannan ta make kafada tare da tabe baki sannan tace to kinji me tace ko dan haka wannan ba matsalara bace sai kuntaho idan kuma da wacce take son ranta da lafiyarta tazo mutafi ta mutu adakin uwarta maza sukaita to ta rufawa kanta asiri tazo mutafi idan kuma kun zabi zama da ita sai kuzauna jiki magayi tana fada ta juya taci gaba da tafiya har tayi nisa bibi ta kwala mata kira tare da cewa momy jirani mutafi tare dan wallahi bani tsayawa nima jiran ta tayi tana karasawa kuwa gurin ta sukayi tafiyar su susu biyu,

Rasheeda in ranta yayi dubu tofa gaba dayan su sun baci yau wadannan yaren sun nuna mata halinsu aikwa yanda suka tafi ko gidan su ta koma ta gansu sai taci musu mutuncin da basu taba tunani ba dan tasan basu da inda zasu kwana saboda basu da kunya yanzu gidan su zasu koma suce zasu kwana  har ita zasuyi wa haka,

sauran yan matan ne suka shiga bata hakuri suna zizzigata akan ta rabu dasu wallahi kar ta daga musu kafa,
tunda har suka juya mata baya alokacin da take bukatar taimakon ko wannen su amma zasuyi mata haka musammanma momy da tagama yaba mata magana son ranta kamar Rasheedan ba gaba take da ita ba dan agirme Rasheeda ta girmi wajen mutum uku acikin su,

nan dai suka shiga famfata suna kurantata,

sannan suka shiga bata shawarwari akan kar tabari maganar su ta bata mata rai da bari yanzu su fara zuwa wajen wancen din ta gyara kanta ta saita kanta ta dawo normal kamar babu abun da yafaru da ita ta kimtsa jikin ta yanzu su nufi inda suka ga ya shiga,

wata tazaro mata  powder tabata ta shafa sannan tasaka turare me ƙamshin gaske da ɗaukar hankalin wanda ya shaƙa,

zee tace ƙawata naso wallahi ba wannan rigar kika sakaba gashi yanzu duk ta ɓoye miki kayanki naso ace wata fitinanniyar riga kika saka yanda kike da shape ɗin nan nasan yana gani zaki ɗaga masa hankali,

ɗan murmushi Rasheeda tayi tace kar kudamu da wannan hakan ma nasan yanda zanyi tafiya komai ya girgiza taku ɗaya girgiza saba'in kwashewa sukayi da dariya daya tace ta gurina shiyasa kike burgeni kinsan takan komai,

hmm kedai bari muje dan na ƙosa ingansa kusa dani banaso yagama abun da yake son samuma insame sa yana cin abinci hakan zaiyi min daidai,

gaskiya ne babbar yarinya kinsan takan komai muje to tafiya suka shigayi gaba ɗayan su itace agaba tundaganan ta canza takun ta tashiga tafiya cikin rangwaɗa da karairaya kamar za aɓala jiki anayi ana girgiza jiki komai na motsawa ahaka suka ƙarasa gurin suna shiga kuwa suka hango sa can kan wata kujera sai ɗan ƙaramin table agaban sa ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yana girgiza ta,

wani farin ciki taji yaƙara nunkuwa akan nada daga bakin ƙofa suka tsaya ita kuma ta shiga takawa ahankali zuwa garesa anayi ana girgiza dan ta yanzuma tafi ta ɗazu ta nufi wajen sa......✍️✍️✍️✍️

masu karatu mai zai faru da Rasheeda mugaya mata gaskiya ko abarta Meer yagaya mata


                   💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'S💖LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
     👇👇👇👇

*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
       by(ster lady)

*2,GIDAN AUNTY*
       by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
      by(xeemat....love)

*4, JINI DAYA*
      by(mrs bbk)

*5,YA FITA ZAKKA*
       by(mum Sayyid)
 
*6,BABY  
      by(mhiz innocent)
[7/16, 11:20 PM] #momyn twins#:   ❤XEEMAT___LOVE❤

💅SARKI SAMEER...💅
             (wasa farin girki)

              
   💖*the talent troupe writer's*💖

                 *Book 2*
    
    *sarki sameer book two na kudine kabiya ka karanta cikin salama kar ka karantan littafi idan baka biyani hakkina ba dari biyu ne 200  bantsawwalaba, ga mai bukata ga account number 8124226526 AZIMA AMINU DAHIRU opay bank sai kuturo da shaidar biyan ta nan 08124226526*

                        🅿️ 90

✨الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر✨✨

✨بسملله الراحمن الرحيم✨✨

Bismilah............✍️

 
      gaba dayan su dakatawa sukayi da abun da sukeyi tare da mayar da hankalin su kan wayar da hamza yake kana ganin fuskokin su zagaka cike suke da mamakin sa,

sarki ne ya mike tsaye cike da bacin rai yatako har zuwa inda hamza yake kwance,

umarni yabasu da su dago wayar da yayi waya sannan aduba number da yayi waya da ita atake kwa suka dauko wayar saidai da security akai mika masa akayi ya bude amma saima yamayar da idon sa yarufe tare da yi musu banza,

sarki da kansa yadaka masa tsawa tare da uban waye kai waye ya turoka cikin masarautar nan ana yi maka magana kamayar da mutane yan iska abun da kake wa mahaifiyata shine yau zakamin kai dan gidan uban waye?

Turo kofar akayi da karfi cikin daga murya akace  dana ne...!!

da mamaki gaba dayan su suka juya suna kallon matar da tashigo musu cikin fada kai tsaye,

karasowa tayi ciki cikin takun isa da takama take tafiya tazo hargaban sarki da yatsa ta nuna sa tace wallahi duk wanda ya kuskura yakara taba min yaro kai bama shikadai ba duk wanda yakara taba daya daga cikin wadannan sai yayi da nasanin haihuwar sa tunda ku babu abun da kuka sani sai zalinci da mugunta mugaye kawai azzalumai,

bata ankaraba taji an wanke fuskarta da mari tare da cewa kiringa iya bakin ki kisan dawa kike magana anan gurin na farko kinshigo cikin fada batare da izinin ba kuma kinzo kina magana dabata dace ba agaban sarki saboda ke mahaukaciyace jahila to da kika zo in kin isa ki hana mu dukansa ne me kika isa kiyi anan ke wace wane matsayi kike dashi dakika isaki dakatar da abun da akayi niya,

kince duk wanda yakara tabashi sai yayi danasni ko to bari adakesa sai muga abun da zaifaru ke bama duka kadai na rantse saina rabasa da ransa agabanki zan kasheshi ki hana yakarasa maganar yana daka mata tsawa,

juyawar da zaiyi yaji ankaiwa wunyan sa mahaukaciyar shaka ana cewa kafin ka kasheni ni bari inkashe ka uwata zakanayiwa magana haka bata girmekaba zaka iya tabani in kyaleka amma baka isa ka taba min mahaifiyata ba ka tsira hamza ke wannan maganr da yaji lokaci daya wani karfi yazo masa da da kwarin gwiwa,

ita kuma matar da tashigo da sauri taje wajen baba tana girgiza shi tanacewa kar ka mutu yanzu ba lokacin mutuwar ka bane ina bukatar ka araye kar ka mutu katashi juyowa tayi taba kallon sarki da shi mamaki ma yahanasa magana yabari sauran sugama nasu ya yanke nasa hukuncin me gaba daya dan ya riga ya kistimawa randa babu ma kara kwana da ransa ayau dinnan sai yasa ankashe kowa da su har matar da takawo kanta tunda yake babu wanda yataba yi masa makamanicin abun da sukayi masa jin zuciyar sa yake kamar zata fashe saboda tsabar bacin ran da yakike cinsa,

cike da daga murya ta kalli sarkin tace kaidai ba halinka mugunta ba to daga yau baza ka karayiwa wani ba kuma wannan abun da kayi kayi na farko kayi nakarshe dan sai kayi da nasani arayuwar ka kuma har abada baza kadaina ba wannan abun sai yazamar maka tabo acinki zuciyar ka tabo ma kuma wanda bazai taba gogewa ba har abada sai nasa ka tsani kanka sai kayi da nasanin da baka taba yiba arayuwar ka,

tunda tafara magana sarki yake kallon ta kawai ko kiftawa bayayi ya kafeta da ido har saida ta gama sannan ya dauke idon sa daga kanta ya mayar dashi kan hamza dake rike ds wuyan mutumin nan har yanzu yaki saki ga sauran suna ta kokarin rabasu amma sun kasa nan ma dauke idon sa yayi yamayar kan Azeema dake kwace kamar matacciya amma idon ta abude yake kawai tsabar azabace yasa takasa motsawa duk da hankalin ta yana kana babanta da matar kuma datake masa magana tana cewa kar ya mutu,

cike da kasaita sarki yafafa zagaya su yana kara binsu da kallo daya bayan daya, sannan yakira wani daga cikin su yana zuwa ya rada masa abu akunne da sauri yafita daga cikin fadar,,

da kyar aka iya raba hamza da wanda ya shakesa ana rabasu kuma suka cigaba da dukan hamza basu dade suna dukansaba sarki yadakatar dasu tare da cewa azubawa tsohon cen ruwa atake suka kwarawa baba ruwa me yawa,

da sauri baba yasauke numfashi me karfi cikin mawuyacin hali lokaci guda duk yatuna abun dake faruwa baisan lokacin da yafara zubar da hawaye ba wannan wacce irin masiface ta sameshi tunda yataso daga yaro har kuruciyar sa bai taba fadawa irin wannan makamancin halin ba baitaba ganin bala'i irin wannan ba amma sai gashi yanzu da tsufa yazo masa wannan masifar ta sameshi shida baisani ba ko Allah yayi laifi ya jarabcesa da wannan masifar ta mutanen nan,

da sauri matar ta kara tashi daga wajen baba ta koma wajen hamza rungumo shi tayi tana cewa kayi hakuri nasan duk ni najefa ka cikin irin wannan halin nacuci rayuwar ka da naturo ka nan amma kayi hakuri nima bada son rainaba bani da zabin da ya wuce inyi hakan hakan shikadai ne mafita agare ni kayi hakuri,
cikin sanyin murya yace umma nasani ya isa haka kiyi hakuri kidaina wannan maganar dan Allah,

Azeema ganin baban ta ya farfado yasata rarrafa da kyar taje wajen sa tana so ta tashi amma takasa, shikuma baba har yanzu baiganta ba,

ganin hakan yasa hamza raba jikinsa da na mahaifiyar sa yayi wajen su Azeema duk da yayi mamakin ganin yanda Azeema ta damu da baba amma yanzu ba wannan lokacinne dashiba yafi barin abun akan kawai ta tausaya masane amatsayin sa tsoho shiyasa tafi tausaya masa,

yana zuwa wajen ya dagota da kyar ta samu ta iya zama da mazaunan ta,

kuka ta fashe da shi tare da dora hannun ta akan sa tace baba da kyar baba ya iya juyo da kansa yasauke idon sa akan da sauri ya mayar da idon ya rufe tare da kara budesu dan ya tabbatar wa dana kansa abun da yagani,

ba karamin mamaki yayi ganin dai dagaske itadin ce,

Ahanakali ya yaɗaga hannun sa zai taɓata tayi saurin riƙe hannun tana ƙara fashewa da kuka tana cewa baba baba katashi karka mutu dan Allah katashi mutafi gida...

ahankali baba ya ƙoƙarta tashi tare da taimakon hamza yaƙarasa zama shima yana zama Azeema ta faɗa jikin shi ta rungume shi sosai tana kuka shima saida ta zubar da kwalar tausayin ta daman mutumin da suka aika yazo yagaya musu yace yarinyar sa tace zatazo cikin gidan nemansa amma yasanar dasu ya dakatar da ita yace kar tazo ya gargaɗe ta kar abarta tazo shiyasa baba bai taɓa tunanin zatazo ɗin ba ashe kwa sai da tazo yanzu gashi za ayi biyu ba ko ɗaya ita bata fita shi baifita ba daman abun da wancen mutumin yayi musu gudu kenan kuma gashide saida hakan ta faru,

da mamaki Hamza yake kallon su Saida yabari suka ɗan tsagaita da kukan kenan sannan ya dubi baba yace baba "kasanta ne daman?

kai baba ya ɗaga masa tare da cewa "ƴata ce zaro ido Hamza yayi ba ƙaramin mamaki yayiba jin wai ƴarsace daman ƴar sa yake so duk loƙacin da ya haɗu da ita basu taɓa haɗuwa da baba sai yau yauɗin ma cikin mawuyacin hali irin wannan da ba damar farin ciki saidai ma baƙin ciki gaskiya baiso ta wannan hanayar suka haɗuba da yasan hakane ai da tuni ya haɗasu kash rashin sani yafi dare duhu,

itama matar gurin ta tsugunna tunda yanzu kamar sarki yabasu damar su tattauna ne dan ita atunanin tama ko angama yimusu hukuncin ya rabudasu shiyasa ya dakatar da sauran ga dukan su,

zama tana zama tace Alahamdulillah naji daɗe da ka farfaɗo da Allah yasa baka mutu ba, kallon ta ta mayar ga Azeema tace sannu yarinya wannan mahaifin kine ko kai Azeema ta ɗaga mata,  sannan ta ƙara cewa amma me yakawoki gidan nan, shiru tayi bata bata amsaba tana tunanin ya za'ayi ta gaya mata agaban sarki ta karawa kanta laifi shiyasa tayi mata shiru,

Hamza zaiyi magana kenan saiga wannan mutumin da yafita yadawo da sauri ya shigo yana haki yace ranka yadaɗe angama shirya komai fitar su kawai ake jira,

bayan ya shigo

57 / 74