fitar ta tashi zata bi bayan ta Amra tayi saurin tarar gabanta zata cigaba da tsokanar ta dadda ta haɗe rai tace wallahi ko ta matsa mata ta rabu da ita ko kuma tayi mata abun da ta tsana idan taja gashin ta bazata saki ba har sai tagansa a hannun ta tsoro ne yakama Amra tasan kaɗan daga cikin aikin ta ta aikata mata hakan dan haka ba shiri ta matsa tabata hanya dadda ta fita daga ɗakin,
tana zuwa falon tayi turua ta tsaya ganin duk basa nan babu kowa afalon,
ranta ne ga ɓaci watakon mutanen nan shanyata sukayi suka gudu suka barta ita tana nan tana jiransu ashe su guduwa sukayi to zasu gane kuren su badai ta riga da ta shigo gidan ba yanda neman gidan bai bata wahala ba haka neman gurin sarki bazai bata wahala ba dan haka bata tsaya wani tunani ba kawai tabi ƙofar da ta shigo ta buɗe ta fita tana fita su Amra suka fito suna kiran ta amma ina ko jinsu ma batayi ba ta riga da har ta fita,,,
tana fitowa sai ta tsaya rarraba ido tana tunanin hanyar ina zata nufa wata hanya kawai tabi batare da tasan ina zata ba kawai tafiya take,
shettima da yafito waje daman gurin motar sa ya nufa har zai shiga yatafi gida sai ga kiran sam yashigo wayar sa yana ɗagawa kawai
yace "kana gidan har yanzu ko ka fita?
shettima yace "a'a yanzu dai nake son fita inama gurin mota shiga zanyi ka kirani,
"Ok" 'to kajirani karkafita yanzu zan ƙaraso,
"Ok" sai ka ƙaraso ɗin yana gama faɗar haka yakashe wayar,
rufe motar shettima yayi tare da juyawa dan komawa inda yafito yana shan wata kwana ɗaga idon da zaiyi ya hango dadda tana tafiya da sauri ya juyar da kansa dan karta gansa yafara sauri yana ɗaga ƙafa dan ya ɓacema ganin ta,
saidai abun da baisani ba yana shawo kwana ta gansa kuma taga duk saurin da yake dan haka itama ta ɗaga ƙafa tabi bayansa tana ganin part ɗin da yashi ta rage saurin ta saboda daman tagaji tayi tafiya me tsawo gashi kuma yanzu tana ta sauri shiyasa da taga inda ya shiga sai tarage saurin ta shiga tafiya ahankali, awa
yana shiga ya sauke ajiyar zuciya afili yace Allah ya taimakeni bata gannin ba dana shiga uku koma mai yafito da ita oho mata wannan tsohuwa tafiya bala'i wallahi yana gama surutan sa yayi sauri ya nufi part ɗin sam,
Azeema da taji motsin kamar fulani zata fito daga ɗakin ta tayi saurin yin saɗaf saɗaf ta juya tabar wajen zuciyar ta kamar zata fito waje saboda tsoro sai yanzu take ƙara jin tsoron matar ashe tana gama wanke wanke ta ta taho zata gayawa Fulani sai kuma taji wayar da take dan haka ta kasa kunne rabi da wani abun na abin da Fulani tace duk taji akan kunen ta tafaɗa,
harta tana harɗewa wajen yin sauri da sauri ta ƙarasa ɗakin su tana shiga ta faɗa kan katifar ɗakin tana sauke ajiyar zuciya sai yanzu da ta ganta aɗaki hankalin ta ya kwanta tunanin tashiga yi shin me wannan matar take ɓoyewa da take jin tsoron asani aikawa indai hakane zata bibiyi wannan saurayin da ya nace mata zata tambaye sa tunda taji yace yasan komai itama kam sai ta gano komenen haka ta zauna tarin ga tunani kala kala akan fulani......,
dadda na ƙarasowa part ɗin batare da tayi sallama ba ko ta nemi iznin shigowa ba kawai ta tura ƙofar ta shiga kanta tsaye shigar ta tayi daidai da fitowar Fulani daga ɗakin kallon kallon suka shiga yiwa juna......,
dadda ce ta fara kawar da kanta daga gareta sannan tace barka da gida dan Allah wani yaro da ya shigo yanzu nake nema naga kamar nan yashigo,
yanda kasan da gini tayi magana haka Fulani tayi da ita bata yanka mata ba,
Ganin haka yasa dadda ta girgiza kai kawai bata ƙara cewa komai ba sai kawai ta shiga dube dube afalon tana leƙeƙe tana so ta gano inda shettima yake,
Fulani bata ɗauke idon ta daga gare taba taci gaba da takowa zuwa inda take tana me mamakin ganin ta acikin,
"Nace ba keɗin wacece da zakishigo min kai tsaye ba abaki iznin shigowa ba waya ce miki ana shigo min guri kai tsaye idan barar ki zakiyi bana nan zaki shigo ba ba asanar dake yanda tsarin yake ba wayema yabarki kika shigo cikin gidan nan kuma har bangarena,
banza dadda tayi da ita wata ƙofa ta gani tayi lungu a hasashen ta ko nan shettima yabi dan haka bata kula fulani ba tayi gaba zata wuce,
taƙaicin ranin hankalin da fulani taganj matar na shirin yi mata yasa ta riƙo rigar ta baya tajawo ta ta dawo gabanta cikin daka mata tsawa tace ke wacce irin mahaukaciya ce anan miki magana kin maida mutane ƴan iska kishigo har inda nake kice zakiyi abun da kika ga dama gidan ubanwa kike shirin zuwa,
"gidan ubanki nace gidan ubanki zani kinji mu da ƴar iskar mata anshigo ɗin ko gidan nakine ke kaɗai bakisan manya ba bake yakamata kifara gaidani ba amma maimakon kimin magana mai daɗi shine zaki min hauka akai to ni nawa haukan yafi naki da kinbini ta lallami da kinsamu amsarki amma tunda tahaka kika biyo sai ki shaƙeni ingaya miki idan kina da ƙarfi, dalla malama sakarni kibari masu gidan suyi magana danni da ƴar aiki ma kikafi kama daman ance irin ku idan suka samu waje sunfi ɗan gida iya shege to wallahi kibini ahankali idan bahaka ba jikin ki yagaya miki danni bana ɗaukar hauka yanzu zan saitawa mutum hanya ya shiga taitayin sa, tana kaiwa nan ta fusge jikin ta daga hannun fulani tana shirin ta cigaba da tafiya inda tayi niyar zuwa,
da sauri fulani ta ƙara jawota a harzuƙe ta ɗaga hannun zata sauke mata shi afuska,
caraf dadda ta riƙe hannun ta tare da wurgi dashi da ƙarfi da har saida yasa Fulani tayi baya kaɗan kamar zata faɗi,
da yatsa dadda ta nunata wallahi idan kika kuskura hannun ki yataɓa jikina sai kinyi da nasani na rantse da Allah saina koya miki hankali,
azafafe fulani tace ke kinsan wacece ni da kike gaya min duk maganar da kika ga dama kizo har masarauta ta kice zaki gaya min magana kuma ki kwana lafiya to wallahi baki isa kinbar cikin gidannan lafiya ba yau sai kingaya min uban da ya tsaya miki kikazo kikewa mutane hauka anan dan naga alamar ina jin bakya cikin hayyacin ki kike wannan maganar kina buƙatar adawo dake hanyar daidai, sai ansai ta miki tunanin ki da ƙarfi ta kwalawa murja kira tana amsawa yafito da sauri hartana haɗawa da gudu gudun ta ta ƙaraso wajen tana zuwa fulani tace "je kikira min sarki dorina da bafade da Sarkin su duk kice suyi sauri suzo kiran gaggawa ne,
da sauri ta fice daga falon ta,
dadda ce ta kwamshe da dariya tace aikin banza ashe ma taƙamar taki ta banzace tunda bazaki iya ɗaukar mataki da kanki ba sai kinsaka an ɗaukar miki wallahi kinban mamaki tsohuwar banza kawai, ni banda loƙacin ki ba gurin ki nazo ba da harkike cewa nazo bara kalata da shiga ta tamiki kama da wacce ta nemi wani abun arayuwata ta rasa ko tufafina sun miki kama da hakan saboda tsabar wulaƙanci da cin fuska ne yasaki faɗar haka ko?
Azeema da tajidai hayaniyar tayi yawa yasa tayi saurin fitowa daga dakin ta ɗan leƙo tana leƙowa idon ta yasauka akan dadda zato ido tayi tana me mamakin ganin ta me yakawo dadda gidan nan inna lillahi wa inna lillahi raji'un Allah yasa ba mama ce ta turo taba da sauri ta koma ɗaki dan tana godewa Allah da bata fito gaba ɗayan ta ba tasan idan dadda taganta shikenan asirin ta zai tonu,
duk abun da suke shettima na kallon sa daga bakin ƙofa kawai so yake yaga yanda wasan nasu zai ƙare yasan halin ko wacce daga cikinsu dan haka babu wacce zata ɗagawa wata ƙafa kowacce ƴar kanta ce basu da haƙuri gaba ɗayan su ita fulani nuna isa da gadara da wulanƙan ci ita kuma dadda bata ɗaukan raini ko kai waye baka isa ka taka taba kuma ta taku dan haka yana gurin har dariya yakeyi ƙasa ƙasa saboda faɗan nasu ba ƙaramin ƙayatar dashi yayi ba zaiso yaga ƙarshen faɗan nasu yaga wace zata haƙura ta barwa wata,
a harzuƙe fulani ta buɗi baki zata mayar mata da martani aka turo ƙofar daka tawa tayi batare da tayi maganar da tayi niyya ba,
bata kalli ƙofar ba tace maza kufitar min da wannan mahaukaciyar daga nan gurin ku fita da ita ku koya mata hankali,
shiru taji sunyi basu yi abun da tace musu ba,
jin hakan yasa ta dago dan tayi musu masifa sai kawai taga wayam basu bane ashe sam ne yashigo ita kuma duk atunanin sune,
idon sa akan dadda ko bai tamabaya ba yasan abun da yafaru dan haka bai tanka musu ba kawai ya wuce zai tafi part ɗinsa dadda tayi saurin cewa kasan de ku nake nema zaka wuce kamar baka taɓa gani na bama,
"kiyi haƙuri ina zuwa, kawai yace da ita sannan yayi gaba tunkan ya ƙarasa ma yaga shettima a tsaye na dariya tsayawa yayi yana kallon sa yace kai kuma me kakeyiwa dariya da hannun shettima ya nuna masa su dadda sannan yace ya akai zaka katse min kallon da name dama kabarsu wallahi faɗan nasu nishaɗan tar dani yake,
mtsw bakada aikin yine shiyasa kana kallon su suna faɗan amma ka kasa shiga tsakaninsu kadai san halin waccen rikitar tiyar tsohuwar yanzu sai tajamana abun da zamuyi danasani kafito mu wuce gidan su bossay yace muje ana neman mu wai yarinyar nan tana gidan,
"habadai wacce yarinyar kake nufi kuma,
sameer yace yarinyar da muke nema mana shiyasa yanzu ai hankalina bai tashiba dana ga matar nan agurin nan dan haka tun kan su kacame azo asamu wata matasalar kazo mubar gidan arabu da ita lafiya dan ko gurin momma bazamu komaba mu wuce canɗin kawai daganan,
"to wai dan Allah taya ta koma abun da yaban mamaki wannan wane irin juye juye ne ansace ta awani waje anga alamar ta acikin gidan nan yanzu kuma ace anganta acan wannan lamarin fa ni yafara bani tsoro wallahi,
kadai zo muje kawai nima bansan ya akai hakan ta faruba sai muje zamuji,
"Ok to muje, atare suka juya suka ƙarasa wajen su Fulani da suka cigaba da cece kucen su irin nasu na manya,
suna zuwa sam bai saurare suba kawai yaja hannun dadda tana ƙwace tana cewa yasake ta sai ta koyawa fulani hankali itama fulani tana cewa wai a ina yasamo wannan mahaukaciyar matar yasake ta kar yasake tafita da ita daga cikin gidannan sai tasa an ɗaure mata ita,
kowacce dai da kalar maganar da take amma yaƙi sauraron ko waccen su yacigaba da tafiya da ƙyar dai aka samu aka raba su suna fita shettima yajawo ƙofar ya rufe fulani aciki sannan suka wuce suna zuwa suka danna dadda a mota suka rufe suma suka shiga sannan sameer yatayar da motar da gudun gaske yabar masarautar dadda sai surfa masa masifa take yayi mata bazan yace gaba da tuƙin sa ya ɗauki hanyar gidan su bossay........✍️✍️
💖NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER'S💖
*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
👇👇👇👇
*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
by(ster lady)
*2,GIDAN AUNTY*
by(mss lee)
*3,SARKI SAMEER*
by(xeemat....love)
*4, JINI DAYA*
by(mrs bbk)
*5,YA FITA ZAKKA*
by(mum Sayyid)
*6,BABY
by(mhiz innocent)
[7/12, 9:47 PM] #momyn twins#: ❤XEEMAT___LOVE❤
💅SARKI SAMEER...💅
(wasa farin girki)
💖*the talent troupe writer's*💖
*Book 2*
*sarki sameer book two na kudine kabiya ka karanta cikin salama kar ka karantan littafi idan baka biyani hakkina ba dari biyu ne 200 bantsawwalaba, ga mai bukata ga account number 8124226526 AZIMA AMINU DAHIRU opay bank sai kuturo da shaidar biyan ta nan 08124226526*
🅿️ 87
✨الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر✨✨
✨بسملله الراحمن الرحيم✨✨
Bismilah............✍️
*Ina masoyan dadda wannan page ɗin nakune*💃💃💃💃
______*Dadda*______
"tunda suka fara tafiya dadda take surfa musu bala'i kamar su sukayi mata laifin sunyi mata magana tayi shiru sun bata haƙuri amma duk da haka da haka taƙi sauraron su....,
Sameer da yagade abun nata bana ƙare bane da yaga ta damesa taƙi yin shiru sai kawai yafara yawo da motar kamar zai bugata da wani abun suyi accident aikwa tana ganin haka ta sakar musu ihu tana cewa kashe mu kake so kayi nashiga uku na yaron nan anya kana da hankali yace bani dashi ai shiyasa zan nuna miki rashin hankalin wallahi idan bakiyi mana shiru da bakin kiba sai buga motar nan da abu kin mutu daman kece abaya kuma idan na bugata ke zaki mutu bamu ba,
"wallahi bazan shiruba da bakin ka nake maganar,
jin hakan yasa yaƙara jan motar da ƙarfi sannan ya taka burkin da ƙarfi,
talau talau tayi zata faɗa gaba sai kuma tadawo da baya atake ƴaƴan hanjin ta suka motsa saida taji kamar zasu fito saboda tsabar tsurewa da tayi saida hawaye suka ta rar mata atake kwa tayi tsit kamar babu ita amotar,
atare suka juyo shida shettima suna kallon ganin yanda ta koma yasa suka saka mata dariya taƙaici da haushi yama hanata magana amma ita kaɗai take raya abun da zatayi musu ta rama wannan rashin mutuncin da sukayi mata tunda take babu wanda ya taɓa sata gaba yayi mata haka waccen akuyar ta gama ɓata mara rai shine suma yanzu suka zo suka ɗora akai,
sam yace "akaro na farko da yafara kiran sunan ta yace "hajiya dadda yadai bakin ya mutune ko kuma inƙara kashe shi da mota,
banza tayi dashi tare da galla masa wata uwar harara kamar idonta zai faɗo,
"Au bazakiyi magana ba kuma harda hararata to bari inƙara suma idanun in kashe su yana faɗar haka yaƙara sakin murmushin mugun ta sannan
ya juya ya tayar da motar yana shirin fara tafiya dadda datagade yaron da gaske bashida hankali kuma inbata dakatar dashi ba sai yaƙara yi mata itakuma ahalin yanzu ai bazata taɓa son ta ƙara jin abun da yayi mataba yanzu dan tasan tsaf zata iya rasa ranta idan yaƙara dan haka sai ta sauke makaman yaƙin ta tayi saurin cewa wallahi ya mutu bazan ƙara yin magana ba na rantse muku da sarkin gidan ku🤣
sosai sukayi mata dariya tare da kallon ta shettima yace "daman haka kike da tsoro yau naga logonki hajiya dadda,
Sam ya ɗora dacewa "daman tun can bata samu daidan ta bane nidaman bata taɓa shigowa hannu na bane da tuni na daɗe da saita wallahi duk iskancin nan nata tana sane take yinsu,
Allah sarki dadda yaudai da gaske bakin nata ya mutu dan bata da halin magana shiru tayi duk abun da suke mata bata tanka musu ba dan har ga Allah yauɗinnan ba ƙaramin tsorata tayi ba dan haka ta siyawa kanta zaman lafiya tasawa bakin ta saƙata,
sukuma sukaci gaba da tafiya suna ƙara yimata abun da suka ga dama suna mata dariya yau sun samu dama.....,
***************************
"kallo fa yakoma kan dady kowa shi ya zubawa ido yana jiran yaji me zaice amma yaƙi magana saidai kuma kallo ɗaya zakai masa kagane tsantsar tashin hankalin da yake ciki kana ganin sa kasan baida gaskiya.........,
"muna sauraron ka maama ta ƙara yima sa magana,
da ƙyar dady ya iya ɗaga kai yakalle ta sai kuma yayi saurin ɗauke kansa ganin yanda fa kafesa da ido,
yakai wajen 15 minutes bai iya cewa komai ba saida meer yaƙara gargaɗin sa sannan murya ƙasa ƙasa yace da farko dai ina mai baku haƙuri gaba ɗagan ku laifine na riga na aikatashi tunda daɗewa kuma har yanzu abun bai bar raina ba nayi da nasani nayi nadamar abun da na aikata saboda nima ba ason raina hakan tafaru ba dole akayi min kuma abun da ya daɗe yana min yawo akai bansan mutumin ba, ranar da bun ya faru ina cikin tafiya amotar wani uban gidana saboda aloƙa ci banda aikin yi...
ina cikin tafiya ta sai nayi parking ɗinta abakin hanya zan siyo ruwan sanyi awani shago bayan naje nasiyo ne nadawo na shiga motar na tayar naci gaba da tafiya na ɗanyi nisa kenan sai kawai naji an ɗora min wuƙa a wuya ba ƙaramin tsorata nayi ba dan saura kaɗan inje indaki wata motar Allah ya kiyaye nayi saurin taka burki ina shirin juyawa inga waye sai yace idan kajuyo sai caka maka wuƙar nan,
nandai nakasa juyowa daman sai aloƙacin na kula ashe ya juyar da mirror ɗin gaban motar bare in kallesa ta ciki..,
haƙuri nashiga bashi ina cewa me nayi mishi me yake nema awajena,
sai yace intayar da motar duk inda yace min inyi ban Musa masa ba saboda ina son raina dan na lura idan nayi mishi taurin kai zai iya buga min wuƙar nan,
haka na tayar da motar yana kwatan tamin duk hanyar da ya nuna ita muke bi muna miƙe wani layi yace dani kaga waccen matar dake tsaye nace eh yace to ita nakeso kabi ta kanta da motar nan,
ba ƙara min tsorata nayi ba dajin furucin sa cike da fargaba nace dan Allah kayi haƙuri bazan iyaba idan nakashe tafa shikenan nayi kisan kai kuma nasan hukuncin me kisa awajen ubangiji nidai bazan iyaba kayi haƙuri ka barni intafi,
sai kawai gasaka min dariya yace ai tunda ya shigo motar nan sai nayi abun da yasani nidai ban mara cemasa komaiba kuma ban tsaya da tafiyar ba muna daf da ita sai naga ta matsa ina shirin incigaba da tafiya batare da na ƙara bi ta kantaba, amma ban ankaraba wannan mutumin kawai yasaka hannun ya juyar da sttiring ɗin motar kan ta tabugeta atake kwa tafaɗi a wajen sai nayi saurin taka burki na buɗe motar nafito nayi kanta atakaicedai mutumin nan dana koma