Author : Bilyn Abdull Category : Romance
Haka ta barshi ya kwana shi kaɗai, sai a jirgi ne suka zauna waje ɗaya. Suna shiga ya maida ƙofar ya rufe ya mannata a jiki. Kallonsa take fuskarta babu walwala sam, ga idannunta sun ɗan ƙara fitowa saboda ramar da tayi ta jiyya. Shima kallon nata yake cikin wani yanayi mai wahalar fassara, kafin a hankali ya motsa lips ɗinsa cike da raɗa ya furta, “Besty bazaki yafe ma Ajwaad ki daina fushin nan ba?”.
Kanta ta ɗan kawar gefe kaɗan, idannunta na tara ƙwalla, ALLAH har yanzu taƙi daina ganin yanda yake dukan Nibras a idanunta da yanda take tsirara sai kimono a jiki, da yanda ta dinga roƙonsa akan yaransu amma taurin kai irin na mutumin nan ko. Hummm. Hannu yasa ya dawo da fuskar tata inda yake, sai kuma a hankali ya matsar da tashi gab yana busa mata numfashi. Cikin sake sauke murya ya ce, “Yanzu minene laifina anan? Ko sai yanzu kike jin kishi?”.
Hannayenta biyu ta saka ta turashi, dan wlhy da gaske fa sai yanzu take jin kishin abinda Nibras ɗin tayi, dan tun bayan lafawar komai zuciyarta ta kasa nutsuwa, tana matuƙar son tasan minene ya faru har yay ma Nibras dukan nan, musamman data ganta tsirara sai kimono a jiki. Amma babu wanda ya gaya mata komai har shi. Bata zarginsa, kuma ai tasan Nibras ɗin ce ta kawo masa kanta, amma idan ta tuna ko wani abu ya faru zafi zuciyarta take mata. Yanda take turashi shi kuma ko gezau baiyi ba ya sake fusatata tasa hannaye biyu tana dukan ƙirjinsa. Tsayawa kawai yayi yana kallonta yana danne dariya da ƙyar, sai da tayi iya iyawarta har ta gaji dan kanta ga hawaye sannan yay murmushi da kamota ya rungume tsam a jikinsa. Sai ta sake sakar masa kukan kawai. Baice mata komai bai har tayi shiru dan kanta sai a jiyar zuciya kawai take saukewa, sannan ya ɗagata cak ya nufi bedroom, saman haɗaɗɗen gadon ɗakin ya kwantar da ita ya fita ya jawo akwatinsu ɗaya jal sai dai babba ne sosai, sai bag ɗinta da bag ɗin laptop ɗinsu ita da shi dan aiki kam dole a cigaba da yinsa daga nan. Har lokacin tana a kwance inda ya barta. Baiyi magana ba ya shiga bayin ya dudduba sannan ya dawo bedroom ɗin ma ya dudduba, ya fita falo da ko'ina na gidan ya sake dawowa ya shiga bayin ya haɗa ruwa a jacuzzi mai ɗumu da ƙamshi sannan ya zo ya ɗagata ya cire mata kaya ya cire nashi ya wuce da ita. Cikin ruwan ya saka su, a tare suka sauke ajiyar zuciya. Sai kuma yanda ya ɗan ƙanƙameta ta ɗago tana kallonsa. Murmushi yay mata ƙasa-ƙasa fuskarsa a shagwaɓe ya ce, “Please Besty ki huce mana”.
Kafaɗa ta maƙe masa tana tura baki da kauda kai. Ya riƙo haɓarta cike da lallashi yace, “Mizan miki ki huce to?”.
“Ka faɗa min abinda ya faru a ranar”.
Ajiyar zuciya ya sauke, sai kawai ya shiga bata labarin komai bai ɓoye ba. Kai tsaye ta ce, “ALLAH ya isa ban yafe mata hawa min jikinka da tayi ba wlhy”.
Dariya ce ta kusa kufcema AA ya danne da ƙyar, sai kuma ta kalleshi itama kamar wata yayarsa ta ce, “Kai ma ka kalleta ko?”.
Kansa ya girgiza mata yana sake rungumota. “Ai har abada babu wata surar jikin mace da zata sake birge Ajwaad balle ta zame masa abin kallo in sha ALLAHU Besty. Kiyi haƙuri Besty mubar maganar nan wlhy ko tunawa bana son yi dan ƙona ni take matuƙa, ina jin nauyi da kunyar Yaya Fawzan da ke kanki da yarana, shiyasa har yanzu ji nake ban gamsu da abinda nai mata ba ma”.
Karon farko Maanal tayi murmushi tana shafa ƙirjinsa cike da kulawa. Sai kuma ta tausasa murya ta koma lallashinsa. Sun jima a bayin kafin su fito, haka ya taimaka mata tai shirin barci shima yayi, basa jin yunwa dan sun ci abinci a jirgi gab da zasu sauka. Dai-dai nan bell tai ƙara, yasan su twins aka kawo dan haka yaje ya amso su hannun Abah, sai coffee da Abah yay musu order shima suma su Babban Yaya sun amshi nasu. Sukaima juna sai da safe ya koma nasu shima ya shigo. Bayan sunsha coffee ɗin Maanal tayi feeding su twins kwanciya kawai sukayi duk da AA na cikin yanayin buƙata haka ya daure....
__________★
Satinsu ɗaya kenan a Chaina, Alhamdullah jikin Maanal kuma yayi sauƙi sosai, dan anan ma ta sake ganin likita sun tabbatar musu komai kuma normal. Shi AA ma ranar baya nan sunyi tafiya da abokinsa prof.. wani program. Oum da dama tafe take da kayan gyaranta sai tayi amfani da wannan damar ta shiga gyara Maanal ta jiki data ciki. Dan danan ta ƙara murjewa da gogewa dama ramar nan da tayi duk ta ciko abinta, sai wani glowing take kuwa Masha ALLAH. Ameerah da Najma suka sakata gaba, wai da alama Yaya AA na dawowa ba sauƙi za'a sake samo twins. Tun tana ƙyalesu harta fara ramawa itama. Kai daka gansu kasan suna cikin farin ciki da ƙaunar juna ta haƙiƙa. Su twins sam basu da taka maiman wajen zama. Barci kawai ke kaisu wajen Maanal.
Kwanan su AA takwas suka suka dawo. Kallo ɗaya da Maanal tai masa ta fahimci babu sauƙi, dan bai ɓoye mata ba ya fito fili ya nuna mata yana cikin wani hali. Murmushi kawai tayi batace komai ba, sai da ta taimaka masa yaci ya ƙoshi ta jashi bayi yin wanka. Anan ne fa ya kasa jurewa aka fara sakin layi, ƙarshe dai babu arziƙi aka kammala wankan aka fito. Daga nan ne fa labarin ya canja. Haba ai yayi haƙuri, kusan wata biyu.
Yako tabbatar mata yayi haƙurin, dan taji a jikinta har sai da ta koma masa kuka da magiya. Amma ina sai da ya tabbatar ya samu yanda yake so sannan ya koma lallashi da ban haƙuri, itako tana zuba masa shagwaɓa. Tun daga ranar aka buɗe sabon shafin amarci. Kullum suna sake mannema juna, kowa ƙoƙarin ƙyautatama ɗan uwansa yake. Kamfani kuwa suna tafi da komai yanda ya dace daga nan tamkar suna a gida Nigeria. Ga yaransu sunyi ƙyau sosai kamanin iyayensu na sake fitowa a tare da su.
Haka suma su Babban Yaya komai Alhamdullah, daga ɓangaren aiki har samun soyayya wajen matayensu, dan daga Ameerah har Najmah suna iya ƙoƙarin su suma na faranta musu. Ga ciki suna fama amma basa nuna gajiyawa da kulawa. Tsakaninsu da Oum da Abah tamkar iyaye ne da ƴaƴa ba surukai ba da iyayen miji. Duk abinda basu fahimta ba haka Oum ke zama ta koya musu yanda zasu gane. Kamar yanda suke kiran iyayensu da ƴan uwansu haka suke kiran Mamy suna gaisheta da Aunty, tun Mamyn bata sakewa har dai ta sake ɗin. A haka suka shiga watan haihuwa, dan tsakaninsu babu wani nisa sosai. Gaba ɗaya sai kulawarsu ta koma ƙarƙashin Oum da Maanal. Mazansu da ƴan uwa na binsu da addu'ar sauka lafiya.
Alhamdullahi Ameerah ce ta fara haihuwa ɗiya mace. Zo kaga murna wajen a halin Darma dana Hajiya Shuwa da dangin babanta na Katsina. Dan danan hoton yarinya mai kama da babanta ya baje ko ina. Kowa farin ciki yake da annashuwa. Anama Baby addu'a anama mai jego. Anama su Oum barka. Lokacin da Mamy taga hoton Baby harda hawayenta. Ita Aunty ma wlhy yanzu tausayi ƴar uwar tata ke bata.
Sati ɗaya da haihuwa aka sakama yarinya sunan Oum, sunan Anum ke nan, sai dai ita suna mata laƙani da Zarah. Duk da ba ƙasarsu ba AA yace sai sunyi shagali. Haka kuwa akayi, suka haɗa ɗan walimar cin abincin dare suka gayyaci abokan arziƙi na ƙasa da baƙin haure irinsu. Akaci akasha aka ɗan rausaya. Ƴan Nigeriya sai videos sukaita gani kawai da sanya albarka. Maijego tayi ƙyau har ta gaji, hakama Baby da ƙawayen maijego su Maanal, su twins yayu da sukai ɓul-ɓul abinsu dan har sun fara koyon zama ma sun sha ƙyau.
Sati uku tsakanin haihuwar Ameerah data Najma, itama ta sulluɓo yar budurwa mai kama da Yaya Fawzan. Yara dai duk sun rantse gidansu zasu ɗakko. Ya suhanallah wannan haihuwa ta musamman ce a zuri'ar Darma baki ɗaya. Danda nan itama hoton Baby ya fara yawo, finally Yaya Fawzan yaga jininsa a duniya. Ga yarinya ƙatuwa Masha ALLAH. Mutane sun so azo Nigeria a yi suna, sai dai yanzu ma haƙuri su Oum suka basu, dan su fa da gaske so suke su bama Nigeria iska sosai da sosai. Nan ma AA bai haƙura ba yace sai fa sunyi bikin suna. Haka kuwa sukayi shi tamkar na haihuwar Ameerah. Yarinya ta ci suna Khadijah. Nan ma anci an sha an yi wadaƙa sai dai mu babu damar cin banza wannan karon an barmu a Nigeria 🤭🥱. To ALLAH ya sanya albarka bazamu fasa addu'a ba ai.........✍️
215
........Sosai Oum ta tsaya akan masu jego sukai jego mai ƙyau da kulawa. Bawani batun wanka ko gargajiya amma komai Alhamdullah. Ga yara sunata ƙyau abinsu kamar ka lashe. Bayan sunan ne AA da Yaya Fawzan suka je Nigeria. Satinsu ɗaya suka dawo, sai dai sun biya ta saudia sun ɗakko Naufal da suka samu hutu. A zuwa sun nan sosai zuciyar Mamy ta karaya, dan ta gama yarda dai ƴaƴanta ba nata bane ba na Fateema ne. Mijin ma nata ne. Duk da nadama ta mamayeta ta gagara ɗaga baki ta nema gafarar kowa har yanzu. Sai aikin kuka, su dai su AA sunta lallashinta da mata nasiha iya iyawa. Sannan suna mata dukkan gatan daya dace akan komai tsaye suke a kanta. Kai bama su ba ko Baba Sardauna da su RK hidima sukema Mamy sosai, kawai dai sunan bata a gidan Darma ne yanzu. Sai nakasan ƙafa data ido data zuciya dake zagaye da ita. Idan akai dubi ta wani fannin kuma data gangar jiki saboda HIV. Amma da yake tana shan magani bama zaka gane ba.
Zuwan Naufal yama kowa daɗi, yaro ya ƙara girma ya fara zama ɗan saurayi, kamaninsa da su AA ya fito tsaff kamar sunyi kaki. Abin mamaki ko tambayar Saheeba baiyi ba. Sai ma farin cikin ganin su Oum da sabbin ƙanne har huɗu daya samu. Duk motsi sa kuwa yana manne da yaran nan. Yay hutunsa ya gama Abah da Oum suka maida shi Saudia, suma sun ɗan huta na sati uku sukai umrah suka wuce Nigeria dan Baba Sardauna baya jin daɗi. Sun duba shi aka gaggaisa da ƴan uwa da abokan arziƙi, har gidan Mamy Oum taje. Taji daɗin kuma ganin yanda Mamyn take cikin kulawa mai tsafta da nagarta. Suka sha hira Mamy na faman kukan zuci. A yanzu ma ALLAH bai bata damar roƙon Oum gafara ba. Girman kai da taurin zuciya na hana bakinta buɗewa akan hakan. Satin su Oum biyu a Nigeria suka koma abinsu....
________★
Rayuwa mai daɗi da nagarta ta cigaba da wanzuwa a cikin zuri'ar Aliyu Abubakar Darma. Hankalinsu ya kwanta matuƙa yanzu. Ga yara sunyi ɓulɓul da su su twins na gudunsu da magana ras. Zarah da Khadee ma na fara koyon tafiya. Yara masha ALLAH kamar ka lashe dan ƙyau da kulawa. Su dukansu basa ma banbance iyayensu saboda haɗin kai da iyayen ke da shi. Kowa ya yarda shi uba ne, kowacce ta yarda ita uwa ce. Yanda zata kula da wanda ta haifa, haka zata kula da wanda bata haifa ba. Mafi yawan lokaci ma a wajen Oum suke kwana. Suna da shekara ɗaya a Chaina Maanal, Ameerah, Najmah suka zo Nigeria halartar bikin yaran gidan su Ammie da zagaya dangi. Kowa ya gansu sai ambaton masha ALLAH. Yaransu kamar a cinye dan so. An sha biki daya amsa sunansa biki, dan kuwa Daddy yara takwas ya aurar a rana ɗaya. Hajiya Basariyya tazo abin tausayi, ta haihu tuni yaron ma ko isashiyar lafiya bai da shi sikila ne. Gaba ɗaya sai ta tsangwami kanta, ta kuma gigita da ganin irin daular duniyar da su Ammie ke ciki yanzu. Da itama bataima kanta mugunta ba da harda ita anan fa. Amma gashi nan masu aikin gidan ma sun fita fasali da ƙyawun kallo. Da taga Maanal kuwa ai sai ta ƙara sakin baki. Yarinyar ta girke abinta ta zama cikakkiyar mace komai yaji, ga ƙyau ga gayu ya ranta abin sha'awa masha ALLAH. Ko wajen events Hajiya Basariyya bata iya zuwa saboda kunya. A hakan ma Huznah ta mata ɗinkuna masu tsada, amma kayan daban jikinta daban koda ta saka. Duk sanda idonta ya sauka akan Daddy sai tayi kuka dan tausayin kanta. Sai ma taga kamar an ƙara masa wani ƙyau da ƙuruciya shi da matan nashi. Haka dai akasha biki amare aka kaisu gari daban-daban, Khadijah kawai aka kawo Abuja gidan Yaya Yazeed.
An kammala biki da kwana biyu ALLAH yay ma Gwaggo rasuwa. Dama su Maanal nada planing ɗin zuwa Giron sai kuma ga dalili. Haka suka shirya suka tafi ita, Amaal, Shaheeda da Ammie sai Nene, dan Aunty Sakina mijinta ya hana itama da yake tana aure yanzu anan cikin Abuja. Duka harda yara suka tafi. Sun ko samu tarba ta girmamawa, haka akai zaman uku da su, Gwaggo dai ansha jiyya sosai, dan ita duk da tana shan maganin HIV ɗin abin ya haɗa mata da tsufa shiyasa ta jigatu. Babu dai Alhamdullah, sai Sailu ce dai duk ta rame tayi baƙi, kodan abin ya mata yawa ne ga baƙin cikin Haƙilah da ɗanta, dan ta haihu namiji yaro kama da ubansa Temo sak. Kaida ka ganshi kaga ɗan ƙabilu, ga cin masifa kamar jaki. Bai fi shekara ɗaya da rabi ba amma cizon ƴaƴan mutane da yagushi ba'a magana. Idan akai magana Haƙila ta tsige mutum tas. Yawonta kuwa babu abinda ta fasa sai tai kwana uku bata gida, haka take barma Sailu ɗan kuma dole ta kula da shi, idan ta dawo kuma tai ta mata tujara kamar ba uwarta ba. Shi dai Sule ALLAH ya taimakesa, yana cikin Sokoto yanzu haka yana karatunsa na addini dana boko. Idan ka ganshi kamar ba shi ba, ya nutsu sosai masha ALLAH. Hakan yama su Maanal daɗi suma, sun kuma tabbatar masa yana kammala wannan makarantar Saudia zasu nema masa gurbin karatu. Aiko yayta murna da farin ciki. Haƙila kuwa da sukai ma faɗa ganin tana neman musu rashin kunya sai suka ƙyaleta suka ma fita sabgarta har akai uku suka baro garin. Suka bar Babu da kuka da kewar ƴan jikokinsa. Har yanzu zuciyarsa ta kasa sabawa da rashin Ammie, a kowane motsinsa cikin tuna rayuwarsu ta baya yake da nadamar kuskurensa. A wannan karon ma haka yayta neman gafararsu har su Maanal.
Suna dawowa Abuja da kwana biyu su Maanal suka fara shirin komawa Chaina, dan mazajensu fa sun dame su. Najmah na Kano, dan haka Ameerah da Maanal suka shirya suka sameta acan suma. Sun zagaye ahalin Darma har Yola wajen Gwaggo Khadijah. Har gidan Huznah suka je itama akai zuminci. Maanal taji daɗin ganin yanda rayuwar Huznah ta canja, dan sun sake gida ma yanzu ga ƴan yaranta uku gwanin sha'awa. Daga ƙarshe suka yada zango a gidan Mamy.
Mamy taji sun zo ƙasar, amma bata san suna Kano ba. Yau tunda ta tashi bata jin daɗi, ga Aunty ta fita biki a dangin mijinta. Sai ita kaɗai a gidan sai mai aikinsu. Tana tsakar gida tana shan iska Ahmad da Muhammad suka shiga gidan da gudu, Najma na kiransu amma ina basu dakata ba. Suma Zarah da Khadee na ganin yayinsu sun yi ciki sai suka bisu da nasu gudun. Gaban Mamy sosai ya faɗi, ta dinga bin yaran da kallo dan Muhammad dake gaba na shigowa kawai ya fara zagayeta Ahmad na binsa suna dariya, su Zarah ma sukabi layi.
Zuciyar Mamy na bugawa tana musu magana amma basu kulata ba sunata dariya da gujegujen su. A haka su Maanal sukai sallama suka shigo. Sai da kan Mamy ya nema fashewa. Ganin wasu cikakkun mata ƴan gayu ƴan ƙwalisa da kallo ɗaya zakai musu kasan nera ta zauna a jiki da suturarsu. Ga wani ƙamshi na girma ya cika tsakar gidan. Sai da Ameerah tama yaran tsawa suka tsaya cak sannan Mamy ta dawo hayyacinta. A nutse suka ƙarasa shigowa fuskokinsu da murmushi suna mata sannu. Fahimtar kamar bata ganesu bane yasa Najmah faɗin, “Mamy Maanal ce da Ameerah da Najma. Sai jikokinki”.
Gaba ɗaya sai lips ɗin Mamy suka fara rawa, idonta ya cika da ƙwalla. Da ƙyar tai musu jagora zuwa cikin gidan. Sunata kallon ko'ina su dai. Bayan sun shiga sun zauna mai aiki ta kawo musu ruwa. Cikin girmamawa suka gaida Mamy, ita ko tana amsawa da rawar murya. Maanal ta harari yaran da suka tsaya suna kallon Mamy kamar sun sami magiji.
“Wai baku iya gaisuwa bane ba yaran nan”.
Da sauri Muhammad ya kama kunensa ya ce, “Sorry Mie-mie”. Ganin haka shima Ahmad ya kama nasa kunnen, hakama su Zarah, suka haɗa baki suka ce “Sorry Mie-mie” bakuna a taɓe abinka da ƴan madara🥱. Maanal ta ce, “Oya naji a gaida Mamy”. A tare yaran suka matsa inda take cike da ladabi bakinsu a haɗe sukace, “Mamy good afternoon”.
Yawu mai kauri Mamy ta haɗiye. Tana murmushin yaƙe ta ce, “Kuna lafiya?”.
Kansu suka ɗaga mata dan suna jin hausarsu tsaff. Ganin tayi shiru Ahmad ya ce, “Baki ce ya Grandpa da Grandma, da Daddy's ɗinmu ba?”.
Mamaki ya kama Mamy, ga shi su duka huɗu sun wani tsareta da idanunsu sak irin na Aliyu da Fateema da su AA. Sai kunya ta kama su Maanal. Najmah ta ce, “Ta tambaya a zuciya, oya azo a zauna”.
Mamy zatai magana sai ga Aunty, yanda Aunty