Sarki Sameer 2 Wasa Farin Girki By Yaya Azeema

Author :  Ayshacool Category :  Love

Chapter   1 / 74

1 to 3K   out of 221K words

[4/25, 11:05 PM] #momyn twins#:            ❤XEEMAT___LOVE❤
                  
💅SARKI SAMEER...💅
               (wasa farin girki)
 
          *BOOK 2*
*FREE PAGE*
     
       Barkan mu da dawowa dafatan kowa yayi salla lafiya Allah ya karbi idabadin mu Kamar yanda nayi alqawari 25 April zan cigaba to gashi na cika Allah yasa yanda nagama book 1 lafiya Allah yabani ikon kammala wannan ma kuskuren da zanyi kuma Allah ya yafe mana baki daya Ameen🙏

    Gargadi da jan kunne littafin sarki sameer na biyu na kudine nayi na Allah nayi na annabi a book 1 duk yawansa nagama batare da wani yabiyani ko sisin kwaboba amma yanzu zaku biyani dan haka dan Allah dan Annabi  duk wanda yasan be biya na biyu ba pls karka karantan littafi idan kinsan baki biyani hakkina ba, idan kika karanta kuma baki biya ke da Allah mahadu acan sannan kuma duk wanda yabiya yakaran ta kar yafitar min da littafi ga wanda be biyaba  pls kabarshi a inda ka karanta duk me buqata shima yabiya kudin dana saka ba mai yawa bane bare wani yace yayi masa tsada bazai iya biya ba saidai idan mutum baiga dama ba....

*Zakubiya dari biyu asaka ku a group normal group 200 spatial group 300 VIP group 500 iya kudinka iya sha'anin ka👌*ga account number nan👇👇

*yan Facebook*
Wandan da suke da qaramar waya ko kuma wadanda sunfiso su ringa karantawa a Facebook din to zan bude muku wani group din a Facebook iya wadanda suka biya zan sakasu aciki  nan da kwana uku in sha Allah zan fara posting sai ku hanzarta biya kar abarku abaya ,

Ga duk wanda ya shirya biya 👇
8124226526 AZIMA AMINU DAHIRU OPAY BANK duk wanda yabiya  sai yaturon da shaidar biya ta number ta 08124226526
Yan facebook kuma sai kuturon ta account dina na Facebook ina amfani da Azeema dahiru Aminu(xeemat)

                    🅿1&2

Bismillah...........✍

________________*DADDA*
da qyar nasamu wata qasan bishiya da ba wanda zai ganni anan nake kwana wajen kwana na biyu agurin ba ci ba sha damuwa babu wacce ban shiga ba ga Ameesha kullum cikin kuka take min dan 'yar madarar da nake batama ta kusa qarewa kadan kadan nake bata saboda idan ta qare bansan a inda zan samo mata wata ba daman ba ruwa take shaba ahaka mukayi rayuwa tsawon kwana biyu da wuni guda danaga de ina niyar halaka kaina sabida yunwar da nake ji ta gama kamani dan da qyar ma nake iya daga qafata nake tafiya idanuna kwa har rurrufewa suke yi saboda rashin bacci da yunwa haka nafito daga cikin dan dajin ga Ameesha  abayana sai kuka take min ahaka nazo bakin titi amma sai na dan rufe fuskata da gefen mayafina saboda kar aganeni......,
saida nayi tafiya me dan nisa ina laliban inda zan samu tuwan sha amma bansamu ba ahaka naci gaba da tafiya saiga wani me adaidaita shine na tsaidashi nace dan Allah yataimaka min banda kudi yadan saukeni a police station amma yaki saida na tsaida wajen guda biyar kafin nasamu wani ga tausaya min ya dauke ni ina zuwa tunda ga waje da naga fanfo naje nasha ruwa na sauke Ameesha itama nabata sannan nadanji dama dama sai na shiga ciki ina zuwa nasamu wani dan sanda yayi min iso wajen ogansu nande nagaya musu halin da ake ciki shikam yace besan zance daman ai angaya min ko mu biya kokuma yayi zaman gidan prison duk magiya da nayi mishi da roqon sa amma be saurareni ba da na bukaci a fito min ma dashi inason magana dashi sai yace bazan samu damar ganin sa ba naci gaba da roqonsa daga qarshe ma sai kawai yasa azo a fita dani daga office dinsa wasu yansanda mata suka zo suka jani sukakai ni waje sai na riqe daya daga cikin su nace dan Allah tabashi hakuri ya barni inganshi ina son magana dashi amma sai tace min inyi hakuri hakan bazai yiyu ba har ta juya zata tafi sai kuma tajuyo murya qasa qasa tace baiwar Allah bari ingaya miki gaskiya danki baya cikin nan gurin amma bar garin nan dashi tun safiyar jiya hankalin yatashi nace mata ina aka kaishi tace gaskiya bata sani ba amma tana tunani ko kano aka kaishi dan tadanji qishi qishin din maganar amma bata da tabbas amma inje can in gwada tambaya ko yana can nace  mata ai bansan ko ina ba acikin kanon hasalima bantaba zuwa ba tace idan naje intambaya inana gidan yari sabon budewa za anuna min nayi mata godiya sannan ta tafi tabarni awajen sai nafara tunanin yanzu ta ina zan fara neman kudin da zan tafi kano amma na rasa mafita a gurin nayi zama na naqi tafiya saboda nasan sai nafi tsira daga wajen wadan can mutanen baza suganni ba anan jaka ta najawo nashiga bicikewa kamar na ajiye kudi aciki sai dai bansamu ko biyarba daman nasan hakan zata faru sai nasake zuge bayan zip din akwa abun da ban taba tunani ba kenan  sai kawai naci karo da ATM din malam da yaban lokacin da zan fita tashin hankali yama sa na manta da shi kwata kwata aikwa da sauri na miqe daga gurin na fita waje duddubawa nashiga yi ko zan samu inda ake cirar kudi amma ban samu ba akusa saida nayi nisa sannan na hango wani wajen me pos  ina zuwa na mika mishi sai nace ya duba min yagani nawa ne aciki yana dubawa sai yace min dubu tamanin da da bakwai ne aciki sai nace mishi kawai yacirar min sha bakwan yaban nasaka pin nabashi ya cirar min sannan na karba nabashi charges din dari biyar sannan natafi inda zan samu abinci nafara nema sannan nasiya naci na koshi dan saida nasai na dari biyar sannan naji na qoshi da naji kwarin jikina sai naje nayowa Ameesha siyayya  nata kayan harda kayan sakawa da duk de abun da nasan zata bukaqata kafin muje saida na kashe mata wajen dubu biyar sannan na nufi hanyar tasha inda zan hau motar kano bansha wata wahala ba nasamu na shiga kuma ina shiga motar ta tashi muka dau hanyar kano mundau lokaci muna tafiya sai wajen magrib muka qarasa muna isa cikin garin kano saiga wata baqar mota ta sha gabanmu inaganin haka gabana yafadi ina addu'ar Allah yasade ba yan fashi bane kar su kwace min kudade buga motar akai da da qarfi sai drivern ya bude yafita yana tambayar ko lafiya me suke so sai daya yace zamu dau wata mata ka bude mana ina jin hakan kuma najiyo muryar mutanen nanne nayi mamakin jin yanda suka biyo ni kota ya akayi suka san na taho waya ce musu ina hanyar kano da sauri nayi qasan kujera sannan nace wa matan gefena dan Allah sudan rufeni kar subari wadan can mutanen suganni ni suke nema kuma wallahi mugayene kasheni zasuyi sutaimakamin ,
suka ce to "
ina jinsu drivern yace ya sunanta kuma meyasa kuke neman ta wani yace ina ruwanka ka bude mana kar muhada dakai driver ya bude musu yace gashinan dayane ya shiga ya lalleqa sai yafito yacewa sauran banganta bafa sai yace kade qara dubawa dole tana ciki tunda ta tabbatar mana da ta taho kuma taga motar da tashiga dan haka ka duba ko kuma kowa yafito daga cikin motar muduba idan mungama sa koma dan nasan tana ciki ba inda faje jin maganar da sukeyi ba qaramin faduwa gabana yayi ba shine yau tawa ta qare bani da wata hanyar guduwa ina cikin wannan tunanin sai wata mata tace kitashi ki shirya zan taimaka miki ki gudu kitsaya abayana ina fita zan fada kansu zan nannade mishi fuska da mayafi na ke kuma sai ki gudu kafin su ankare dake dannasan idan nayi haka zan ja hankalinsu gaba daya naji dadin taimakon da tace zata min dan haka sai natashi nagyarawa Ameesha goyo Allah yataimakeni ma tunda nabata madara tasha da maganin murar da nasiya mata saboda naji hancinta yafara toshewa tunda ta kwanta bacci kuma har lokacin bata farka ba,
gyara mayafina nayi naqara rufe fuskata sai na cire ATM din dake cikin jakata da kudaden duk de abun da nasan me amfanine na cire nasaka acikin aljihun bujejen wandon da nasaka ta ciki saboda acikin motar zan bar jakar takalma nama aciki na barsu nade shirya gudu sosai mutane nata fita har akazo kanmu matar tace kimde shirya ko nace mata eh kamar ynada tafada kuwa hakan mukayi tana fita tayi kansa nikuma da farko banyi gudu ba sai nabi a hankaki na fita ba wanda ya lura dani har nafara gudu inajin su kuwa sauran sukayi kan matar sunayi mata magana wasu ma sun dauka itace matar da ake nema saidai bayi nisa ba naji wani daga cikin su kai ai kunganta can zata gudu ai dayan ma basubi takan matar ba gaba dayansu suka biyo bayana,

inajin haka na kunce goyon bayana kawai na jefar da zanin a wajen nacigaba da gudu ni kaina bansan inda nake saka qafata ba kawai gudu nake suna bina abaya wata kwana nayi sai nasamu wani lungu na buya suna zuwa kuwa sukai ta nemana amma basu ganni ba sai suka wuce kawai sai da na bari sukayi nisa sannan ni kuma nafito sai na canza hanya nabi wani titi nacigaba da gudu bansan inda naked dosaba ina cikin wannan gudun ne wannan baiwar Allahn ta cece ni tafada tare da nuna Ammi da hannu (shine asalin haduwar ga da Ammi na farko anan suka san juna )

bayan na dan kwana biyu sai nayi tunanin gwara inbar gidan saboda zuwa lokacin nadena yarda da kowa tunda ko basu fadan ba dukkan alamu sun nuna yar sandar nan da tace intaho kano itace tagaya musu inda nake alhalin kuma itace tace intafi amma kuma daga baya ta ci amanata shiyasa nake ganin duk inda ma naje duk bakin su daya ba wanda zai taimakeni saboda Allah,
bayan barina gidan bansan inda zan dosa ba sai kawai na nufi kasuwa sai na tambaya inda sabon prison din yake sai aka kwatan ta min amma da naje sai akace ba wanda aka kawo haka naqara dawowa jiki babu kwari har zuwa dare bansamu mafita ba ina tavgarari a bakin hanya aranar de a wani harabar masallaci muka kwana ina ta barci har mai ma sallacin yashigo bansani ba saida yatashi ni yace baiwar Allah lafiya kuwa kika kwanta anan adan takaice de nabashi labarin nace masa wasune suke bina zasu kasheni gashi sunkashe min mijina shiyasa na gudo nazo nan na kwanta kaji dalilin kwanan nawa agun shine ya taimaka min ya nuna gidan sa yace inje idan an idar da sallah zai shigo incewa mutanen gidan shi ya aikoni dana shiga ba kowa haka naita yin sallama amma ba wanda ya amsa sai kawai nasamu waje daga gefe na tsaya ina jiran shigowar sa ina gurin ba wanda ya fito har aka idar da sallar ya shigo yaganni awajen ya metasa na tsaya nace nayi sallama ba amsa ba yace to shikenan muje ciko yana tafiya ina binshi abaya muka shiga wani daki wata mata na salla saida ta idar sannan yace uwani ga bakuwa tazo tana ta sallama baku amsaba tace bakuwa kuma da asuba daga ina nande shima yayi mata bayani amma fuskarta ba walwala tace to barkan ta da zuwa ga guri ta zauna ta nuna bakin gado sai mutumin yace baiwar Allah ki ajiye yar sai kiyi salla kafin da gari ya qarasa wayewa ko nace masa to sannan na ajiye yarinyar ya nuna min inda bandaki yake naje yi alwala na fito bayan nayi idar na gaisar da matar amma sai naji ta masa min ciki ciki tunda ga nan nagane cewa matar bata son zamana dan haka nayi alkawarin gari nayin haske zanbar gidan zama nayi adakin saboda zuwa lokacin mutumin har ya fita daga dakin ina gurin har gari yayi haske ina shirin  fita kenan saigashi ya shigo dakin ganina a tsaye yace ina zani nace masa zan tafi ne yaca a'a ba inda zani idan na tafi ina zani bayan ba wanda nasani nace masa yayi hakuri yabarni intafi yace a'a saboda banason mitayin jayayya sai kawai nace masa to zan zauna zuwa gobe kafin insan yanda zanyi yace to haka na koma na zauna shiru kamar ni kadaice adakin danko inda nake ma matar bata sake kallaba kamar ma batasan da zamana acikin dakin ba,
inda nayi sallah na kwanta agun dan bacci nake ji wanda nayi be ishe niba ina kwanciya kuwa bacci yadauke ni,
kukan Ameesha ne yatasheni ina tashi naga tana tafaman kuka amma matar nan tana kallon ta bata dauke ta ba kuma bata tasheni ba haka natashi nadauke ta na rarrasheta nabata madara tasha saidaga baya na lura da kwanon abinci agefena saida nagama bata sannan nasamu tayi shiru nikuma daman yunwa nake ji dan haka kawai nahau cin abincin da nagama kawai sai ban kulata ba  nafitowata mutanen da nagani na shiga gaisarwa duk suka amsa amma suma mata daya ce naga fuskarta a sake dayar kuma ko amsawa ma batayi ba dayace tazo kusa dani ta karbi Ameesha dake hannu na tace kintashi ai malam yace muzo mu gaisa sai muka tarar kina bacci sai lokacin na danji dadi danaga ita ba irinsu bace dan haka kawai nima nasake da ita muka dan yi hira na lurama kamar adakinta yake ita take aikin dan haka na taya ta adan kan qanen lokaci muka saba da ita sauran kuma ba waccce na qara bi takanta tunda sun nuna basa sona nima sai nafita daga harkarsu sai da muka gama komai sai nace mata dan Allah taimako nake nema inason inkama gida dan madaidai ci ba me tsada ba sai inzauna tace bazan zauna anan ba nace mata eh nafison in zauna nikadai zama agidan wasu be kamace niba da girmana tace to shikenan bari zatayiwa malam magana idan yadawo sai aduba nace to shikenan shiru de inajira inga yadawo amma be dawoba sai dare yana dawowa kuwa tayi masa magana yace zaiyiwa wani abokin sa magana da yake harkar gidaje amma sai zuwa gobe anan muka bar maganar zuwa goben,

Washe gari ma yace yama sa ana cigiya amma kamar na nawa nake so sai nace masa me sauke de yace kamar na dubu talatin ko ashirin ya isa tunda ni kadai ce nace masa eh ya isa ni koma bekai haka ba inaso duk tsufansa kuma dan nama fison tsohon gida me sauki sosai ko daki dayane ya isheni yace to ba matsala za asamu intakaice mukude saida mukai wajen wata ba asamu gida ba saida kyar akasamu shima ance sai andan yi masa gyara kuma ba anan bane awata unguwar ne nace ba matsala yanzu zuwa yaushe za agyara din yace inbada kamar nan da sati daya nace to alokacin nahada kudin da na ciro a pos da kuma wanda Ammi tabani nabashi dubu a shirin da biyar yakarba yaje yakai musu akallade sada nayi wajen wata daya da sati biyu sannan na tarkata yan kayan da na siya mana nabar musu gida dan banajin dadin zaman gidan kwata kwata agurin mutum daya nake samun sauqi duk tsawon lokacin da muka dauka dasu bawanda nasamu sauyi daga garesa kuma  hatta yaran gidan basu da kunya ba wanda yake girmamani ita kuma wacce muke mutuncin da ita bata da da ko daya shiyasa na matsu inbar gida,
mu uku muka nufi unguwar dani da limamin da kuma abokinsa wanda zai kaimu gidan ranar da muka bar gidan tunkan mukarasa unguwar aka kira limamin awaya daya daga cikin matansa ce ta kira shi wai yadawo tare dani wasu mutane sunzo nemana ko mudawo ko mufadi inda muke duk ina jinsu sai nace masa yakashe wayar kawai karyace komai sai ya kashe wayar sai yatambayeni ya za ayi dayan abokin nashine da shima yasan komai sai yace kawai ai mafita dayace shine liman ya koma yace musu ya riga yakawoni gidan da yakama min inyaso sai ya kwatan ta masu gidan sai yace nikuma yanzu mutafi gidan sa kafin yasamo min wani gidan daban yanda bazasu iya sanin inda nake ba munji dadin shawarar sa dan haka muka yarda tun alokacin muka saukeshi ya juya mukuma muka nufi gidan wannan abokin nasa inda yake unguwar kurna banyan mun isa sai naga banbanci da wadan can mutanen gidan liman nan gidan mace daya ce sai 'yayan su mace da namiji suma duk yarane namijin nema me wayo amma macen bata da wayo hannu bibbiyu matar ta karbe ni ko jin wacece nima bata tsaya tambayar mijin nata ba kawai yace mata ga bakiwa nan kafin asamo mata gidan haya zata zauna anan saboda bata san kowa ba anan tace to ba komai ai sai muzauna sosai take kula dani duk danasan tama girmeni ko bada yawa ba amma yanda take kula dani tana bani girma kamar nice gaba da ita haka muka zauna da ita yatanta ma sai faman daukar Ameesha suke naji dadin zaman gidan sosai cikin kwanciyar hankali harnayi kwana biyu,
bayan kwana uku aka samomin gida bamu da nisa da su badan taso ba muka bar gidan dan yaranta harda kuka macen ma cewa tayi sai ta bimu da kyar de suka bari muka tafi kudi naqara cirowa nasiyi duk wani abun amfani da nasan zan bukata da kayan sakawa da na daki komai de babu abun da bansiya ba dan zuwa lokacin ma kudin da na rage basu fi dubu goma ba dasu bayan 'yan kwanaki kuma sai nafara saro kaya inakaiwa wata makaran ta ina siyarwa saboda banason inzo in kashe kudin gaba daya shiya sa nafara juyasu ta hanyar kayayyakin yara haka naci gaba da rayuwata nikadai sai Ameesha amma wataran ina kaita gidan mutumin nan wajen 'yayan sa wataran kuma akawosu harma suka fara zuwa da kansu shakuwa ta shiga tsakanin su me qarfi har Ameesha tayi wayo sosai ta girma tama

1 / 74