ta ƙuarawa ido batare da ko ƙiftawa ba haka take kallon ƙafar tade san tabbas batayi mata kama da ƙafar waɗan cen mutanen ba.......
Ayi sallah lafiya gobe sallah baza kusame update ba saidai zuwa jibi ko gata idan Allah yakaimu
💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'S💖
*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
👇👇👇👇
*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
by(ster lady)
*2,GIDAN AUNTY*
by(mss lee)
*3,SARKI SAMEER*
by(xeemat....love)
*4, JINI DAYA*
by(mrs bbk)
*5,YA FITA ZAKKA*
by(mum Sayyid)
*6,BABY
by(mhiz innocent)
[6/30, 10:03 PM] #momyn twins#: ❤XEEMAT___LOVE❤
💅SARKI SAMEER...💅
(wasa farin girki)
💖*the talent troupe writer's*💖
*Book 2*
*sarki sameer book two na kudine kabiya ka karanta cikin salama kar ka karantan littafi idan baka biyani hakkina ba dari biyu ne 200 bantsawwalaba, ga mai bukata ga account number 8124226526 AZIMA AMINU DAHIRU opay bank sai kuturo da shaidar biyan ta nan 08124226526*
🅿️73&74
✨الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر✨✨
✨بسملله الراحمن الرحيم✨✨
Bismilah............✍️
" "ɗaya daga cikin sune takai hannu zai kamota yana dariyar mugunta yace ke har kin isa ki gudar mana zonan wallahi baki isa kin gudar mana ba duk inda ma zaki sai mun kamaki yana wannan maganar loƙacin da yakai hannu zai taɓata saidai bekai ga kaiwa jikin ta ba yaji an riƙe masa hannu ƙam a harzuƙi ya ɗago dan sauke wa mutumin dake tsaye sarai sun gansa amma suka nuna kamar ma basu san da zaman sa ba,
bai gama daidaita tsayiwar sa ba yaji ya murɗe masa hannu azaba tasaka shi sakin ƙara wata razananniyar ƙarar yasaki sakamakon jin ƙarar karyewar ƙashin hannun sa,
da sauri su garbe sukayi kanta zasu ɗauke ta tayi saurin tashi tana tashi tayi kan mutumin da ya taimaketa ɗin bayan shi taje ta ɓuya,
ogansu ne da ransa yagama dugun zuma yakai ƙololuwar ɓaci yayi kan mutumin da niyar kai masa naushi kafin yakai nasa naushin yaji ansauke masa wani wawan bugun da atake bakin sa ya fashe yafara zubar da jini amma duk da haka bai daɗara ba ya ƙara kaimasa hannu zai buge sa aikwa nan mutumin yakaiwa wuyan sa damƙa ya shaƙe masa wuya ya fara naushin bakin sa ga shaƙa ga naushi ba saki bakin sa ba saida ya zubar masa da haƙoran bakin sa sannan yasake sa daga nan kuma yabi jikin sa da suka saida yaga ta dena motsi sannan ya rabuda shi yakoma kan garbe dake faman ja da baya yana niyar guduwa taku biyu yayi ya shaƙosa shima nan ya shiga dukansa ya fasa masa kai sakamakon bugashi da ginin wajen da yayi atake kansa ya fara zubar da jini shima ya sumar dashi ataƙaicede saida yayiwa kowa lilisa ɗayan kuma baɓɓalasa kawai yayi ƙafa da hannu ba inda yabari da za amora sannan ya rabu dasu haka,
"cikin takunsa na isa da ƙasaita ya fara takawa zuwa inda tayi suman tsaye tana kallon sa tunda yafara dukan su ta zubawa bayan sa ido duk da tagaji da tsayiwar ƙafafun ta sunyi mata nauyi amma saboda tsabar al'ajabi da mamakin ganin yanda yake faɗa hakan ya hanata motsawa daga gurin,
ga mamakin ta yana zuwa kusa da ita kamar zaiyi mata magana sai kawai ya gota ta gefen ta yayi wucewar sa batare da yace mata komai ba,
juyawa tayi da ƙyar tabi bayansa da kallo ganin de da gaske tafiya zaiyi yasa tayi saurin bin bayansa da ɗan gudun ta tana zuwa ta faɗa kan bayansa ta riƙesa gam tare da zagaye hannun ta akan cikin sa,
cak yaja ya tsaya yakasa ci gaba da tafiyar da yake yi sarai yasan itace dan haka baiyi mamaki ba saidai yayi mamakin meyasa kuma zata biyo sa kin cemata komai yayi kawai ya tsaya yaga iya gudun ruwan ta yanaso yafaraji daga gareta yaji me zatace,
itama kuma anata wajen so take yace mata wani abun amma taga baida niya dan haka kawai itama saitaja bakinta tayi shiru kuma batare da ta sake shi ba harda ƙara kwantar da kai abayan sa kuma duk yana jinta amma baice mata komai ba,
sunkai wajen minti goma ahaka daga ƙarshede da yagaji cike da taƙaicin yarinyar yasaka hannun sa yaraba jikinsa da nata tare da matsawa gefe ya watsa mata kallon banza sannan ya sake juyawa zai tafi,
bata daddara ba taƙara binsa tayi saurin shan gabansa,
harara ya wurga mata yana haɗe girar sama da ƙasa aransa yake ayyana wannan mayyace ko aljan yau yagamu da ita tana neman ta takurawa rayuwar sa,
tagefenta ya ƙara ratsawa zai wuce tayi saurin riƙo hannun sa tana girgiza masa kai tana hawaye fuskarta duk ta ɓaci da hawaye,
ko kallon ta baiyi ba ya runtse idon sa cikin kausarsiyar muraya ya daka mata tsawa da cewa "How dare you.. don't touch me again if not I will teach you a lassen, leave me alone yana gama faɗar haka cikin daka mata tsawa ya fusge hannun sa ya ƙara gaba, batare da ya tausawa halin da take ciki ba,
yana tafiya yana ta faman zabga tsaki ji yake dama baifito ba shide tunda yafara tahowa garin nan yake fuskantar ɓacin rai tun jiya ake ɓata masa rai gashi yauma da sanyin safiya ya haɗu da wasu mahauka tan musamman waccen yarinyar dan yafi jin haushin ta ɗan duk atunanin sa itace tajawa kanta inbanda haka tana ƴar ƙaramarta yarinya da ita ina ta baro iyayenta tafito da safennan Allah yaƙara ma sai yaji dama bai taimake taba ya rabudasu suyi mata abun da suka ga dama inyaso gobe bazata ƙara fitowa waje ita kaɗai ba, sai da nasani ma yakeyi,
yaɗanyi nisa da tafiya yajiyo takun tafiyar ta abayan sa bai tsayaba yaci gaba da tafiya batare da ya tsaya ba,
shan gabansa ta karayi cikin kuka shaɓe shaɓe harda shashsheƙar ta kuma takasa magana ba zato ba tsammani kawai yaji ta faɗa masa kan ƙirjin sa rungume shi tayi sosai sai kuma ta fashe masa da kuka sai yanzu abubuwan da suka faru da ita suka fara dawo mata arai tunawa da tayi da tuni yanzu tana cen hannun su suna wulakanta ta da tuni yanzu wani labarin ake ba wannan ba da tuni sun rabata da mutuncin ta daga nan kuma ta barmusu duniyar dan bata tunanin idan sukayi mata haka zata iya cigaba da rayuwa tasan mutuwa zatai da tuni yauce ƙarshen ta aduniya shikenan bazata ƙara ganin daddar taba da ta rage mata gatanta aduniya sosai tashiga tunani kala kala tana ƙara riƙeshi kamar zata shige jikin sa tana kuma sakin wani irin kuka ga duk wanda yaji irin sa dole ya tausaya mata dan ba ƙaramin kuka take ba kuka take me tsuma zuciyar me sauraro, dan kamar ranta zai fita haka take kuka.....
shiru yayi yana sauraron kukan nata duk rashin imanin sa saida yaji ta bashi tausayi amma shi baisan yanda zaiyi da itaba dole ta rabu dashi yatafi baisan ta batasan shiba kuma bazai iya kaita can gidan suba to idan ma yakaita yacewa su ummy a ina ya samota kai inama zaman mace a inda yake bazai iya ba yana gama tunanin hakan ya yanke shawarar tafiya ya rabuda ita saidai kuma yama fara ƙoƙarin raba jikin sa da nata ta ƙara riƙeshi ta cukuikuyi shi tana ƙara shigewa jikin sa,
abufa yakusan fin ƙarfin sa duk yanda yaso ya rabata da jikin sa ya gagara yarinya tabi ta riƙeshi ta hanasa tafiya da yaga abunna ta hakane baza ta rabu dashi ba sai yace mata sakeni mutafi to amma duk da haka taƙi yarda ta sakeshi,
shide yarasa yau da wacce irin yarinya ya haɗu da ita badan yana ɗan jin tausayin ta ba da tuni ya fatattake ta amma ba yanda ya iya dole ya taimaketa tunda shi yajawo wa kansa da kansa,
daga inda suke a tsaye ya kawai ya ɗagata cak ya saɓata akafaɗa yashiga tafiya da ita amma zuwa yanzu ta rage kukan da takeyi sai shashsheƙa kawai takeyi.....,
ahaka yaci gaba da tafiya cike da taƙaicin abun da yafaru har ya ƙarasa gida kwankwasa wa yayi me gadi ya buɗe masa yana masa sannu da zuwa cike da mamakin ganin sa da yarinya akafaɗa amma de amatsayin sa na me gadi ba hurimin sa bane dole yaja bakin sa yayi shiru yana binsu da kallo har suka shige,
da sallama ya shiga falon gidan amma kasancewar safiya ce babu kowa acikin falon yasan duk suna bacci basu tashiba kuma aƙa idarsa indai mutum yana bacci baya tashin shi daga bacci dan haka kawai yayi sama da ita zuwa ɗakin sa,
itade tayi lamo ajikin sa tana kallon gidan ahaka har ya haura upstairs ɗin da ita yakaita ɗakin sa yana shiga ya kwantar da ita kan Capet ɗin ɗakin dan acewar sa baza ta taɓa masa wani daga cikin dakin ba saboda kayan ta duk sunyi datti,
yana shirin tashi ta ƙara riƙoshi kallon da ya watsa matane yasa ta haɗiye kukan da take shirin yi kuma tayi saurin sakin sa,
kaɗa kai kawai yayi batare da yace mata komai ba ya nufi bathroom dan yin wanka saboda gaba ɗaya ƙyanƙyamin kansa yake da kayan jikin sa dan ba yanda zaiyi ne ta riga ta taɓashi tun farko batare da sanin sa ba amma da bazai bari ta raɓe saba,
kayan jikin sa ya shiga tuɓewa yanayi yana taɓe fuska kamar me taɓa kashi haka yakeyi da fuska haka yagama cirewa daga shi sai gajeran wando yayimar kayan yayi ya buɗe ƙofar ɗakin yafita waje ya watsa su waje ta window sannan ya dawo Allah sarki baiwar Allah dake agajiye take taji sanyin Ac ya ratsata ai tunda ta rufe idon ta loƙacin da taga yana ƙoƙarin cire kaya tayi saurin rufe idon bata ƙara buɗewa ba bacci yayi gaba da ita tun kan yadawo cikin ɗakin,
yana shigowa bai kalli inda take ba ya wuce banɗa ki yayo wanka sannan ya fito ya shafe jikin sa da mayukan da yazo dasu,
sannan ya sauya wasu kayan ya ɗauko kayan ciye ciyen sa yaci abun sa duk abunnan da yake yana sane da ita aɗakin saidai bai kalli inda take ba saida yagama komai ya hau kan gadon sa sannan batare da ya kalle ta ba yace idan kin gama zaman ki tashi kije waje idan mutanen gidan sun tashi sai ki gaba tar musu da kanki suyi yanda zasuyi dake idan taimako kuma kike so kigaya musu suyi miki abun da zasuyi miki ki ƙara gaba nagama yi miki abun da zan miki kuma kar kibari intashi inganki acikin gidannan ni na kawoki amma banason zamanki anan kiyi kibar gidan yana gama faɗar hakan ya juya mata baya yayi kwanciyar sa batar da yasan halin da take ciba kuma baidamu da rashin amsar taba......, aɓagaren ta kuwa batama san yanayi ba dan bama ta duniyar ta tafi duniyar bacci......,
*************************
tunda safe su sameer suka haɗa kansu alahamdullillh jikin bossay da sauƙi yana tashi yajishi garau saidai kuma tunda safe Sameer yace ya kashe wayarsa shima kuma daman tunanin hakan yake dan yasan dole akira shi daga gida kuma yasan halin dadda tunda tace sai anhaɗa ta da Ameesha tofa yau saita Allah dan haka gwara ta kira layin sa taji akashe ammade bata ɗaga musu hankali ba kuma batasan inda suke ba dan haka dole tayi haƙuri tabari har sai ya koma gida hakan sai ya fiye masa kwanciyar hankali,
Wajen ƙarfe goma da rabi suka fita daga gidan gaba ɗayan su harsu hamra da Ammar,
acikin mota hamra ta ƙara basu labarin motar da tagani ɗazu da safe gaba ɗayan su sunyi mamaki amma wasu daga cikinsu basu yarda ba,
Sameer ne yace amma meyasa baki faɗa mana ba tun kan mufito daga gida shiru tayi bata basu amsa ba,
shettima ne ke tuƙi dan haka daman basuyi nisa da fitowa ba sameer ya kalle sa yace mu koma gida,
shettima ya kalle sa yace mukoma fa kace yaza ayi mukoma bayan mun kusa ƙarasawa ai ni ina ganin gwara mufara zuwa can kar su rigamu zuwa suje suyi wani ƙulla ƙulan nasu mukasa samun wata sheda ko ɗaya inyaso wanann me sauƙi ne idan mun dawo gida mayi duk abun da zayi saboda mutum ɗaya zamu riƙa me gadi tunda ya buɗe musu ƙofa suka shigo kuma suka fita ai dole yasan ko suwaye suka fita nidai ina ganin gwara mufara zuwa ɗin tunda wannan bama mu da tabbas kasande halin Amra da shiriri ta wataƙil ma wata motar ta gani ta zata waccen ce amma in ba hakaba me zai kawo motar cikin gidan nan batare da sanin kowa ba indai har ta shigo koma waye ya shigo ai ansan dashigowar sa,
gaskiya ne maganar ka hakan yakamata mufara yi kaga idan mugano wani abun sai nufi tabbatar wa saboda muna da hujja a hannun cewar bossay da haka suka yarda kowa yayi na'am da maganar akan sai sun dawo sai kuma a tambayi me gadi....
**********************
tunda asuba dadda take nacin sai ankira mata bossay amma ankira wayar taƙi shiga dan haka tasakasu agaba sai anfito mata da jikarta dan Wallahi baza ta yarda ba idan ba da rashin gaskiya ba a al'amarin me yasa zai kashe wayar sa saboda yaji tace sai taga jikarta yau shine yaƙi dawowa kuma ya kashe wayar sa saboda yasan basu da gaskiya,
Sude su Ammi sun rasa yanda zasuyi da ita sunyi iya bakin ƙoƙarin su wajen sun ganar da ita amma ta rufe ido taƙi sauraron kowa dan haka kuwa kowa yarabu da ita kowa yaci gaba da sabgar gaban sa,
dadda da taga haka sai ta koma ɗaki ta ɗauko mayafin ta da ɗan canjin da take dasu ta fito falo tana shirin fita daga gidan Ammi ta fita daga kitchen da sauri ta ƙaraso wajen tana cewa dadda yanzu fisabilillahi bazakiji maganar da muke miki ba meyasa kikeyin haka waɗan nan mutanen ba mayaudara bane bazasu taɓa cutar da Ameesha ba amma kinƙi sauraron kowa yanzu dakike niyar fita kinsan inda take ne ina zakije,
Kinga Aminatu nifa wallahi babu wanda ya isa ya rabani da jikata wallahi sai naje sun fito min da ita idan kuma sun kasheta ne saidai hukuma ta rabani da su idan ku kun kasa ni zanje da kaina bade ance ɗan sarkin garin nan bane to ai matambayi baya ɓata zanje har gidan sarkin insanar dashi abun dake faruwa asan yanda za ayi a fito min da jikata dan bazan juri rashin ta ba wallahi bazan taɓa lamin taba akan duk wanda ya taɓamin jika yarinya marainiyar Allah amma anbi an takurawa rayuwar ta anrabata da iyayen ta shine itama sai anga bayan ta so na kuɓuta daga sharrin waɗan cen su basu kasheta sai sune zasuzo har gida su ci amanata ingama basu labarin ta amma memakon su tausayawa rayuwar baiwar Allah amma sai sunemi suci zarafin ta su kasheta to duk ma wanda ya aikata mata hakan wallahi idan mafarkin nan ya zama gaskiya sai inda ƙarfina ya ƙare ko zan rasa komai arayuwata sai na ƙwatar mata ƴanci sai wallahi sai duniya tasan abun da akayi mata dan haka koyi haƙuri kibarni dan bazan taɓa sauraron duk abun da zakice min ba nasan ke mutuniyar kirkice amma daman ance ka haifi ɗa baka haifi halin saba bazan iya yabon ɗanki ba akan basa hannun sa aciki ba tunda har dashi nagani amafarki kuma ga alama nagani da yaƙi dawowa kuma yakashe wayar sa kinga kwa dole inyi zarginsa kiyi haƙuri idan kinji haushina akan zargin da nayi masa saduwar alkhari nagode da mutuncin da kiakyi min bazan taɓa matawa dake ba arayuwata kingama yimin komai kuma nayarda dake dan haka natafi kuma ba lalle indawo cikin gidan nan ba koda ace naganta to zan ɗauketa ne muyi nesa da garin nan shiyasa daman tunfarko bana son inhaɗa mu amala da kowa saboda gudun matsala irin wannan tana gama faɗar haka ta share hawayen da ya zubo mata tare da rungume Ammi sannan ta ra jikin ta da nata sannan tayi saurin juyawa ta fice daga gidan tana share hawayen ta,
mutuwar tsaye Ammi tayi bata taɓa tunanin dadda zatayi mata haka ba yanzu tana nufin ta tafi kenan baza ta dawo cikin gidan ba me yasa dadda zatayi mata haka me yasa dadda bata jin magana,
jiri taji yana niyar ɗinbanta da sauri tayi saurin dafe bang,
tunanjn me ya hana bossay dawowa gida da kuma kashe wayar da tayine ya tsaya mata arai ga kuna abubuwan da dadda ta fada tana cikin tunane tunanen naji zubar hawaye akan kumatun ta hannu tasa ta share tana me jin quna acikin zuciyar ta wani abune yazo ya tokare mata arai jitake kamar ta dora hannun akai ta kurma ihu haka take ji,
jitayi andafata da sauri ta dago duk atunanin ta ko dadda ce tadawo hada ido sukayi da farouk cikin sanyin murya yace Ammmi me yafaru naga kina kuka kasa bashi amsa tayi saboda wani kukan da taji yana shirin tahomata,
rungumeta yayi yana bata hakuri da kyar ta iya cewa farouk dadda ta tafi ta tafi ta barmu tace bazata dawo ba, ta qarasa maganar cikin matsanaciyar damuwa,
da sauri ya raba jikin sa da nata shima cikin damuwa kamar zaiyi kuka yace Ammi me yasa kika barta ta tafi Ammi zata iya fadawa wani halin fa tun yaushe ta tafi Ammi kikara kiran yaya ko zai dauka kiji ina yake kinji Ammi duk yabi ya rikice sai faman jero mata tambaya yake jero mata,
riqo hannun sa tayi tace kwantar da hankin ka in sha Allah babu abun da zai sameta kuma in Allah ya yarda zatadawo kar kasaka kanka adamuwa Allah sarki uwa ganin yafita shiga damuwa yasa itama kwantar da damuwarta dan taga ta cire shi daga damuwa haka taita rarrashin sa har yasauko amma gaba dayansu ba sukuni agaresu kowa yayi jigum jigum abun duniya ya ishesu......,
************************
Su sam suna karasawa wajen mall