AJIYA A DUHU

Author :  Bilyn Abdull Category :  Romance

Chapter   121 / 213

360K to 363K   out of 636.6K words

kuma babban yaya ke fitowa hannunsa riƙe da waya yana magana. Sai kawai sukaci karo dan su duka hankalinsu baya a gabansu. Cikin sauri tai ƙasa zata tallabe basket ɗin shima ya duƙo zai tallabosa batare dama yaga wacece ba. Wani kalar bugar hancinsa mayataccen ƙamshin turarenta yayi, ya wani irin zuƙa ya lumshe idanunsa irin na AA. Ita ɗin ma dai nasan ƙamshin ne ya wani kalar ratsata. Sai da taja numfashi kamar mai asthma ta haɗiye. A tare suka ɗago, yana ƙoƙarin ce mata sorry itama tana ƙoƙarin cemasa sai kowa yay shiru. Sai kuma ita ta saki murmushi da faɗin, “Lah Babban Yaya ashe kaine. Good evening fatan anyi salla lafiya”.
        Sosai wani abu mai girma ya tsargama babban Yaya, kasancewar sa ba gwanin murmushi ba shi sai ya tsareta da idanu kawai. Muryarsa a ƙasa ya furta, “Ameerah kece haka?”.
    Murmushi tayi tana mai duƙar da kanta cike da kunya. Shima sai ya wani lumshe idanu ya buɗe kamar mai shirin suma. Sai kuma ya bata hanya yana faɗin, “Kin dawo lafiya ya karatu?”.
      “Alhamdullahi Yaya an kammala.”
  “Masha ALLAH, ALLAH ya sanya albarka sai aure ko?”.
   Kalmar ta suɓuto masa batare daya shirya hakan ba. Ɓoye fuska Ameera tayi cike da kunya ta ce, “Yaya ba yanzu ba”.
      Murmushi yayi da ɗan taɓe baki ya ce, “Idan mun yarda mu yayye kenan. Oya shiga Oum ɗin na ciki”.
    Ai da sauri Ameerah ta shige. Dan harga ALLAH kallon da baban yaya ke mata ba ƙaramin rikita mata lissafi yay ba yau ɗin nan. Oum na ganinta ta fara murna da mata oyoyo, ALLAH sarki Oum uwa maba da mama kenan ita kowa nata ne, shiyyasa da wahala kaji mutum yace baya sonta. Rungumeta Ameerah tayi cike da farin cikin ganinta, dan itama tayi missing ɗin Oum sosai. Dai-dai nan Maanal da AA suka fito daga bedroom ɗin Oum. Ameerah ta ɗan kafe Maanal da kallo, sai kuma ta juya tana kallon Oum idanu a zare ta ce, “Oum Maanal ko?”.
       Oum na dariya ta ɗaga mata kai. Cikin wani kalar farin ciki Ameerah ta juyo tana sake kallon Maanal, dan tasan labarinta sosai a wajen Oum. Ta ce, “Woow Oum ƙyaƙyƙyawa da ita”. Sai kawai taje ta rungume Maanal ɗin tana faɗin, “My twin sister nayi farin cikin ganinki”.
      Murmushi Maanal tayi kaɗan duk da bata santa ba, suna haɗa ido da AA ya ɗauke kansa. Ameerah data ɗago itama sai ta kalla AA ɗin. “Oh Yaya AA shine koka faɗa min Bestynka ta dawo, bayan ranar har gaisheka nai ta WhatsApp”.
        Hararrata ya ɗanyi ya raɓasu zai wuce. Ameerah bata damu ba dan tasan halin kayanta. Har cikin rai ɗaukar su AA take kamar Yaya Ameer, suma kuma suna mata gata irin ta yayu da ƙanwa. AA ɗin ne ma dai bai cika sakewa ba. Kuma tunda ta fahimci halinsa kenan bata wani damuwa da wani ɗaure-ɗauren fuskarsa ko rashin yawan magana. Oum ce taima Maanal bayanin Ameerah, dan ranar data fara ganin Hajiya Shuwa a gidan ta bata labarinsu kaf. Oum nace mata su Najma ma nan cike da farin ciki taja hannun Maanal suka nufi garden dan su Najma nacan. Aiko suma su Najma na hango Ameerah suka taso a guje suna ihun murna dan abokiyar wasansu ce idan sunzo hutu. Nanfa hira ta ɓalle dan Ameerah babu ruwanta.....

_________

       Washe garin salla AA ya damu Abah da maganar Yaya Fawzan da Najma. Mamaki ne ya kama Abah sosai, amma sai murmushi yake na farin ciki.
      “Naji daɗin wannan al'amari ƙwarai da gaske Ajwaad. Kuma ina sha ALLAHU bazayi ƙasa a gwiwa ba a yau ɗin nan zan kira Baba na sanar masa. Idan so samu ne a satin nan akai kuɗi a haɗa bikin da naka ma. Dan na jima da fahimtar Fawzan na buƙatar ƙara aure”.
      Murmushi AA yayi shima, ya ce, “ALLAH ya tabbatar Abah, kaga shike nan ma an huta ta ƙarasa karatun a ɗakinta”.
       “Sosai kuwa haka za'ai in sha ALLAHU, in ma zai yi hakuri sai a ɗaura kawai idan ta kammala jarabawar tunda wata ɗaya ne sai ta tare. Kaima kuma dama ina nemanka akan naka auren da yarinyar nan Nuratu”.
    A take fuskar AA ta canja. Abah na lura da shi yay ɗan murmushin manya. Kafin ma yace wani abu AA ya fara magana murya a cinkushe.
      “Abah wai maganar yarinyar nan baza'a barshi bane. Nifa ko ƙaunar ganinta banayi a gidan nan balle kallonta a wani matsayi mai kusanci dani. Yarinyar nan bata da tarbiyya sam, sannan rawar kanta yayi yawa. Haba mace babu nutsuwa ai ba mace bace. Dan ALLAH Abah ni dai ka rufa min asiri ka rushe maganar nan matata ta isheni wlhy”.
      Sosai abin ya ba Abah dariya, dan kamar fa AA zai masa kuka. Amma dai ya danne cike da kulawa ya ce, “Karkace haka Ajwaad koba komai ƴar uwarka ce ita. Sannan bamu san inda rana zata faɗi ba nan gaba ALLAH ya jarabceka da sonta. Kuma kaga an riga an tsaida magana da iyayenta bai kamata mu zama ƙananun mutane ba ai ko”.
     Sosai zuciya ta tokare maƙoshin AA. Da kyar ya iya furta, “Shike nan Abah, amma dan ALLAH ba yanzu ba, a ɗan bani lokaci idan na shirya da kaina zan maka magana”.
    Ɗan jimmm Abah yayi na tunani, sai kuma ya jinjina kansa, “Okay ba damuwa, amma ina son ka kira Baba kai masa bayani da kanka, dan gaskiya bansan yanda zan tunkaresa ba. Tunda na hannun damarsa ne kai nasan zai saurareka”.
        “In sha ALLAHU zamma je Kanon gobe”.
   Nanma dariya sai da ta kusa kufcema Abah, ya ta dai danne da ƙyar. “Okay ALLAH ya kaimu, sai batun Maanal, zata koma gidan Shahidah...”
       “Saboda mi?”.
   “Saboda Oum ɗinku ta nema alfarmar hakan, wai zasu mata ko gyaran jiki na amare kasan dai mata.”
     Sam AA baiso hakan ba, amma har gaban abada bazai iya musu da Oum ba. Dan haka yace, “Shike nan Abah. Dama akwai kaya da suka iso na lefenta, suna hannun Babban Yaya. Amma da zai yiwu ba sai an kaisu ko'ina ba, kawai a ajiye mata Abah”.
         “Masha ALLAH, ALLAH yay maka albarka Ajwaad. Hakan yayi sosai, tunda ankai wancan na wajen Rafeeq kada mutane suga kamar wata fariyya ce. Amma in aka ajiye mata ƴan uwanta kawai suzo su gani ya wadatar.”
      “Nima abinda nayi tunani kenan”.
Albarka sosai Abah ya dinga saka masa, daga haka suka cigaba da hirarsu....

WASHE GARI

        Da safe AA ya wuce Kano, lokacin Maanal ma na barci ko sallama basuyi ba. Kai rabon daya samu zama da ita tun daren salla da suka fita yawo sai 12 suka dawo. Jiya ita da su Oum da yaran duka a gidan Shahidah suka yini sai dare suka dawo. Yau kuma gashi zai wuce kano tana barci. Ashe Oum ta shirya masa, dan sun gama tsara komai ita da Hajiya Shuwa, dama Maanal ba gidan Didi Shahidah zata zauna ba, nan gidan Hajiya Shuwa ne. Oum ta ɓoye hakan ne dan kar ma AA yace zai dinga zuwa gidan wajenta ya ɓata musu aiki. Aiko a ranar da yamma Oum ta amshe wayar Maanal aka kaita gidan Hajiya Shuwa babu wanda ya sani hatta da Abah. An kuma gargaɗi Ameera. Gaba ɗaya sai Maanal taji ta damu batai sallama da AA ba. Amma dai ta dake ko'a fuska bata nunama Oum komai ba.

      A ranar AA bai dawo ba sai washe gari, yanata baza idon ganin Maanal shiru. Da ga ƙarshe dai ya daure ya tambayi Oum tace ba Abah ya gaya masa zataje gidan Shahidah gyaran jiki ba. Kasa cewa komai AA yayi, dan Oum ta wuce gaban ka-ce-na-ce a wajensa. Duk kuma yanda tayi dai-dai ne. Aiko bai ƙara magana ba bawan ALLAH, sai ma ya tattara ya koma aiki. Maanal kuma ya saka aka ƙara rubuta mata sabon hutu bayan wanda suka sha tun daga dawowa Chaina.
       Mamy ma dai bata ganin Maanal a gidan, bata tambaya ba amma abun naci mata zuciya. Gefe shirye-shiryen bikin da suke ya ɗauke mata hankali. A haka aka ci kwanaki sati ɗaya. Saura sati ɗaya biki kenan. Da yamma babu zato suka samu baƙuncin Baba Sardauna tare da Uncle Mahmoud da yay masa rakkiya. Saheeba ce ta shiga tana faɗa ma Mamy zuwansu. A take fuskar Mamy ta canja, cikin taɓe baki ta ce, “Uwar mi kuma akayi to?”.
      “Waya sammusu Mamy, kin dai san in dai kaga tsohon nan to ba alkairi ba ne”.
    Kafin Mamy ta bada amsa kira ya shigo mata waya, Abah ne kuwa, tana ɗagawa yace tazo ga Baba. Kafin tace wani abu ya yanke. Kwafa tayi mai ƙarfi, kafin ta miƙe tana tsinema Darma Family gaba ɗaya. Hijjab ta saka sannan ta nufi sashen Abah ɗin hannunta ɗauke da basket na abinci data saka Haule ta haɗa mata. (Munafukai) Ta faɗa a zuciyarta ganin Oum zaune kusa da Baba fuskokinsu cike da farin ciki, dakewa tai itama ta ƙawata tata fuskar da fara'a. Cikin girmamawa ta gaishe da Baba, ya amsa mata da kulawa kamar yanda ya saba. Sai ta koma tsokanar Uncle Mahmoud irin wasan ƙanin miji. Shiko yana ramawa. Haka dai aka gaisa cikin farin ciki kamar babu komai a zukata..
      Bayan su Baba sunci abinci sun huta bayan sallar isha'i akai zaman meeting. Baba da kansa yay masu bayani cewar sun shiryama Ajwaad da Maanal bikin tarewa. Sannan batun Nuratu ga yanda suka tsara saboda abinda ya dinga faruwa a tsakanin Maanal da Nuratun da azumin nan. Dan haka yana roƙonsu su basu haɗin kai ayi komai a tashi lafiya, su kumayi fatan zuwan na Nuratun itama da kamar yau ne da an kammala ginin da za'a sakata ciki, saboda haɗasu waje guda bazai haifar da ɗa mai ido ba..........✍️




*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*

*09032345899*



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_💞AJIYA A DUHU....💞_*




*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*


*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R


_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

*_BOOK 2_*
🅿️➖6️⃣2️⃣


______________


........Babu wanda yay musu akan hakan, tunda dai agaban idon kowa komai ya dinga faruwa. AA sai wani munafukin murmushi yake a kaikaice. Mamy na lura da shi sai ko ta ƙara ƙulawa. Amma dai ta dake yanda kowa yay addu'a itama tayi. A zuciya kuwa kaf family ɗin Darma sai da ta tsine musu yau, a ganinta munafunci ne kawai. Da ƙyar ta iya riƙe kanta aka tashi a wannan zama. Ko ganin hanya batayi sosai ta nufi sashenta, tana shiga sai ga Maman Saheeba ta kirata. Kamar bazata ɗauka ba tadai daure ta ɗauka ɗin, ko sallamarta Maman Saheeba bata amsa ba a haukace ta fara magana wai yanzu Baban su Nuratu yazo ya sameta da batun Baba Sardauna ya sameshi ɗazun da yamma ita bata nan yace masa ayi haƙuri a ɗan basu lokaci akan bikin nan suna neman alfarma. Ita kanta Mamy gigicewa tayi dan taso ace ita zata zauna ta tsara ma su Maman Saheeba ɗin ashe mugun tsohon sai da ya fara zuwa can, da alama ma daga gidan nasu sukayo airport. Cikin son kwantar mata da hankali ta ce “Nana!”.
        Ƙin amsawa tayi, ta cigaba da masifa, sai kan Mamy ya dinga wani irin sarawa na ciwo, ga masifar Maman Saheeba na haura mata har saman kan. Sai kawai jiri ya kwasheta ta zube a ƙasa. Sai Haule ce ta taimaka mata ta tashi da ƙyar, ta kamata domin takaita bedroom tace ta ƙyaleta. Haka ta taka zuwa bedroom ɗin nata da ƙyar ta kwanta. Wani irin ciwon kai kamar ana buga mata guduma na cikinta. Sai hawaye sharrr-sharrr. Waya ta jawo da ƙyar tai kiran baban su Nuratu. Bugu ɗaya kuwa ya amsa. Cike da girmamawar da yake bata ya shiga gaisheta. Ta amsa cikin sanyin murya tana tambayarsa miya faru? Yaya sukai da Baba Sardauna.
       Sai da ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce, “Aunty, Alhaji Sardauna magana yay min ta fahimta kuma ta gamsuwa. Kawai ƴar uwarki taso tada hankalinta ne da naki. Ya tabbatar min tunda Nuratu tazo gidan nan naku take jan rikici tsakaninta da ita matar Ajwaad, shiyasa suka ga za'a iya samun matsala ace an haɗasu a muhalli guda. Tun rikicin na iyakar su biyu zai koma ya taɓa zuminci ne tunda yau da gobe sai ALLAH. Shiyyasa shi Ajwaad ya nema alfarmar a bashi lokaci zai mata gini sai ya sakata a ciki, idan kuma tafi son nan gidan sai ita matarsa ta koma can ita Nuratu ta zauna nan kusa da ke. Dan ALLAH ina wuyarta ga daɗinta a wannan shawarar? In ce sauƙi ma aka samawa kowa. Amma ta yada hankalinta gata can harda yanke jiki ta faɗi sai da aka saka mata ƙarin ruwa. Ko saurarena na gama mata bayani ma batai ba fa ta hau bori tai kiranki”.
     Ajiyar zuciya Mamy ta sauke. Sai kuma a hankali tace, “Shikenan ka bari zan shigo Kanon gobe da safe.”
     Cikin jin daɗi yace, “ALLAH ya kaimu aunty sai kinzo”.
    Mamy na yanke kiran tai lamo, sosai take fassara maganganun baban su Saheeba ɗin dalla-dalla. Wani sashen na zuciyarta najin gamsuwa da zancen, wani ɓangare kuma na nuna mata yaudara ce kawai, ba kowa ya shiryata ba kuma sai Oum. Ko kuma ta kitsama Ajwaad ya faɗama Baba Sardauna, in ba haka ba ta ina Baban yasan wani anyi rikici da azumi? Koda yake akwai munafukan yaran nan ƴan hutu, suma zasu iya fa. Dan ita bata san AA yaje Kano kwana biyar da suka wuce ba. Kawai dai tasan yayi tafiya, amma bata san ina yaje ba. Sosai zuciya ke tunzurata akan taje ta samu Oum, amma wata na kwaɓarta akan ta fara bari Ajwaad ya dawo ta fara tuhumarsa sannan. Wani gefe na nuna mata ba lokacin fito-na-gito bane yanzu. Ta bari sai ƴaƴanta sun gama dawowa tafin hannunta ta hanyar auren zaɓinta gaba ɗaya tukunna. Dan haka ta cigaba da lallaɓawa ai auren nan na Nuratu da Ajwaad, shima Fawzan ya auri Amani dan yarinyar kullum sake shige mata zuciya take, kullum sai ta kirata a waya sun gaisa. Ganin haka bata taɓa tuhumarta batun Fawzan na kiranta ba, ita kuma Amani batai mata maganar ba itama. Shi ko Fawzan dan karma Mamy tai masa maganar Amani a tsaitsaye yake shigowa gaisheta da safe, idan ya dawo aiki kuwa sai gab da magriba shaf-shaf yazo ya fice. Ganin kuma bai sake cewa komai ba sai ta ɗauka yana kan lallaɓa Amani ɗin ne su daidaita. Taso yaje da sallar nan amma sai Maman Saheeba tace ta bishi a hankali, wataran ma bata sani ba zai je wajen Amani ɗin tunda har ya yarda suke waya..

       _________★

     Sosai akema Maanal gyara na fitar hayyaci, ciki da wajenta ga wani uban ƙamshi na bala'i a dukkan motsinta. Fatan ta kuwa wani irin santsi da take da walƙiya abin ba'a magana. Ita kanta ji take a jikinta komai ya canja. Hatta gashinta, ƙafafunta da tafukan hannunta gyara Hajiya Shuwa ke musu na balan bala'i. Kai Hajiya Shuwa tasan sirrin gyaran mace na bala'i ƙwarai da gaske. Dan hatta baki da lips ba'a bari ba. Ga wasu manyan lectures na zaman aure da take buɗema Maanal ɓaro-ɓaro. Idan ta nuna jin kunya ta mata daƙuwa da faɗin.
      “Kaniyarki, ba batun kunya muke ba anan, ki nutsu ki fahimci komai nake so. Kina dai ganin gogaggiyar yarinyar da ake so a aura masa mai ido a tsakiyar goshi. Mijinki ba ƙaramin mutum bane ba, sannan yana masifar sonki. Haƙurin da yay na shekaru karma kiyi zaton zai raga miki. Sannan yana zaga duniya yana gamo da mata kala-kala baki sani mugun halin wata ba, wasu matan da shirinsu suke kasancewa akan ƙwace miji wlhy. Mu kammu munsha wannan gwagwarmayar a lokacin ma duniya na barci balle yanzu da idonta ke a buɗe ƙyar”.
    Ire-iren irin wannan nasihar ke sanyaya jikin Maanal ƙwarai da gaske. Sai ta ƙara nutsuwa tana ɗaukar komai yanda ya kamata. Wani gefe na zuciyarta kuma najin kewar su Oum da su Ammie. Dan kowa ma Hajiya Shuwa ta hanata waya, acewarta so take ta bata hankalinta gaba ɗaya. Aiko ta bata ɗin, dan Maanal ɗin a kallo ɗaya zaka fahimci makarantar Hajiya Shuwa ba tasiri a gareta yanda ya kamata....

          Ata ɓangaren Oum kuwa shirin biki suke mai ban mamaki, dan sai ka ɗauka ma sai yanzu ne za'a ɗaura auren. Ta ƙarƙashin ƙasa kuwa Abah da AA da RK da Babban Yaya na shirya na Yaya Fawzan, dan an gama komai amma su kaɗai maza suka san da auren ko su Oum basu sani ba. Ita kanta Hajiya Majdiya Baban su Najma kawai ya sameta cewar zaima Najma aure. Da farko rikicewa tayi, amma da ya zauna ta mata nasiha da tabbatar mata zatai farin ciki daga baya sai ta kwantar da hankalinta, dan tasan bazai cutar da ƴarsa ba, kuma yana da dalilin ɓoye matan. Za'a ɗaura aure ne kawai biki sai Najma ta gama jarabawarta da take shirin farawa nan da sati ɗaya. Dan haka su idan za'a kaita su zasuyi nasu bikin. Kuma hatta shi Fawzan ɗin bai san da wannan batu ba, dan AA da RK sun gama shirya komai da komai har gayyatar abokansa....

      Mamy ma taje Kano, sai dai aranar ta dawo. Da alama kuma ta ciwo nasarar sasantawa

121 / 213

Chapters