Garkuwa 1 Complete Hausa Novel

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Romance

Chapter   28 / 72

81K to 84K   out of 214K words

Shiyasa mahaifinku keta ?in amsar sarautar har sai randa Imran ya mallaki hankalinshi, ku kuwa kun zama ababen kyarata. Yaya zanyi da raina.
Shiru sukayi gaba Wayansu,
Shi kuwa Ya Jafar sai ?ara sautin karatun yayi. Yanayi yana zubda hawaye.


Shi kuwa Jalal, shiru yayi yana ri?e da hannun Jafar Win.
Jamil kuwa katse kiran yayi.
Affan kuma wanda dama tare suka shigo, fuska ya Wan kele, cikin irin matsayin da ?an auta kedashi a wurin iyayensu yace.
"Mama, shifa zato zunubine koda ya kasance gsky. Ki dena jifar Mommy da batun wai ita ta tambaWamu, ya za'ayi keda kanki ki rin?a suffantamu da marasa nagarta mu dai gsky ba a tamSaWe mukeba,
Menene a cikin mulki da sarauta, Mama akwai wani mulkine matabbaci a duniya banda mulkin mahaliccin mu, in ma Imran ya gaji sarauta menene a ciki Wan uwanmu nefa".
Cikin sanyi ta girgiza kanta a hankali tace.
"?an uba dai ba Wan uwaba".
A tare suka zuba mata ido baki Wayansu.
Aunty Juwairiyya kuwa, ruggume yarta kawai tayi, tana jin ranta na suya.

A cikin fada kuwa, tun tuni Maimartaba ya fito, yana shigowa suka gaisa dasu Bappa ya amshesu a mutunce, cikin kulawa, da mutuntaka, bayan sun gaisa Winne suka koro mishi jawabin abinda ke tafe dasu.
Shiru mutanen fadar sukayi baki Wayansu, sai muryar Ardo Bani, da yake ?are zancensa da cewa.
"Babban tashin hankalinmu, kullum Wauki WaWWayan da akeyima yaranmu da tsoffinmu.
Kana a sace dabobbin mu, in mun kai kukanmu ga hukuma ko masarauta sai ayi burus damu, koma a ?ara mana da cin zarafi ko ?azafi. To gashi yanzu ankai matakin ana sace mana yara, ko gawarwakinsu ba'a bar mana, shiyasa mukayi tattakin isowa gareka adalin shugaba, ka duba lamarinmu."

Wani irin zafi da ?una ne ya cika zuciyar, Maimartaba Lamido, zalumci yayi yawa.
Gyara zaman babbar Al'kebbar sarautar dake jikinsa ya Wan yi, yana maijin ?una da tafasa a zuciyarshi, fargaba da tsoron, ha?in bayin Allah'n da aketa kashewa ya cika mishi zuciya, sabida sanin shine sarki kuma shugaba, ga duk wani mutun dake yankin.
Wani nannauyan numfashi yaja mai ?arfi.
Juyawa yayi ya fuskanci maga takardar fadar tashi, cikin bada umarni yace.
"A rubuta takarda a aikawa Haman-?achama cewar ina bukatar ganinshi, da gaggawa.
Kana ya tabbatar kafin ya isoni yankin da yake mulka babu sauran zalumci, ko ?abilanci!".
Cikin cika umarnin da maga takardar ya Wan rusuna, tare da cewa.
"An gama ya Mai alfarma Sarki Adalin Sarki."
Waziri, Galadima, Wambai, Sarkin fada, kana da sarkin dogarai, duk, shiru sukayi sabida a zahiri ake iya han?o tsantsar tashin hankali da Sacin rai a fuskar adalin shugaban nasu.

Su kuwa su Bappa sosai sukaji sanyi, a zu?atansu, sabida nuna kulawarshi garesu,
cikin iya sarrafa harshe da tausasan laffuza mai martaba sarkin Nuruddeen Bubayero JoWa yace.
"Kuyi ha?uri, ku gafarceni, bani da labarin dukkan abinda ke faruwa daku, sai yanzu, naji daWi da kuka nemeni, da matsalarku, In sha Allah ni kuwa zan Wauki mataki, da izinin ubangiji koda belbelun dake cikin shanunku baza'a sake kashesuba, bare dabobbin ku, bare a kai ga rayukanku. Zan kirayi GARKUWAN FULANI, yanzu, zan sashi maza ya taho ya dawo ?asar sa,
Domin shiga lamuranku nauyin a kanshi yake."
Sai kuma ya Wan numfasa kana ya kalli wani bafadensa dake tsaye bayanshi yanayi mishi fifita da maficin da akayishi da gashin kekkyawan Wawisu.
Cikin bada umarni ya umarceshi daya koma gefe,
Da sauri ya rusana ya koma gefen.
Shi kuwa Sarki Nuruddeen, wani Wan kekyawan matashi dake gefen damanshi ya kalla tare da cewa.
"Imrana, kiramin Sheykh Jabeer."
Kai ya Wan rusunar kana yasa hannu ya amshi wayar da Kakan nashi ke mi?a mishi.
Amsa yayi, kana ya kira Sheykh Jabeer, wanda shi kuma a dai-dai lokacin yana gaban Sheykh Aliyu, Abdulkareem, Jabeer, Sitti, Jazrah, Haroon. Da dai sauran ahlin nasu.

Wanda kiran ne yasa ya samu ya fece daga tarkon da ake naWa mishi.

Jin wayar tayi ringing har ta katse ba'a Waga bane, yasa Imran Wan rusunar da kanshi tare da cewa.
"Wata ?il baya kusa da wayar."
Kai ya jinjina mishi tare da cewa.
"A a zai kira, bayan amsa kirana yanzu zai kira".
Kai ya gyaWa alamar gamsuwa.
Suko su Bappa duk suna zaune cikin kamala.

Shi kuwa Sheykh kamar yadda ya saba, hakane baya amsa kiran kakan nashi, sai dai ya bari in tayi ta katse sai ya kira, shiyasa, yanzuma ya bari saida ta katsen sannan ya kira.


Gyara zamansa yayi tare da kara wayar a kunnensa na dama.

Imran kuwa yana ganin kiranshi yayi maza ya amsa,
cikin tarin girmamawa yace.
"Barka da hantsi, Hamma Jabeer".
A can gefen Sheykh Jabeer Win kuwa, ido ya lumshe cikin yanayinshi da sun rigaya sun saba yayi shiru.
Da sauri Imran ya kuma Wan rusunar da kanshi yace.
"Afwan Sheykh Assalamu alaikum ".
Murya can ?asa yace.
"Wa alaikassalam".
Cikin Wan tura baki Imran ya kuma maimaita mgnarsa ta forko.
"Barka da safiya, Hamma Jabeer ya, Sitti?".
A ta?aice yace.
"Alhamdulillah".
Da sauri Imrana yace.
"Masha Allah, ga LamiWo".
"Na'am". Yace a takaice.
Shi kuwa Imran mi?awa kakansu wayar yayi.
A hankali Sheykh ya Wan buWa laSSansa cikin zazza?an sautin muryarsa yace.
"Assalamu alaikum".
Murmushi mai cike da so da ?aunar jikan, nasa yayi tare da amsa sallamar tasa. Gaisawa sukayi, bayan sun gaisa ya tambayi labarin su Sitti da ?anennenta da kuma mahaifinta, sai kuma ya kora mishi jawabin abinda ke faruwa a jihar tasu.
Kana, ya Woro da cewa.
"Ka dawo, kayiwa lamarin tubkar hanci". Cikin sanyi yace.
"In sha Allah. Ina nan tafe, nanda kwanaki uku. Ina jajanta musu, abinda ya faru, kuma in sha Allah.
hakan bazai kuma faruwa ba.

Da haka sukayi sallama.

A can garin Numan kuwa cikin Rugar Kikan.

Gaba Waya garin shiru yayi, dan wannan abunda ya faru yayi masifar shiga jikinsu.
Da dama maza matasanmu sun tafi kiwo, kamar yadda suka saba, rayuwar yau da kullum.
Saura sai irin dattawan da aka bari, da mata da yara maza da mata.


Cikin garin Bonon kuwa, gaba Waya, matasan garin dama ?auyuka gefensu na ?abulun ?achamawa, duk sun hallara wuri Waya, suna cike gaban dodon tsafinsu, wato Bonon Win, giyar burkutu mai Wan karen tsami da wari, suketa sha, tamkar zasu fasa cikkunansu.
Yayinda gefe guda kuma, ma?erar dake gefe wasu matasa su ne ma?era keta wasa ababen faWansu, kamarsu wu?a?e, Adda, sitaka, barandami, mashi, kibau, da dai sauran mugayen makamai, sai she?i sukeyi.

Suna cike a wurin, Ba'ana ya iso, cikin wata shigar rigar sa?i.
Hanya suka rin?a buWa mishi, hardai ya isa ga sarkinsu, dake zaune gefen dodo sun. Zama yayi kusa da sarkin nasu ya sasu a gaba,
Cikin harshen Sacamancin yace.
"Ku hanzarta, ku shiga, duk matasansu majiya ?arfi, sun tafi kiwo. Dottijan su kuma sun tafi, kai gulmarku, ga Sarkin su wannan karon basu tsaya ga sarkinku na nanba, ina da ya?inin kuma za'a sauraresu a can.
Yanzu matansu da ?a?ansu, ?anana mata da mazane suka rage a garin.
Sai wasu dattawansu dake, dakon dawowar magulmatan can.
Kuyi maza, kushiha kafin su dawo, ku share garin kab.
Ku kashesu gaba Waya babba da yaro mace dana miji."
Da sauri wani daga cikin su yace.
"Harda gidansu Shatu?".
Cikin izaya yace.
"Harda su, domin Mata, bata nan, ku kashe kowa nata, ta hakane zata dogara dani kaWai tunda bata da kowa nata a duniya, dole Ni zan zama mijinta ubanta yayunta ?annenta uwarta, in zama Garkuwarta in zame mata duniyarta ta hakane zata yarda nine Waya gatanta kuma duniyarta, ba tare da ta zargeniba, a hankali wata rana in sata tayi ridda, musha giya, muyi tsafi tare da ita, bazatayi min musuba, mu haifi Wanmu na forko mu bawa dodonmu yasha jininshi yasa mana al'barka a aurenmu".
Wani irin ihu da sowa na tsantsar jin daWin bayaninshi sukayi baki Wayansu.
Hakama dodonsun, saida ihunshi ya firgitasu baki Wayansu.
Dariya mai amo mara daWin ji. Sarkin nasu yayi, kana ya busa ?ahon dodonsun, alamun ya basu izinin tafiya.

Nan fa duk suka rin?a shiga, cikin ma?erarnan suna Waukan makamai, suna nufar garin Rugar Kikan (Rugar Bani) kenan a guje...


Cikin garin Shikan kuwa, Bani rana ta fara tasawa, mata masu zuwa tallan nono cikin garin Numan, suka fara Waukar ?orarensu, suna fita garin.
Yara maza da mata kuwa, wasu na wasa wasu na Webo ruwa, wasu na Webo kayan lamSu.
Yayinda wasu kuma suka dawo break dan tara tayi.

Cikinsu kuwa harda Junainah.

Tafe take da saurinta da Wan tsalle-tsallenta tana rataye da yar jakarta,
da sauri ta tsaya ganin Junaidu a gabanta rike da kwanWon zabari wanda yake cike da ?a?an itatuwa.
Murmushi ta Wanyi tare da sunkuyar da kanta cikin surutunta tace.
"Har naji tsoro!".
ta ?arishe mgnar tana kallonshi,
Murmushi yayi mata shima cikin son ?arinyar yace.
"Haba dai, tsoron me kuma zakiji, tunda gani, babu abinda zai sameki muddin ina raye, zan zame miki Garkuwa".
Da sauri tasa hannu ta rufe bakinta tare da cewa.
"Kai! Kai! Ya Junaidu, sunan Babanmufa ka kira".
Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace.
"Au na manta ashe sunan surki nane".
Kai ta gyaWa mishi kana tasa hannu ta amshi, nonon inabin da yake mi?a mata,
baki ta buWe da nufin sawa a baki,
sai kuma ta tsaya tare da tura baki jin yana ce mata.
"No kada kici ba'a wonke bafa."
Sai kuma ya ajiye kondon, ya amshi inabin ya Wan gangara, gefe kaWan ya wonkeshi a bakin ruwan wutsiyar Kogin da yayiwa Rugar tasu ?awanya.
Ya tahowa tana kallonshi.

Koda ya iso mi?a mata yayi,
kana ya Wauki kondon, ganin still tanata kallonshi ne ya sashi cewa.
"Ya dai?".
Kai ta kauda tare da fara tsinkar ?a?an inabin tana afawa a baki tana taunawa,
Murmushi ya kumayi ganin yadda ta lumshe idonta.
A hankali tace.
"Ya Junaidu kayi kyau sosai yau, har kamar ka fini kyau".
Dariya ya Wanyi kana yace.
"Yo dama ai na fiki kyau".
Ma?e kafaWa tayi tare da cewa.
"Uhum a a kam".
A haka dai suna tafe suna hira.

Can cikin gida kuwa, Ummiy ce zaune bisa kujera ?ar tsuguno da buta a gabanta, alamun al'walan sallan walaha, zatayi.
Inna kuwa, da wasu ma?otansu uku Biba, Hari, da Innawuro. suna zaune bisa taburma a tsakar gidan. Suna amsar gaisuwa.

Can cikin garin kuwa su Alhamdulillah Manu dasu Siddine da dai sauran dattawan garin ne zaune a fada.
Sai yara daketa kai komo.

Da sauri su Siddi suka mi?e tsaye ganin, matasan maya?an ?abilar Sachama, sunata shigowa garin tako ina gabas da yamma kudu da Arewa, bisa dukkan alamu zobe sukayiwa garin
Kana ga zurma-zurman makamai masu tsawo tamkar ra?umai. Sai she?i sukeyi.

Cikin Waga murya, Alhaji Manu yace.
"Kai lfy? me haka?".
Ganin sun nufosu gadan-gadan ne yasa, suka mi?e gaba Wayansu, kowa ya fara, neman makari, to amman ina, basu da zato ko sanin za'a far musu, shiyasa basu da shirin komai na kare kai.
?aya daga cikin sune, yace.
"Mu gudu kashemu sukeda shirin yi ba tare da laifin komaiba".
Siddine ya kuma Waga murya tare da cewa.
"To in mun gudu matanmu da yaranmu fa".
Ihun da sukajiyo tako wani sashi na garinne ya tambatar musu, ana karkashe su.
Gudu suka farayi kowa ya nufi hanyar gidanshi dan Waukar matakan kare kai.
Sai dai ina basu da hanya duk inda suka Sullo sai sunci karo da, maya?an.

Lokaci Waya garin ya ruWe ya birkice kota ina sai ife-ife da gudun ceton rai da makiyayan Rugar Kikan keyi.

Wani irin sauti mai baiyana azabar fitan rai Alhaji Manu yayi, lokacin da wani kafurin ya caka mushi sitaka a ?ahon zuciyarshi.
Siddine ne ya juyo da azaban razani, amman sai shima ya saki wani sauti mai gigitarwa jin azaban sara da sukan da akeyi mishi.
Garifa ya kacame,
Hadi ne babban Wa ga Alhaji Haro mahaifinsu Junaidun Junainah, ya nufi cikin gidansu da azama,
Yana cike da fargaba, da tashin hankali domin wasu irin ihu da yake jiyowa a cikin gidan nasu.
Yana kusa kai ya samu, makasan suna cike a gidan.
Suna ta'addanci, sun kashe kowa na gidan.
Ganin haka ya juyo yana juyowa. Yayi kiciSis da abokinshi Sale, yana tafe jini na zuba an farka mishi ciki.
Cikin magagin mutuwa yake cewa.
"Hadi sun kashe kowa na garin nan sai wanda baya nan.
Hadi na kira Hukumar yan sanda ta nan cikin Numan na shaida musu, amman kafuran nan ma?iya Allah da Manzonsa sai cewa sukayi,
A kashe mu mana, ai an rage musu aikine.
Na kira su ArWo Bani, suna Wagawa katin wayata ya ?are.
Hadi sun kashe kowa na gidanmu.
Taroshi Hadi yayi suka faWa nan suna kuka mai cike da taraddadin rabuwa.
Cikin ?arfin hali Sale ya ture Hadi tare da cewa.
"Ka gudu Hadi ku gudu, Ni nasan bazan rayuba.
Ka gudu.
Sun kashe min Kowa har jariren tagwayen da aka haifa min shekaran jiya, sun kashesu.

Cikin kuka Hadi yace.
"Bazan iya guduba Sale su kasheni kawai, ina zanje bayan sunyiwa garin zobe.
Da ?arfi Hadi ya abka jikin Sale Jin ansa gatari an sari kafaWarsa ta dama,
Juyowar da zaiyi kuma aka tsira mishi mashi a ?irji.
Nan take ya cika, hakama Sale.

Cikin gidansu Shatu kuwa.
Ummiy ta sallame sallan kenan, taji.
Inna dasu Innawuro suna kurma ihu da salati.
Yun?urawa tayi da azama jiki na rawa ta nufo woje.
Fitowanta yayi dai-dai da lokacin da aka sare kan Innawuro, wanda kan yayi tsalle ya faWo kanta, kana ya gangara ya faWa gabanta.
Wani irin ihu mai cike da karaji gauraye da salati ta kurma lokacin d??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a taga an burmawa Inna mashi a ciki.
Ihunta da salatinta ya jawo hankalin su, sukayo kanta.
Sai dai kafin su isoma ta yanki jiki ta faWi babu numfarfashi tamkar matacciya.

Koda suka iso, dariya suka kece da ita cikin rashin imani Wayansu yasa ?afa, ya taka ruwan cikinta, tare da cewa.
"Shegun FULANI ku mutu, mu huta, da ganinku a garinmu, gonakinku da dabobbin ku duk sun zama namu.
Mu Wauke yaranku mata mu maidasu karuwanmu, muyi musu ciki su haihu mu bawa dodo.
Muji daWi dasu.

Ganin kamar ta mutune yasa suka tattakata suka wuce suka fita daga gidan.

Junainah kuwa da Junaidun, suna gab da shigowa garin suka fara jiyo ihun mutanen garin.
Cikin azaban firgici Junaidu ya wurgar da kondon ?a?an itatuwan dake hannunshi,
da gudu yabi bayan Junainah data ruga a guje sabida hango, anata kashe mutane a gabansu.
Cikin kuka da tarin kiWima da fita haiyacinta take cewa.
"Wayyo Ummiy Wayyo Inna Wayyo Bappa, zasu kashemu.
Wayyoooooooo Adda Shatu zasu kashemu".
Ri?o hannunta yayi da ?arfi cikin rawan jiki da murya yace.
"Junainah bazasu kashekiba, zan kareki da izinin ubangiji, zaki rayu, Shatu bazata rasa kowa duniya ba.
Junainah zan zame miki Garkuwa zan fanshi ranki da nawa ran.
Ki zama tamkar yar tsira, Shatu ta zama tamkar yar jarida, ta rubutawa mutanen duniya su karanta, kisan gillan da akeyiwa Fulani mazauna daji.
Da ?arfi yasa hannu ya zaro wukar dake ?ugunshi wanda da ita ya yayyanki nonunan ayaba dasu inabi.
Wayarshi ya kuma zarowa
Ya Salmanu ya kira,
Salmanu kuma dake, kwance a gadon asibitin nan Genaral Hospital Numan.
Wanda bai workeba tun dukan shaWi da ba'ana ya mishi.
A hankali yasa hannunshin ya amsa kiran wayarshi ganin Junaidu ke kiranshi.
Cikin kiWima da firgici Junaidu yace.
"Ya Salmanu, maya?an ?abilar Sachama sun shigo Rugar mu, sunata kashemu, mazanmu da matanmu.
Ya Salmanu Junainah ina son ta tsira, ko dan ran Junainah ka kira mana hukumar yan sandan cikin Adamawa, ina son su iso su ceci Junainah kada Shatu ta rasa kowa a duniya.
Ban saniba ko zan gazawa bawa Junainah tsaro".
Gaba Waya jikin Salmanu rawa da tsuma yakeyi, katse kiran yayi da sauri ya kira.
"A.S.P Kabiru Nasir. Wanda yake, Hetkotan Adamawa.
Koda ya mishi jawabin abinda ke faruwa, a take. A.S.P ya kira.
S.P Daniyel dake Numan ya bashi doka da oda maza-maza su bawa fulanin Rugar Kikan tsaro gaggawa, shima yana nan tafe da rundunar sa. Ya bashi umarni mai ?arfi ya ?ara da cewa, muddin yazo ya samu ba dai-dai ba ta San?aren tsaro, to akan aikinshi.

Wannan abun na umarni daga samane, yasa mugun kafurin nan. Firgita gudun rasa aikinsa, da tonuwar asirinsu da gudun kada a cireshi asa musulmi a kujerarsa, yasa cikin gaggawa ya haWa kan rundunar sa ya nufi.
Cikin Rugar Kikan.

Junainah kuwa wani irin karkarwa takeyi wanda, tuni fitsari ke tsiyaya yana bin sawunta.
Wani irin ihu tayi, ganin wani kafurin ya kaiwa Junaidun sara a bayanshi.
Wani irin juyi Junaidun yayi ya farma kafurin da da wu?arsa dan kare kansa da Junainah.
Duk da su biyar suka zagayesu, basuyi nasara a kanshiba, yana kare kanshi da Junainah, har saida suka tsira daga waWannan.
Sai kuma wasu, mutun takwas suka cimmusu.
Da ?arfi suka ban?aren Junaidun, suka fara kiciniyar zare Junainah da ya ruggumeta da azaban ?arfi da yayi.
Wani irin ihu yasa jin an caka mishi.
Wuka a gadon baya.
Still bai saketaba, sai ya?in kareta da ya farayi, da iya ?arfinshi.
Ita kuwa Junainah ganin an caka mishi wu?ane yasa ta sume.
Dai-dai lokacin kuma rundunar yan sandan suka iso.

Kamar bazasu guduba, dan sun san da bakin hukumar sukeyin aikin, to sai dai ganin musulman cikin yan sandan suna sakin harbine yasa.
Suka ari ta kare.


Daga nan suka rin?a gudu sunayiwa yan uwansu fito alamun su gudu.
Cikin ?an?anin lokaci duk suka gudu.

Su kuwa yan sandan, suka shiga cikin Rugar Kikan Win.
Hankalin musulman cikinsu yayi masifar tashi ganin irin kisan gillar da akayiwa bayin Allah'n nan, kisa na rashin imani.
Nan take suka kira motocin asibiti.
Suka rin?a jidon masu sauran rai suna sawa a motar ambulance suna kai cikin Genaral Hospital Numan.
Kana suna harhaWa gawakin kuma a tsakiyar garin.
Cikin mintuna talatin rundunar A.S.P ta iso.
Tare da yan jaridu.


Su Bappa kuwa. Koda suka gama tattaunawa da Maimartaba, sai ya umarci Waziri daya hanasu tafiya a bisa adalcinsa.
Yace su tsaya suci abincin rana, kana suyi sallan azahar kafin su tafi.
To haka yasa suka zauna.
Waziri yasa akayi musu duk ihsanin da Maimartaba ya bada umarnin ayi musu.
Sukaci abinci sukasha, Sannan sukayi sallan azahar.
Daga nan aka sallesu suka tafi.

Tuni cikin gari kuwa gidajen rediyo sun Wauka, batun faWan FULANI makiyaya da ?achamawa manoma, wanda akaso a juya rahoton da cewa makiyayan ne sukayiwa manomanne Sarna.



Bayan. Tafiyan su Bappa da kamar 30 minutes ne. Labari abinda ya faru ya riski Maimartaba.
Nan take yasa Waziri da Galadima da hadimai mutun ashirin suka nufi cikin Numan dan suje su tabbar da abinda akace Win.

Su Bappa kuwa, sam basuji lbrinba saida suka isa cikin Numan.
Ganin garin a hargitse ne yasa ArWo Bani ya kalli Bappa da Alhaji Haro da suke gefenshi cikin mmki yace.
"Lafiya kuwa? Meke faruwane a garin nan?".
Cikin kaWuwa suka haWa baki wurin cewa.
"Allahu alamu".
Drivern nasune, ya kallesu a tsorace yace.
"Anya kuwa yau ba faWa akeyiba a garin nan ba".

"Kai ba lfy ba kam!".
Cewar Alhaji Umaru
Shi kuwa Drivern, bakin titi ya Wan gangara ya tsaya, ya tambayi wasu yan agaji daketa.
Shiga cikin wani babban Pharmacy da alamun magunguna suke saya,
koda suka mishi bayanin abinda ya faru.
Jiki na rawa yazo ya sanarwa su ArWo Bani.
Lokaci Waya hankalinsu. Yayi masifar tashi.
Nan sukace ya wuce dasu.
Asibitin.

Koda sukaje hanasu shiga akayi.
Hakane yasa, sukace to ya

28 / 72