Sarki Sameer 2 Wasa Farin Girki By Yaya Azeema

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   20 / 74

57K to 60K   out of 221K words

gobe ba makaranta sai ku zauna kinga kema sai tasaka naki gobe ba shikenan anraba ba,
sakin fuskarta tayi harda dan murmushin ta tace to shikenan momma dama abarta muyi weekend dinnan tare wallahi naji dadin haduwa da ita,
momma tace to saidai yayan naku yadawo sai ku tambashi da kanku ko ku tambayi yayanta danagansu tare kuma sunce tare zasu dawo cike da murna gaba ɗayan su suka hada baki wajen cewa Allah yasa abarta momma, tace Ameen,
"bayan Ameesha tagama saka kayan sai momma ta tura su suka fita daga dakin zuwa falon dan cin lunch,
agurin cin abincin ma saida suka kusa fada sude fada baya musu wuya komai ma nafadane haka ake fama dasu Hamra son girma da kuma tsokana ita kuma Amra rashin hakuri da indai tai mata sai ta rama ta wani bangaren Amra tafi hakuri kuma tafiya sauqin kai da saurin fahimtar abu saboda ita sai ka tabota kuma akwai yawan wasa dan ita sai taimaka magana wanjen goma amma bata gaskiya aciki kawai tayine awasa kuma koda kayi mata laifin da yabata mata rai to data rama anwuce wajen zata manta dashi saɓanin hamra da ita bata san wasa ba gashi wataran ita zata fara tsokanarta da fadan amma kuma ita idan tayi mata sainata ran yabaci ga riqo akwaita da riqo indai kayi mata abu ko bata ramaba to yana nan aranta dan badan Amra bata biye mata da tuni sunfara 'yar gaba saboda abu kadan yahadasu sai tafara daina mata magana itakuma Amra sai ta kurata to bayanda zatayi dole ta sauko shiyasa suke yawan samun saɓani saboda halinsu baizo ɗaya ba kuma kowa bazai barwa kowa ba idan rigimar ta tashi ahakama dan anayawan tsawatar musu akan kuma hana fadan dokeke acikin gidan shiyasa komai zasuyi iyakacin su na fatar baki,

    "Bayan sundaidai ta parking agaban gidan prison din suka fito gaba dayan su tare da nufa ciki bayan sun shiga suka sanar da wanda sukazo nema akayi musu iso har zuwa office dinsa suka shiga su suka bayan sun suke qara sanar dashi daga inda suke da kuma abun da yakawo su duk da yariga da yasani amma saida suka qara yimasa bayani,

ba bata lokaci yafara yi musu nasa bayanin,

  kamar yanda nagayawa mahaifin ka gaskiya lokacin da abun yafaru banine anan ba saida yanzu zamuje daku kuduba ko ina idan kun ganshi to sai afara binciken inda file dinsa yake inyaso ku kuma sai shigar da qarar,
sam yace idan kuma ba anganshiba kana nufin baza mugansa ba shikenan ko ko me kake nufi,
da mamakin maganar mutumin yake kallon sa ganin shi ko ajikinsa maganar da yayi tunawa da ko shi waye sai kawai ya kawar da mamakin sa, yadanyi murmushi sannan yace bawai haka nake nufi ba ai ganin nasane zaifi sawa mugano bayanen sa da wuri amma idan baya nan kaga abun zai bamu wahalar gano inda yake kamar yanda kukayi min bayanin cewa tun alokacin bayan an hamada haduwa da kowa kaga kwa mai yiyuwa ne ace suncanza masa guri tunda har basa so azo wajen sa,
yanzude abudaya zamuyi muje afara bincikawar idan babu shi zanduba cikin sunayen da suka yi aiki anan inayaso sai muduba na shekarar da yayi aiki anan koda yanzu baya nan sai muneme shi ko ya kace nidai inaganin wannan ce hanyar da Yakamata mubi dan inada tabbaci kaf cikin gurin nan ma baifi kasamu mutum biyarba waɗanda suna nan tunwancen lokacin har zuwa yanzu wasu dayawa sunbar nan wasu anyi musu transfer wasu kuma sunyi ritaya tunda gaskiya andade,

shiru yayi yana kallon su danjin bun da zasuce game da bayanin da yayi musu, Shiru sukayi gaba dayansu saida ga bisani Shettima yace hakan yayi dole abi ta wannan hanyar yanzu kamata yayi aje aduba din gashi ma kuma matar tagaya masa inda dakin yake kaga shiga kawai zamuyi inba ya nan sai ko tambayane muyi dan nima bana tunanin zasu barsa anan haryanzu,
sam ne yaja dogon numfashi tare da furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya miƙe yana zagaya office din tare da saqale hannun sa abayan sa batare da yace komai ba saida yayi yan mintina sannan ya juyo yana kallon sa da shima shi yake kallo aransa yana mamakinsa,

ba dubawar da zamuyi yanzu abun da za ayi shine kawai ka dauko mana record din naku aduba sunan mutumin da yakarbi case din ta kansa zamu fara ai bama yacikin prison dinan dole sunfita dashi mutumin zamu fara nema kafin muyi komai shizamu fara kamawa zai fadi inda yakaishi kafin ya sauka,

shiru mutumin yayi yana nazarin maganar sa kafin yace masa gaskiya yanzu baida alhakin da zai iya basu wani abun dole shima sai yayi magana da manyan sa kafin yabasu
Shettima yace kamar nanda yaushe zakai magana da sudin yace musu subashi nan da gobe ma sai sudawo,
nande ba wanda yaqara cewa komai banda kallo da sam ke binsa dashi babu abun da yake wanda kallon nasa har saida yasa mutumin yadan fara tsarguwa da kallon da irin kallon da yake masa,
baide kulasaba har suka miqe tsaye su shettima sukayi masa godiya sannan suka fita daga ofishin,

yana ganin fitar su hannun sa har rawa yake wajen saurin dauko wayar sa yadannawa wata number kira ana daga ya sheqe da dariya sannan yace ka kwantar da hankalin ka har na tsarasu sunma tafi yanzu haka ma inajin sun shiga mota nace gobe su dawo nikuma kafin goben baza su qara ganina ba duk sanda sukazo zance musu bana nan mahaifin nasama zanyi blocking din number sa ta yanda bazai qara samu naba duk wata hanya da zata hadamu dasu Bazan bari su ganni ba bare hartakai ga na basu sunanka daga can bangaren aka bashi amsa da cewa yauwa aikin ka na kyau zansa aqara maka salary wannan watan zaka samu kaso me tsoka kaide Kaci gaba da abun da nasaka inbahaka ba kuma kasan halina koda wasa karka kuskura kagaya musu inda nake kajini yana washe baki yace angama baza sutaba sani ai kasanni da iya aiki daga cen mutumin yace ai saboda haka na ɗoraka akai nasan zaka iya fiye da hakama jin anyabeshi yasa shi qara washe baki yana yimasa godiya daga nan sukayi sallama ajiye wayar sa kenan yamaida kansa jikin kujera yanajin dadin qarin kudin da za ayi masa,
kawai yaji anturo qofa kallon qofar yayi dan ganin me shigowa zunbur yayi ya miqe yana binsa da kallo baigama kallon sa saiga sauran nan sun shigo suma wani qarin abu yahadiye da ya tsaya masa amaqogaro da tunanin me kuma yadawo dasu bayan sun tafi karde ace sunji maganar da yayi wata zuciyar tace taya za ayi sujika bayan qofar arufe take kuma na waje bai isa yaji na ciki ba sauke ajiyar zuciya yayi duk alokaci guda yayi wannan tunanin tare da dan basarwa harda qaqaro murmushin dole tare da cewa a'a kundawo ku kunyi matuqa ne yafada yana qara binsu da kallo tare da komawa kan kujerar yayi zamansa hankalin sa kwance,

Shettima mane yace eh munyi mantuwa abun da muka manta shine baka fada mana sunan wanda ya sauka ba kafin ka hau tunda dole daga shi saikai kaga dole zakasan sunan shi,
wanidan qayataccen murmushi yasaki tare da cewa taya zanyi insani dana sani ai da tun dazu nagaya muku ai shiyasa nace kubari sai zuwa gobe sannan na binciko ko waye,

wani irin kallo sam ya wulla masa da yasa shi yin shiru takawa yayi har inda yake yana kallon sa da kyau kafa yaɗaga ya dora akan tebur din nasa sannan yazuba masa idanun sa sannan yace kace me banjiba sai ka maimaita shiru mutumin yayi bai tanka masaba sauke qafar yayi ya daki teburin da qarfi tare da buga masa tsawa yace maimaita nace mu zaka gayawa maganar banza suwaye manyan naka tsuru yayi yakasa magana yana faman rarraba lokaci guda wata zufa ta fara tsatstsafo masa
dan matasawa yayi daga kusa dashi yaje inda ya tashi dazu wani abu yadaga sai ga qaramar waya agun zarota yayi yana nuna masa yadannan ta haske yakawo, ajiye masa ita yayi agabansa da kallo yabi wayar tare da miqewa tsaye yana zazzara idanu tare da kafe wayar da ido alamar kira yagani ajiki kuma kiran na tafiya sam ne yadanna wayar yasata a hands-free tare da dago tasa wayar itama yasaka ta a hands-free sannan ya karamasa ita akunne yace kagane ko har yanzu kana buqatar bayani?
Bossay ne yace ah in baigane ba ai sai ayi masa bayani yanda zaifi ganewa yana fada ya matso kuda shi tare da kifa masa wani gigitaccen mari baigama tantancewa ba yaqara bashi ta dayan barin yace yanzu kagane,
Adade baigane ba amma yanzu da aka mareshi kuma yaji duk muryoyin su acikin wayoyin yagane cewa sun ajiye masa waya tare da connecting din kira atakaicedai sunji wayar da yayi shiyasa suka dawo,
tsoro da furgici duk alokaci daya suka riskesa tunda yadafe kumatunsa baqara yarda ya dago ba gudun kar yaji wani ammafa aransa yana ayyana duk abunsu saidai suyi sugama amma bazai taba gaya musu ba duk abun da zasuyi mishi saidai suyi surabu dashi inkuma suka nemi suyi mishi hauka yanzu yasa akamasu adaure su agun,

bazato ba tsammani yaji wani irin duka ta tsakiyar kansa kamar an doka masa guduma da sauri yajuyo yana kallon sam da ya hade rai idonsa har sun fara canza kala cikin daga murya yace ya sunan shi kuma a ina zamu sameshi waye shi yafada yana tsatstsare sa da ido shiru ba amsa tsawa ya kuma daka masa yace waye shi zaka fada ko sai aikaka inda ba adawowa yafada tare da kaimasa shaqa kif kif yafara da ido shima cikin fakiya da daga murya yace bazan fada ba kuma kasake ni kasan matsayina anan gurin wallahi idan bakuyi wasaba duk sai nasa an kulle ku inga uban da zai kunceku kasakeni nace yaqarasa shima da yimasa tsawa yana rufe bakin sa ya kwasheshi da marin da saida yaga haske ya gifta cikin bacin rai yace kasaka inka isa nikuma sai nasa an qulle duka dangin ku ba kai kadai bama kaiwaye da har ka isa kayi min tsawa ko uwata bata min tsawa sai kai nace sai kai yaqara kai mishi naushi a kumatu na take bakin yafashe,

Amma duk da haka bakin bai mutu ba yaqara cewa kodan waye angaya maka dan babanka yana lauya zanji tsoron kane ko shi bafi qarfin in kulle shiba kuma bai isa yasa akulle niba ko akoreni daga aiki shi asuwa wallahi matsayin sa baikai nan ba yafada yana qoqarin fusge hannun sa daga riqon da yayi masa amma yakasa saboda ba qaramin riqo yayi masaba,
jin hakan yasa sam bayar da wayar kawai yahaushi da duka ta ko ina bossay ma ba abarsa abayaba haka yazo suka tarar masa suna duka suna dukansa suna yafadi gaskiya amma yace saidai su kasheshi amma bazai taba fada musu ba,
saida suka gaji dan kansu suka ga daku iya dakuwa yafita hayyacinsa dan har numafashin sama yafara daukewa sannan suka rabu dashi shettima yace tunda bazai fada ba kawai su tafi da wayar inyaso sai suje sucire sim din su duba number da yayi waya da ita last,
karkada masa kai sameer yayi sannan yace masa ai bazamu rabudashi ba mukai sa mota mutafi dashi duk sanda yagajida azabar da ake masa yafada kallon sa shettima yayi sannan yace kana ganin zasu barmu mufita dashi ahaka ai dole sai suntambayi ba'asi karmuje kuma suyi mana wani abun ma idan sukaga halin da yake ciki nide ina ganin kawai murabu da shi anan inyaso sai mudawo gobe sam kallon baka da hankali yayi masa sannan yace bakaji me yace bane bazai qara bari muhaduba kana ganin yanzu inmuka rabu dashi zamu qara kamasa ne bare kuma idan wancen yaji labarin munsan wannan qarya yake ai dole su qara canza wani daban kawai bets solution shine mutafi dashi inyaso sai mugano inda wancen yake takan wayar nan yafada yana nuna wayar hannun sa,
Shiru shettima yayi yana tunanin ta yanda za suyi sufita dashi daga gurin nan batare da kowa ya gansuba dan nufasawa yayi sannan yace kai yanzu to wacce shawarar ka yanke taya kake ganin zamu fita dashi batare da kowa yagani ba,

bai basa amsaba kawai suka ga yanufi hanyar fita saida yakai bakin qofa sannan yace musu kujirani ina zuwa bayan fitarsa da kamar minti hudu yadawo hannun sa roqi da wata baqar leda ajiyeta yayi agabansu sannan yadauki audiga ya gogewa wancen jinin da yadan bata masa fuska sannan wani abu aroba me kamar turare sai ya fesa masa shi afuska sannan ya zaro face mask yasaka masa sannan ya miqe yace ku kamo sa yatashi tsaye haka suka tasheshi tsaye kuma yatsaya da qafarsa idonsa abude yake amma kuma babu abun da yakeji kawaidai asama sama yakejin sa baisan ko shi waye ba komai zaiyi komai yakeyi shi mutum ne ko aljani oho,
Sam yace kusake shi zai iya zuwa da kansa kawai mubi bayansa kafin nan da minti biyu mu isa cikin mota in bahakaba kuma zai iya faduwa ahanya muyi sauri lokacin mu na tafiya dan tattare furin sukayi yanda baza agane anyi wani abuba sannan suka dauko wayar sa tare da kashe komai na office din na wuta sannan suka fita suka jawo office din tare da saka masa key suka cire key din suka tafi dashi,

suna fitowa mutanen dake waje suka fara binsu da kallo daya daga cikin su yace yallabai jiranka fa ake tundazu naga kuma zaka fita bossay ne yayi saurin bashi amsa dacewa yanzu zai dawo ba fita zaiyi ba ok dayan yace kawai dan baidamu da rashin amsawar yallabai din ba saboda baikawo komai aransaba tunda duk wanda yagan sa ba wanda zaice bashi bane ko kuma da abun da yake damunsa baya cikin hayyacin sa tunda ga fuskarsa nml idon sa abude gashi yana tafiya da qafarsa suna tafiya sam yana duba lokaci ahankali yace saura 59 second muyi sauri dan dudubawa sukayi suga ko ba mutane da sai suriqe hannun sa sujashi yanda zasu fiyin sauri amma suna juyawa sai suka ga idon yawancin mutanen akansu kamar ansan basu da gaskia,

"wanine ya taho aguje yana cewa yallabai yallabai gashi ance inkawo maka wani file ne a hannun sa yana daf da cimmasu bossay yaqarayin saurin shan gabansa murya qasa qasa yace kai baka san meke faruwa ba ko da dan mamaki saurayin yake kallon sa sannan yace meke faruwa a ina kuma bossay yace kai yanzu tsakanin ka da Allah baka sani ba kode wasa. Kake min yace kamar ya wasa nataho zan basa saqo kuma ka tsareni kana cemin bansan abun dake faruwa ba to kagaya min me yake faruwa ni banji ance komai yafaruba ni matsamin kaga har yakusan kaiwa waje banaso yafita baisa hannnun ba qara shan gabansa yayi yace kai wallahi da akwai abun dake faruwa acikin nan gidan amma nayi mamaki dabaka sani ba to ni ya akai nasani mtsw dayan yaja tsaki yace nibansani kai nifa banma sanka anan ba kuma taya har zakafini sanin abun dake faruwa anan kasan kwa muqamina agidan nan bossay yace kai nima fa ma aikacine anan jiya nafara zuwa shiyasa baka sanni ba amma daga zuwana ni na gane abubuwa da yawa amma nayi mamaki da kai baka gane ba amma de bari indawo kajirani zangaya maka abundake faruwa kaima nasan sai kayi mamaki yanakaiwa nan yayi gaba da dan saurinsa ganin har sun fita daga gate din yana tafiya yana dariyar abun da yayiwa wannan kwata kwat zacen dayake masa bakai ba gindi amma wancen baigane hakan ba kuma yatsaya yabiye masa lalle sokone bashida wayo ahaka shima yafita daga gate din yana fita yaga suna kiciniyar shigar dashi mota saboda suna fitowa daidai minti biyu na cika abun kwa da aka fesamasa yafara aiki take yazube musu awajen Allah ma yasosu babu mutane awajen qaraswa yayi gurin su shima yaci gaba da taimaka musu suka shigar dashi da kyar saboda mutumin akwai dan jiki ba laifi bayan sun sakashi aciki sai sam yace shettima yashiga inda mutumin yake shikuma bossay ya shiga gaba shi kuma zaiyi tuqin gaba dayansu da mamaki suke kallon sa wai zaiyi tuqi da kansa musammanma shettima da shide tunda suke baifi ya qirga saunawa yataba yin tuqiba shima kuma tun loakcin yarintar su,
babata lokaci bossay yashiga inda yace masa din shi kuma ya shiga driver seat yazauna tare da tayar da motar suna tayarwa saiga wannan saurayin ya qaraso wajen da gudun sa yataho yanaso ya tsayar dasu amma ina tuni sam yaja motar a 360 suka bar wajen tare da badeshi da qura suka qara gaba kwafa yayi yace amma yallabai bai kyauta min ba ina tayi masa magana amma yaki kulani daman ance bashida mutunci akwai wulakanta mutane amma shi baitaba yarda ba sai yau kwafa yayi cike da taqaici ya juya yakoma ciki yana tafaman mita dan har ga Allah baiji dadin abun da yayi masa ba,
da gudu yake jan motar kamar zasu tashi sama shettima de da yaga yakasa hakuri saida yayi magana yace dan Allah kabimu ahankali gudun yayi yawa gashi kuma nidai baganin ka nake kanajan mota ba bare ince ka kware gaskiya kabimu ahankali,
Banza yayi dashi saima qara qure giya dayayi dan kamar zigashi yayi haka yaje jan motar ga mugun overtaking din da yajeyi yanda bashi da hakuri a zahira haka atuqima bashi da hakuri baya dagawa mota qafa saidai ita ta daga masa haka yaje tayi akan titin wani wajen ma inyazo ya wuce sai anzageshi saboda irin gudun da yakeyi Allah nedai yakarsu babu abun da yasane su har suka qaraso wani dan qaramin gida sannan yayi parking awaje sannan yace wa bossay je kabude mana gate din budewa yayi ya sauka sannan yaje yabude musu shikuma yaja motar zuwa cikin gidan bossay ya mayar ya rufe sannan yabi bayansu,

har gaban qofar da zata shigar dasu yakai motar sannan ya kashe ya fito lokacin bossay har ya qaraso gurin haduwa suka qara yi suka kamashi suka shiga dashi ciki,falo ne empty babu

20 / 74