Sarki Sameer 2 Wasa Farin Girki By Yaya Azeema

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   43 / 74

126K to 129K   out of 221K words

kai zai janye amma ga mamakin sa sai kawai yaga ta riƙo hannun da sauri tare da kwantar da kanta akai taci gaba da baccin ta mamaki ne ya kuma cikashi dan atunanin sa tana sane take masa haka, tunanin abun da zai mata ya huce ya shiga yi dan haushin ta da yake ji yagama cika da taƙaicin ta,

meƙewa tsaye yayi tare da zare hannun sa da ƙarfi yana zarewa yaje wajen kayan sa cajar wayarsa ya ɗauko ya nannaɗeta yadawo inda take kwance sannan yaye bargon daga jikin ta yana yayewa yaga ta wani haɗe jikin ta waje ɗaya alamun sanyi take ji amma duk da haka bai tausaya mata ba ya shiga tsula mata ajiki da iya ƙarfin sa,

amugun razane ta miƙe zaune tare da fashewa da kuka me ƙarfi  baidaina ba kuma yaci gaba da zuba mata wayar cazar ta ko ina,

  sosai ta shiga rera masa kuka tana jawo bargon dan ta rufe jikin ta amma sa yasa ɗayan hannun ya janye yaci gaba saida ya tabbatar da ta daku sannan yace get out of my room before in canza miki kammani bance kar na tashi naganki acikin gidan nan ba shine harda hawar min kan gado uban wa yabaki izinin kwanciya kusa dani ya faɗa yana daka mata tsawa memakon ta tashin saita ƙara matsawa kusa da fuskar gadon tana kuka tana girgiza masa kai,

   "baza ki tashi kifitaba ina miki magana ƙin tashin tayi ta ƙara mannewa da bangon tana karkarwar jiki,

girgiza kansa yayi sannan yace wannan baki ɗaku bane jefar da cazar yayi yaje ya ɗauko ballet ɗin wandaon sa ya tunkaro ta tunda tagansa ta saki wani kukan me sauti tashiga basa haƙuri amma da tagade da gaske dukan nata zaiyi da sauri ta sauka daga kan gadon ta nufi hanyar ƙofa tana zuwa wajen ƙofar cikin rashin sa'a ta zame agun ta faɗi wata ra zananniyar ƙara tasaki sakamakon buguwar da ƙashin ƙafarta yayi da jikin ƙofar,

dafe kansa yayi tare da ajiye ballet akan gado ya nufo inda take tsayawa yayi akanta tare da buɗe ƙofar yace fita ihu gagara yi tana cewa wayyo ƙafata wayyo ƙafata ƙafata zata cire wayyo Allah na dadda ta fadada ƙafata,

tsugunnawa yayi zai fara janta ya fita da ita saiga Ummy ta shigo da saurin ta ganin su ahaka yasa tayi turus ta tsaya tana binsu da kallo dakatawa yayi da niyar fitar da ita ɗin ya miƙe tsaye yana kallon ummyn tasa,

da mamaki ummy tace hayatee me nake gani mace aɗakin ka me yafaru waya shigo da ita daga ina take tun ɗazu nakejin kukan mace na ɗauka ko maƙotane Saida nafito najide anan samane me ya haɗaka da ita me kuma kayi mata?

ummy wacce tambaya kike so in amsa miki kinbi sai jero min tambayoyi kike,

hararar sa tayi sannan tace duka zaka bani tana masa magana amma hankalin ta nakan Ameesha ganin de yarinyar da gaske take kuka kuma gashi ta riƙe ƙafarta sai tabawa ummy tausayi cike da tausayawa ummy ta tsugunna agaban tana yi mata sannu tare da kamo ƙafar taba ɗagata kwa taga ƙafar har ta kunbura sunnu tashiga yi mata sannan tace subhanallah garin ya akai haka ta faru ƙafar ai har tayi tsami gashi ta kunbua,

  cikin kuka Ameesha tace" faɗuwa nayi na bugu da ƙofar nan,

  "Ayya sorry amma garin ya akai kika faɗi har kikajawowa kanki wannan abun,

shiru tayi bata amsaba hakan yasa tagane meer ne sanadin faduwar tata waƙil biyo ta yayi da gudu,
amma de yanzu ba wannan loƙacin tambayar tata kamata yayi tafara bawa yarinyar taimako kafin kuma shi yaga mata inda yasamo ta,ajiye tunanin tayi ta maida dubanta ga Ameesha sannan tace bari ayi miki ruwan zafi zaki iya tashi?

kai ta girgiza mata alamar a'a,

miƙewa ummy tayi sannan ta dubesa duk yabi ya wani haɗe rai ya haɗe girar sama da ƙasa yana ciccin magani,

sai ka ɗaukota kafito da ita dan bana raba ɗayan biyun kaine sanadin faduwar tata kayi sauri ka sauko da ita bari in ɗora ruwan ɗumin tana faɗa tafara niyar fita daga ɗakin,

Meer yace ummy ki tafi da ita kawai ni bazan iya daukan ta ba bana son ganin ta dan Allah ta tafi tabar gidan nan kar ta bari in sauko inganta agidan nan wallahi sai kusa ɓaɓɓallata,

da mamakin furucin sa ma ummy ta tsaya tana kallon sa saida yagama sannan tace kamar ya ba fahimci maganar kaba ince bakai ka kawota kuma shine kake wa mutane wani zancen da ban dan bangane masa ba waye ya shigo da ita gidan,

cikin ɗan turo baki kamar wani ƙaramin yaro yace ummy nifa bansan taba nima ɗazu ne kawai dana  ɗan fita in zagaya garin na haɗu da ita yake ta tsokano ƴan iska sun biyo ta shine fa na taimaketa daganan kuma tanace min saida ta biyo ni har gida bayan mun shigo na ce mata tazo wajen ku tagaya muku amma shine da yake ita mayyace ina farkawa daga bacci naganta akusa dani shine......sai kuma yayi shiru.,

ummy tace shine kayi mata me ka daketa kuma ka biyo ta ko haka kake so kace mun ba,

kai me yasa baka da tausayi ban hanaka taba mace ba me yasa baka dauki mace da daraja ba yanzu kamar wannan yarinyar ma yar karama me tasani kamata yayi ai kajata ajiki kaji matsalarta tunda har kaganta cikin wannan halin ai kasan de ba dadi ne yafito da ita daga gida ba kasani ma ko bata da iyayen shiyasa ta nace maka tabiyo ka tunda taga ka taimaketa amma shine zakazo kasaka ta adaki ka daketa kuma kabiyota gashinan yanzu kaji mata ciwo watil kashin ta ya goce yar karamar yarinya itama sai ka nuna mata halin ka wannan ai abar a tausayawa ce amma kai bansan me mata sukayi maka ba da ka tsane su dan Allah na rokeka da Allah karage wannan halin karin ga jin tausayin mutane ko ba komai wannan yarinya ce inma zaka nuna tsanar taka ga wasu amma bai kamata ace har yara zaka ringayiwa haka ba ka can za hali dan Allah wallahi banason ganin kana irin wadannnan abubuwan bana jin dadi daman nice ma me biye maka kasan mahaifinka baya son irin wadannan abubuwan dan haka wallahi tun kan yafito yaji abun da ka aikata kayi sauri ka dauko ta muje agasa mata kafar ashafa mata man zafi idan kwa ba hakaba kasan halin sa sarai ni da kaina zanje in sanar dashi abun da kayi inbanda abunka ma kai da kayi aikin lada ka ceceta daga gurin su ai kamata yayi ka karasa ladan ka ni ko ni ka kawowa ita ai zamu kula da ita sannan muji daga inda take amma kazo ka lalata komai dole ma sai taji sauki kafin mahaifin ka yaganta dan in yaga kafarta haka kuma yaji kaine sila ranka sai ya baci,

  ka dauko ta muje kamar ya fasa ihu haka yake ji ji yayi kaf duniya ba macen da yafi tsana irin wannan yarinyar gashi sanadin ta tasa mahaifiyar sa nayimasa fada shikuna aduniya inda abun da ya tsana shine fada ya tsani ayi masa fada ko kadan,

yasan duk abun da mahaifiyar sa ta fada gaskiyane hakan zai iya faruwa indai abu yaji labari to shima fadan zaiyi masa shiyasa bashiri badan yaso ba yana bata rai yasa hannu daya ya dagota,

ummy ta kalle sa tace oh yanzu kuma karya mata hannu zakayi to Allah baka sa'a tana kaiwa nan tayi ficewar ta daga dakin,

tsaki ya doka tare da janta zai fita da ita Ameesha ta saki kara saboda bazata iya taka kafar ta ba shikuma ya tsayar da ita da kafafun ta saboda tsabar mugun ta yasani sairai zataji zafi saboda yaga kunburin da kafar tayi amma ya maze yake niyar janta jin tasaki kara yasa ya galla mata harara murya kasa kasa yace wallahi na kara jin kin daga min murya sai shakeki anan kin mutu banza mayya kawai,

Shiru tayi bata kara buda baki ba,

shikuma ahaka yafara janta tana dan dingishi tana dafa bango tana cije baki take taka kafar da kyar tana jin azabar da take mata amma sai hawaye kawai yake fitowa ba karar kuka saboda zuwa yanzu amugun tsorace take dashi,

gani take idan tayi yunkurin daga muryar zai kashetan kamar yanda yace dan haka tayi shiru tana karbar azabar da takeji,

ahaka suka fito har suka wuce falo suka fito waje suka fara taka bene saida yaga sun kusa saukowa falon gudun kada ummy taga ayanda suka fita yasa ya dauke ta ya karaso falon da ita saida ya duba ko ina yaga ummy bata falon sannan ya dire ta da karfi yanda yasan zata kuma bige kafar haka yayi mata ya tsayar da ita da kafafun ta kuma yasake ta,
kasa kasa tasaki kuka tare da saurin zama kan kujerar da take kusa da ita tana hawaye,

hada ido sukayi da shi ya galla mata harara yana girgiza kai irin sai naci uwarki,

da sauri ta sauke kanta kasa,

ganin ta sunkuyar da kanta ya kuma duba yaga har yanzu ummy bata fito falon ba yasa ya matsa kusa da ita kamar abun arziki zaiyi sai kawai yasamu daidai gurin da ya kunbura yataka da kafarsa harda cije baki sannan ya dagata take ta saki wani kukan me sauti tanayi yamake mata bakin yace wallahi idan kibari taji sai na balla miki dayar kafar shifa haushin ta yake ji so yake yaga kawai yayi mata duk abun da zai mata da zasa taji zafi tayi da nasanin biyoshi shi yake so yayi mata,

da sauri ta kara hadiye kukan,

amma saboda rashin imani irin nasa sai ya kara daga kafar zai takata caraf akan idon ummy kafin yakai yajiyo muryar ta,

"au daman rashin tausayin naka har yakai nan bansani ba yaushe ka kara zama haka ta fada tana karasowa gurin kallon ta yayi cikin hade rai yace ummy me kuma nakara yi bakince in kawota ba kuma gata nan ko kinga nakara yimata wani abun,

"bakayi ba amma ai kana shirn yi din ko yanzu ba taka ta naga kana kokarin yiba saboda tsabar mugunta ko to ka kyauta kayi daidai,

cike da jin kunyar kamasan da datayi yace nifa ba haka zan mata ba kawaide idon kine yagane miki haka yana gama fada ya juya zai bar wajen tace dawo kazo ka fita kasamo mata maganin zafi,

ummy ina dashi ai shi zanje in dauko ko kuma idan kingama gasa mata kawai ki kawota sai inshafa mata yayi maganar ahankali kamar gaske,

da dan mamaki ummy ta kalle sa amma ganin fuskar sa ba wata alama na rashin gaskiya sai taji dadi ta dauka yafara saukowa ne ya dauki fadan da tayj masa saikawai tace to shikenan bari in gasa mata amma de kasan bazan iya daukan taba kabari kawai ingama gasa mata sai kuje tare ka dauketa ka shafa mata nikuma sai inje in hado mata abun da zataci,

dawowa yayi falon ya samu kujera ya zauna yace to ummy ba komai gama matan sai mutafi,

nan ummy ta shiga gasa mata kafar ita kuma tana kuka dan da kyar ma tabari saida taji meer yace zai karba yagasa mata tasan halin sa sarai shiyasa tayj saurin tsayawa ummy ta fara gasa mata tun tana kuka har tafara yin shiru saboda taji dadin gashin ya ratsata taji damadaman kafar,

ana gamawa ummy tace yazo ya dauke ta tashi yayi kamar na kirki ya dauke ta yafara hawa saman benen da ita,

suna tafiya yana zabga mata harara ta gefen ido itade tunda ta fahimci hararar ta yake ta dauke kanta daga kansa ta kawar gefe,

saida ummy taga hawansu sanna ta bar falon ta nufi kitchen din dan ganin abun da zata dafa musu gaba dayan su saboda suma basu karya ba duk suna bacci,

yana shiga falon ya direta akasa yanzu bataji zafi ba kamar dazu dan haka kawai ta dafa bango ta tsaya tare da dan dage kafar me ciwon,,

gaba yayi abun sa batare da ya kulata ba ganin hakan yasa tafara binsa abaya har suka shiga dakin kan capet ya nuna mata yace ta zauna,

zama tayi tana tunanin Allah yasa kar yayi mata wata mugun tar wajen shafa mata dan bata yarda dashi ba wataƙil yayi hakane kawai dan yana gaban mahaifiyar sa,

tana zaune agun yaje ya ɗauko mayuka biyu ya dawo daga ɗan nesa da ita ya zauna sannan yace ta miƙar da ƙafar kamar abun arziƙi ta miƙar da ƙafar har ta ƙarasa inda yake aboniki ya yafara buɗewa sai ya laƙato ɗan kaɗan ya shafa shi ajikin murfin ya miƙa mata hannu tasa ta karɓa tana jiran jin me zaice sai yace ki shafashi a hannun ki kamar mai haka ta lakace shi daga murfin tasaka atafin hannun ta tafara murtsikawa da tagama sai ta ɗago ta kalle sa cikin ƙara haɗe rai baice mata komai ba sai ya ɗaoko wani kwalban na wani mai kuma ba man zafi bane kamar ma nml man shafawa shi ya lakato wajen kwatan roban ya dan ɓara mata akan ƙarfar sannan cike da mugun ta yafara danna mata ƙafar take ta saki ƙara bai saurareta ba harda cije baki wajen ƙara dannawa gashi ya riƙe ƙafar da ɗayan hannun ba dama ta kwace,

sosai ta shiga yin kuka tana kwace kwace zata kwace ƙafar amma takasa hawaye duk yagama wanke mata fuska harda majina gaba ɗaya fuskar tayi wani gaje gaje da ita,

batare da yasaki ƙafar ba ya ɗago kansa ya dubi yanda fuskar ta tayi, wani daɗi yaji aransa daman haka yakeso yagani dan haka sai yace idan kina so insakar miki ƙafa to kifara saka hannun ki ki goge hawayen nan kar inga ko ɗigon danshi akai,

Allah sarki baiwar Allah jin hakan yasa da sauri tashiga goge hawayen ta da hannun ta manta ta taɓa aboniki shikuma yana sane daman yayi mata haka shiyasa yafara bata ta shafa ahannu sannan yace ta goge fuskar ta dashi saboda idan ta goge hawayen man jiki zai taɓamata fuska gaba ɗaya ,

take tafara jin zafin abonikin a idon ta kif kifta idon tafara yi tun tana daurewa har taji ina abun yafi ƙarfin ta fuskar ta gaba ɗaya ta ɗauki zafi,

yana ganin haka ya tashi yaje ya rufe ƙofar harda saka key ajiki sannan ya koma kan kujera yayi zaman sa yana jinta tana kuka saima ya ɗauko wayar sa ya toshe kunnuwansa yana danne danne wayar sa,

ita kuwa idon ma ya rufe gaba ɗaya ga zafi ga hawaye sai abun ya haɗu ya caɓe mata ga ƙafar sai zugi take mata kamar zata cire haka take ji,

ji tayi ana buga ƙofar amma ba halin tashi ta buɗe saboda tanajin sa loƙacin da yasaka key ajiki kuma yama cire key ɗin daga jiki,

Ummy da tagaji da bugawa gafara kiran sunan sa hayatee ka buɗe ƙofar mana tana magana tana cigaba da bubbugawa amma baisan ma tanayi ba,

loƙaci zuwa liƙaci de yana ɗagowa ya dubeta yaga yanda take kuka sai ya kuma juyar da kansa ransa fari tass haka yake ji yasan zuwa yanzu zafin abun yafara barin ta saboda ɗaki akwai Ac, amma duk da haka ba yanzu zai kulata ba sai tagama gajiya dan kanta ta tashi tace zata fita sannan yayi mata gargaɗin idan tafaɗawa ummy wani abun sai yayi maganin ta,

ummy da tagaji da bugu hankalin ta gaba ɗaya yatashi tayi saurin ajiye try din da ta ɗauko abinci agefan ƙofar ta ajiye sannan tayi sauri ta sauka ta ɗauko wayar ta ta dawo bakin ƙofar sannan tadanna masa kira yana zaune yaga kiran ta ya shigo wayar fara tunanin abun da zaice mata ya shigayi bai ɗaga ba har kiran ga katse yana katsewa sai kawai ya tashi yaje ya buɗe ƙofar yana buɗewa ummy ta sauke ajiyar zuciya tare da cewa me yafaru ina ta bugu baka buɗe ba na daɗe anan amma bakuji ba lafiya de ko? tayi maganar tana shigowa ciki gurin Ameesha taje da sauri tana yi mata sannu kallon fuskar ta tayi taga duk tayi jaa,

tana ɗagowa tunkan tayi magana meer yayi saurin cewa ina cikin shafa matane taje ta taɓa gurin bayan kuma nagama shine ta taɓa fuskarta da hannun tun ɗazu nake bata haƙuri taƙi yin shiru, sosai Ameesha tayi mamakin abun da yace amma bayanda zatayi bazata iya ƙaryatasa ba shiyasa tayi shiru kawai tana faman shashsheƙar kuka tare da sauke ajiyar zuciya akai akai,


kallon sa ummy tayi kamar de bata yarda da zancen sa ba amma sai kawai tace ayya sorry kiyi haƙuri ko awanke miki fuskar ko zaki fi jin dama dama,
kai ta ɗaga mata alamar eh,
to zaki iya takawa nan ma kai ta ɗaga mata amma aranta tasan bazata iyaba amma bataso tace bazata iyaba ace ya ɗauke ta daga nan kuma yasamu damar da zai ƙara yi mata wata mugun tar,

da taimakon ummy ta miƙe tsaye amma tana miƙewa sai tayi saurin riƙe ummy saboda azabar da taji tama fi ta koyaushe,

sannu ummy tayi mata sannan tace hayatee kaga bazata iyaba ɗauko ta kawai muje wannan ai saidai ma ayi mata wanka dan naga alamar duka jikin tama ba daɗi yake mata ba duk yayi tsami muje agasata da ruwan zafi sai tafi jin daɗin jikin ta,

tabb Ameesha ba ƙaramin tsorata tayi ba jin ance wai za ayi mata wanka da girman ta za ayi mata wanka duk da itama tana mugun buƙatar wankan amma bazata taɓa yarda ayi mata ba gwara tace gaba da zama ahaka,

kamar ya haɗiyi zuciya ya mutu dan baƙin ciki haka yake ji shifa ya tsani ya haɗa jiki da ita bayanda ya iya dole ya sunkuceta cikin fushi yakaita banɗakin yana gama ayyana abun da zai kuma yi mata dan wallahi tunda ta shigo rayuwar sa ba shi kaɗai zai shiga uku ba itama ta shiga uku duk sanda zata sa ace yayi mata wani abu to sai yarama ta wani ɓangaren,

ummy ce taje ta haɗa mata ruwan zafi me ɗumi sannan da taimakon ta cire kayan ta sai Ummy ta haɗa mata komai sannan tace to tayi bari ta bata waje,

43 / 74