Garkuwa 1 Complete Hausa Novel

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Romance

Chapter   23 / 72

66K to 69K   out of 214K words

Lami Bubayero jikan LamiWo JoWa zaiyi mgna".
Wani irin harara suka watsawa Danzagin, shi kuwa LamiWo cikin nitsuwar datattaku tace.
"Da farko dai zan fara da baku ha?urin zalumcin da akayi, muku, Allah ya ji?an wanda suka rigamu gidan gsky."
Da ?arfi ?anzagi yace.
"Amin". Su kuwa dattawan ido kawai suka zuba mishi.
Shi kuwa LamiWo a hankali yaci gaba da cewa.
"Ina mai baku ha?uri da kuma umarnin kada kuce zaku Wauki mataki domin ramuwa."
Kamar daga sama sukaji Muryar Bakur yana cewa.
"Babu wani sarkin da ya isa ya hanamu Waukar fansa sai, Ubangijin daya busa mana, numfarfashi".
Da ?arfi Wani dogarin ya Wago zabgegiyar bulalarshi ya zabgawa Bukar.
Wanda saida yayi tsalle ya kurma ihu.
Cikin tsauri LamiWo ya Wagawa duka fadawanshi da hadimanshi da dogara shi hannu alamun kada su sake dukan kowa.
Saura su Waziri kuwa duk shiru sukayi,
Jabeer kuwa, a hankali yaci gaba da tasbihin da yakeyi, sabida danne abinda yakeji zuciyarshi nayi.
Shi kuwa LamiWo cikin sanyi ya fara mgna, dan yasan zafin rashin da sukayi ne yasa sukace sai sun rama, a hankali ya kalli fuskokin dattawan da yasan sunje mishi har fadanshi dan neman zaman lfy, cikin kula ya kalli ArWo Bani tare da cewa.
"ArWo Bani zaku ha?ura, hukuma da masarauta ta bi muku kadun cutar damu da akeyi, ko zaku Wauki makami dan ramawa?".
Cikin tarin kufula da harzu?a da kuma son cinma wata gagarumar manufar da ya daWe yana fatan ya samu da sai yau, fuska a haWe yace.
"Babu wani wanda zan kuma hana Waukan makami,
Dan kare kanshi da ramuwar kisar gillan da akeyi mana."
Cikin tarin Mamaki da al'ajabi Bappa da sauran dattawan suka buWe baki tare da kallon Ardo Bani, Jabeer ma idon ya buWe cikin sanyi yace.
"Baba Ardo kayi ha?uri, muyi aiki da al'?alami, domin al'?alami yafi tokobi, ina nan inata shirin samar da tsaro na musamman kan FULANIN ?asarmu da nake shugabanta."
Cikin nuna tsantsar fushi da son fusata LamiWo ArWo Bani ya dakawa Jabeer tsawa tare da cewa.
"Kada rufe min baki, meka sani akan Fulani? Me ruwanka damu? Damuwarmu ta shafeka ne? Ina kake sanda ake kashe mana mata, yara, jikoki, mu kanmu bamu tsiraba, in munje mun kai kukanmu a koremu tamkar karnuka, sabida duk baku san darajar fulani ba."
Cikin sauri ?anzagi yace.
"Hattara dai ?aramin Ardo, wannan sarkine na fulSe masarautar filSe ce gaba da bayanta".
Cikin Waga Muryar Ardo Bani yace.
"Tafi can ba?in bawa, bawan banza bawan wofi mai ka sani ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?kan fulSe, meka sani banda bauta da fadanci, masarautar da kuke bautawa bata san menene fulSe ba".
Cikin sauri Waziri ya yun?ura zaiyi mgna, da sauri LamiWo ya dakatar dashi, sabida zuwa yanzu zuciyarshi ta fara tafasa, yaya daga kawowa mutane ziyara dan ja-jantawa suke neman tozarta mushi masarauta. Cikin Sacin rai ya kalli su Bappa daketa kama hannun ArWo bani daketa fizge-fizge yana kwaza musu ba?ar mgna, cikin fushi yace.
"Masarautar JoWa Wince bata fulani ba?".
A harzu?e ArWo Bani yace.
"Tabbas dan data fulanice, da an bamu kariya da tsaro, da an duba kukanmu, a kashemu a hanamu Waukar fansa, an kuma kasa bamu tsaro. Nan da mukaje ina shi jikan naka da yake matsayin Garkuwan Fulani, yana can ?asashen woje, da iya dukiyar da ake bashi tsaro da kariya shi rai Waya ta kai a kula da fulanin daji dubu a kuma basu tsaro.
Yau kwana uku da kashe mana mutane sai yau zaku Webo manyan riguna kuzo mana da batun wai kada mu rama, sara da suka da yanka mana mutane da akeyi,
Kaida kab zuriyar ka da masarauta ka, babu mutun Waya da zai iya jurar koda bulalar *(SHA?I)* ma bare sara da yanka da suka da wu?a a hakan kuke ganin kanku Fulani".
Cikin tarin zafin ?una da tafasar zuciya Waziri yace.
"To me kuke so muyi muku, tun randa akayi abun munzo bamu sameku ba".
A harzu?e Bukar yace.
"?arya ne babu wanda yazo".
A hankali Jabeer ya buWe baki da nufin zaiyi mgna sai yaji LamiWo na cewa.
"Uhum jinina kuke cewa ba fulaniba, to ko jaririn da aka haifa yau a jikin masarautar JoWa zai iya jurarar bulalar SHA?I bare manya ko Wan baiwa zai iya bare jinina ?a?ana ko jikokina, ko kun manta masarautar JoWa ce tushen ShaWi?".
Cikin son harzu?a LamiWo ArWo Bani yace.
"A da can baya ba, yanzu kuma da aka san lusarai ake haifa a masarautar inji an haramta shaWi a masarautar, yau in kun isa fulani ka bada Wan ka ko jikanka ayi gasar ShaWi dashi, in ya iya jurewa, to mun yarda mun gamsu ku fulanine ku masarautar Fulani, in kuwa kun kasa fidda goninku to, ku ba masarauta fulSe bace."
Wani irin karkarwa jikin LamiWo ya fara sabida fusata, wai suda masarautarsuce tushen fulSe a ?asar, su ake cewa ba fulani ba, har ake kiransu lusarai, Galadima, Waziri, Wambai, ?an iya, ?an buram, ?an Maliki, Sarkin Dawaki.
Gaba Waya hankalinsu yayi masifar tashi sabida ganin tsananin fushi da tashin hankalin Sarki LamiWo.
Jamil Jalal Haroon kuwa , hankalinsu na kan Jabeer bisa alamun yana cikin wani hali.
Shi kuwa Jabeer bugun da zuciyarshi keyi ne yasa,
Hankalinshi tashi, ?arfin addu'o'in da yakeyi ne, yashi iya fahimtar abinda suke cewa.
Kamar daga sama kamar cikin mafarki, sukaji murya LamiWo na cewa.
"Ga jikana, Jabeer GARKUWAN FULANI, na badashi a matsayin matashi mai yin gasar ShaWi ku fito da duk gwanin da kukega shine makurar gwayen yankinku. Ayi ShaWi dashi yadda zaku samu gamsuwar yakai matsayin ya kasance GARKUWAN FULANI".
Tunda ya amSaci sunan Jabeer, Sarkin Fada yayi wani irin murmushi mai cike da jin daWin alamun burinshi zai cika.
Hakama ArWo bani wani irin asirtaccen murmushi yayi.

Jala, Jamil, Haroon, Hashim, Imran, Galadima, kuwa wani irin zazzaro ido sukayi.
Cikin tsananin kaWuwa da firgicin batun LamiWo suka zuba mishi ido.

Bukar kuwa cikin karaji yace.
"Ba'ana Bukar shi zai kara dashi."
Ya ?arishe mgnar da fatan Ba'ana ya kashe wanda aka kira da Jabeer tunda jikan LamiWo ne.

Jabeer kuwa wani irin kallo yayi kakan nashi, irin kallon nan.
Na lallai kam tsohon nan ka haukace, ka zauce, ai bani bakam ko inuwata bazaku kuma gani a garinkuba bare kuyi wannan gwajin dashi.
Ga mamakinsu kab sai sukaji ArWo Bani na cewa.
"A yau Winan kuma Yanzun nan, a kuma nan za'ayi gasar ShaWi in har kun isa fulani."
Sosai LamiWo yaji hakan bai mishi ba dan a zotonshi za'asa ranane ya koma ya shirya Jabeer kafin ayi gasar, to fahimtar ?uresu suke neman yi, yasashi gyara zamanshi cikin danne fargabanshi na anya Jabeer zai iya jura yace.
"Na Aminc....!



Yau bisa wani uzuri ban samu yin posting da wuriba, kana kuma ba editing a gurguje na watsoshi, bari in nemo PAGE 16 ko zuwa yan da yamma ne.


By
*GARKUWAR FULANI*
=???
=??=?J?????=?
?>?4?
*GARKUWA*

PAGE 16

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

=??????>?4?


*FREE PAGE SUN ?ARE DAGA WANNAN PAGE 16 DIN IN DAI KIKAGA LITTAFINA GARKUWA BA TARE DA KIM BIYA NA SAKI A GROUP BA TO NA SATANE, DAN ALLAH DA MANZONSA KADA KU FITARMIN DA LITTAFI DAN ALLAH KU BARI IN SAMU KU?I zuwa makka=??=??=??*


*Littafin GARKUWA na kuWine dan Allah da Manzonsa kada ki karanta na sata, kada ki watsamin littafi a sata, turo katin MTN na Wari uku kacal ta wannan number 09097853276 ki biya ki karanta cikin aminci ba tare da ha??i naba. Ko kuma ki biya 1k domin shiga Special Group wanda cikin sati biyu rak za'a gama Part 1, da izinin ubangiji kana a shiga 2, turo dubunki Waya ta wannan asusun 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidan biyanki ta wannan number 09097853276 in baki da halin biyan dubu Waya ko baki da ra'ayi kina iya turo Warinki uku kacal da ban tsauwalaba sabida halin rayuwa da muke ciki. Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki sai littafina in dai kin san niyarki ki saya ki fitar da shine in kuma. Har kin sayane to dan Allah da Manzonsa gaya min in baki kuWinki in cireki a group na, dan Allah=?O?

"Na Amince!". Cikin tarin mamaki Jalal, Jamil, Imran, Haroon, Hashim, da duk sauran tawagar LamiWo suka, zazzaro ido cikin tarin mamaki da al'ajabi, sam basuyi zaton jin haka daga gareshi ba,
Ya Salmanu kuwa wani irin farin cikin mara misaltuwa ne, ya rufewa, domin yana ganin ikon Allah da yake nuna mishi zahirin abinda yake nuna mishi a mafarkansa tsawon kwanakin da yake a gadon asibiti.

Ba'ana kuwa da tun Wazu ya iso, wani irin ihu yayi mai cike da farin ciki, da jin daWin yana ganin zaiyi abinda gaba ko kashe mutanen Rugar Bani sukayi gaba Waya, masarautar JoWa bazata kulasuba,
Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi sabida azabar muguntarsa dake tasowa.

ArWo Bani ma wani murmushi manufa yayi tare da cewa.
"To, ina gwanin naku?".
Cikin karaWi ?anzagi, ya kalli Jabeer tare da cewa.
"Malami ba faWen Allah, malamai magada annabawa, Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero JoWa, GARKUWAN sarki LamiWo, jikan sarki, mai martaba Nuruddee. Jarumin Masarautar JoWa."
Gimtse bakinshi yayi ganin wani irin kallo mai ma'anoni da yawa da Jabeer ke watsa mishi,
Cikin yin ?asa da murya tare da tsuke fuskarsa, ya Wan ron?ofo kanshi, kusa da LamiWo murya a kausashe yace.
"Wannan tatsuniyar da kukeyi, bafa koyarwan shariya bace".
Da sauri LamiWo ya katseshi da cewa.
"Eh amman koyarwar Masarautar JoWa ce".
Cikin kufula yace.
"Ya ina ce maka Allah kana cemin gadon masarautar JoWa ce".
Cikin haWe fuska da ?asaita LamiWo yace.
"Eh ba addini bane, kuma sai an yishi dan gadon masarautar muce".
Kanshi ya kuma motso dashi jikin kakan nashi cikin taSe fuska yace.
"Okay to ai sai ka tashi, ka tsaya su zaneka ciki da woje".
Cikin kausasa murya LamiWo yace.
"Kai ne dai zaka tashi".
Cikin watsawa kakan nashi wani kallo na lallai ma tsohon nan kanka ya kwance yace.
"Ai bani bane sarkin, kaine sarkin ko?".
Cikin faWa LamiWo yace.
"To ko Ubanka bai isa in sashi abu yace bazaiyi ba".
Jin muryar LamiWo ta Wan yi samane, yasa fadawanshi suka mi?e tsaye,
Ware rigunansu sukayi, suka kamgesu da jajayen rugunan nasu, ta yadda babu mai ganinsu,
Cikin haWe fuska Jabeer yace.
"Yesss shi bazai ?iba, tunda kai ubanshi ne, Ni kuwa babu wanda zai sani in zauna in bawa wani ?aton fatar jikina ya zane, kai jimin zancen son zuciya, kai ni kaWaine jikanka, a duniya, a nanma baga Ya Hashim ba ai shine babban jikanka, zancen gsky na gaji da wannan tirsashe-tirsashen naku, kanada ?a?an ai, ka kira Waya daga cikin ya'yan ka yazo ya wakil ceka mana, Amman ni dai kam Muhammad Jabeer babu wani tsohon da zanyiwa mubaya'a in tsaya wani gardin makiyayi ya Wimeni, tunda ba faWin Allah bane".
Ya ?arishe mgnar yana yun?irin tashi tsaye.
Da sauri Galadima yasa hannu ya kamo nashi, fuskar ya kwaSe tare da komawa zaune yana gyara hiramin kanshi da al'kyabbar jikinshi,
Cikin tausasa harshe Galadima yace.
"Jabeer kafa san ma'anar GARKUWA a masarauta."
Cikin sanyi da ganin kima da darajar dottijon Jabeer ya kwaSe fuska tare da cewa.
"Nifa shiyasa wannan mulkin bawai sonshi nakeyi ba, sabida wannan tsarabe-tsaraben daba na addiniba, a buwayi mutun dashi, yaya nasan abu ba Allah ne da manzonsa suka wajabta mana shiba, ace in zauna a cutar dani."
Cikin sanyi Waziri ke jujjuya mishi kai a hankali yace.
"Jabeer Garkuwa fa, kake dole ka kare martabar Masarautarmu kana ka nunawa su fulanin da kake Garkuwarsu kai Jarumine".
Rai a Sace ganin sufa da gske sukeyi, cikin dakiya yace.
"Bana so, ita wannan sarauta ta GARKUWAN FULANI ku bawa duk wanda kukeso, ni ban nemaba dama".
Shiru Haroon yayi dan gskya harga Allah shi wannan abun yazo masa a bazata.
Jalal kuwa cikin haWe fuska yace.
"Wannan ma ai zancen banza ne,
An bawa Ya Jafar Galadima, ko kwana ashirin baiba a kai, aka birkita masa rayuwa, kana yanzu kun likawa Hamma Jabeer wani GARKUWA kun kwasomu kun kawomu Rugar fulani, wai kuna cewa ayi gasar duka dashi."
Da sauri yayi shiru ganin Jabeer ya Waga mishi hannu.
Jamil kuwa tuntuni idonshi ke tsastsafo ruwan hawaye dan gani yake so ake a kashe Hammansu a ?arar da ?a?an Wakinsu,
Laminu kuwa Wan Gimbiya Saudatu matar bappansu Sheykh kuma Kani ga Yah Hisham wani irin dariyar jin daWi yakeyi.

Shi kuwa LamiWo, wayarshi ya zaro, Mai alfarma Sarki Jalaluddin ya kira wanda yake kane ga Jabeer. Wanda ya haifi Mamanshi.
Bayan sun gaisane yayi mishi bayanin abinda ke faruwa, jin haka yasa yace ya bawa Jabeer wayar.

A tsakar filin Rugar Bani kuwa, tuni.
ArWo Bani ya bada dama na suduka yana shekantawa gari cewa.
Ana gamgamin ShaWi yanzu-yanzu tsakanin Ba'ana da kuma jikan Sarki Nuruddeen.

Tuni an firfito da ganguna anata kaWe-kaWe da bushe-bushen sarewa, kana ana buga babban gangan dake tsanar da makotan Rugar Bani sauran rugage alamun za'ayi ShaWi yanzu.

Kafin kace kobo, Rugar Bani ta cika tayi ma?il da mutane, Maza da mata, matasa da tsoffi, sabida an san duk sanda za'ayi ShaWi ana bada sanarwar, kwana uku kafin nan to jin wannan na gaggawa kuma da jikan Sarki za'ayi yasa, mutane taruwa, gashi ranar jumma'ace, duk matasan rugogin suna, gida tunda suka dawo sallan jamma'a.
Rugar Bani ta cika tayi ma?il da bani adam, tako wacce kusurwa tsastsafo akeyi kusufa-kusufa.
Jin karan tamSarin ganganr ShaWi ne ya ?ara gaiyato mutane harda na cikin garin Shikan, tuni ?abilun Bonon sun garzayo cikin Rugar Bani.

Bukar kuwa mahaifin Ba'ana shida kanshi yaje, cikin Garkensu ya Wauko tukunyar tsumin bulalim shaWin da Ba'ana ke tsumasu da dafin kunamai da sauran sihirurruka, na dodon tsafinsu Bonon.

Matasa majiya karfi ne keta Webo ruwa, cikin rijiyoyin garin.
Suna ji?a taron wurin dandamalin, da za'ayi gasar kaWe-kaWen duk sun taru sun cika kunnen kowa.
Jabeer kuwa bugun da zuciyarshi keyi shiyafi komai tada mishi hankali.

A can cikin gidajen Rugar kuwa, duk yan samari da yara sun firfito.
A gidansu Shatu kuwa,
Tunda taji Shelan da Nasuduka yakeyi cewa gasar ShaWi tsakanin Ba'ana da jikan sarki.
Kuka ta farayi, cikin tashin hankali da kiWima ta kamo hannun Ummiy da tayi shiru sai ido take binsu dashi, murya na rawa tace.
"Ummiy kijifa, zasuyi ya kashe, wani wanda baijiba bai ganiba, sunfa san illar dake cikin bulalinshi."
Ganin Ummiy dai ba mgna zatayi ba, yasa ta kamo hannun Junainah cikin tsananin tashin hankali tace.
"Junainah ki gudu, kije kicewa Bappa kada ayi gasar nan, Ni dai a bari na ha?ura zan auri ya Ba'ana a yadda yake, zan zauna dashi, zanyi ?o?arin gyara mishi, rayuwa na gaji, kada a sake cutar da wani a kaina".
Da sauri Rafi'a ta kalleta jin ta kamo hannunta cikin zubda hawaye tace,
"Rafi'a wlh ya Ba'ana zai iya kashe mutun a kaina, da dafin kunamai yake tsuma bulalinshi, da wani tsafin, me ribata ayi ta cutar da mutane a dalilina, babu fa wani mahalu?in da zai iya cin Ya Ba'ana gasar ShaWi, babu wanda zai iya jurar azabar bulalinshi fa."
Cikin sauri ta mi?e tare da mi?ar da Junainah, sai kuma duk suka koma suka zauna,
Jin muryar ma?ocibsu Sarkin aska, yana cewa.
"A a Shatu kada ki tura kowa, kada kuma kije kin tsumayi sakamakon gasar yau in sha Allah zata banbanta da na baya .
Yanzu ma ArWo Bani ne ya aikoni da in gargaWeki."
Yana faWin haka ya juya da sauri ya fita, kana ya nufi wurin gasar.

Da ido suka bishi. Ita kuwa Junainah da sauri ta mi?a ta nufi kitchin Win su, tana cewa.
"Yauwa Adda Shatu, barin in kawo mana gasassun zabbin da Ya Ba'ana ya kawo mana muci.
?azu da nace muci Adda Rafi'a ce, tace mujiraki."
Cikin sanyi Rafi'a tace.
"Yauwa Junainah kawo mana, muci yau tunda gari ya waye bamuci komaiba."
Gyara zansu sukayi, kana ta kalli Shatu cikin kula tace.
"Dan Allah Shatu muci abinci, kinga Ummiy ma ta?i cin komai ganin, yadda kiketa kuka tunda kikaji Satansu ya GiWi da rasuwar Ya Lado da Inna."
Cikin zubda hawaye ta gyaWa mata kai, sabida ita kanta tasan tana jin wani irin masifeffen yunwa, tamkar zai kasheta.
Da sauri Junainah ta nufosu ri?e da akoshin gasassun zabbin da aka zuba dafin macijin a cikin.

A can cikin tsakiyar garin Rugar Bani kuwa.
Tuni su Ba'ana an gama shiryawa zalumci, domin dama ai a ?a'ida shi zai fara duka,
Yana tsaye sai zagaya filin yake yana zane iska, makaWa da mabusa nata yi mishi kirari.

A cikin wurin da Fadawa suka kange LamiWo da tawagarsa kuwa, anata kai ruwa rana da Sheykh Jabeer,
Cikin kufula, yake cewa Sarki Jalaluddin da suke waya dashi.
"Nifa babbar matsalarta wannan abun da za'ayi ba *Sunna* bace ba kuma *Farilla* bace, ba kuma *Mustahabbibace*, kai ko a babin *Makaruhi* ban taSa cin karo da wannan banzar al'adar da kukeso in yarda ayita dani ba,
Ina kuma da ya?ini in da zan bajeta a babin musulunci, kai tsaye za'a iya karhantashi, sabida ai cutar da kaine kuma, Musulunci bai yarda mutun ya cutar da kanshi ba, haka kurum kuce wai in tsaya a zaneni, inji shi kanshi kakan LamiWon JoWo da yaji haza a gasar ShaWin shine ya hana wannan al'adar a masarautarsa sannan yanzu ace za'a saketa a kaina bayan tsawon shekaru 145 ba'ayishi ba, tun zamanin jahiliyan ma an bar abu sai yanzu ku tara abu a kaina, to wallahi bafa zai yiwuba."
Cikin kufula Sarki Jalaluddin yace.
"To ya kakeso ayi Wan masu ilimi kowa jahiline sai kaine mai ilimi sabida tsabar tsoro da Wan karen son jiki kana gudun abinda zai taSa lfyarka shine zakayi ta jawo mana wasu dogin falsafofi, a hir Win kafa Jabeer ko uwarka bazan sata abu taimin musuba".
Gaba Waya sun hautsuna mishi zuciya,
Ji yadda suketa zageshi, dan kawai yace bazaiyi abinda al'adace ba addiniba sai wani ce mishi suke ko uwarka ko ubanka, bayan sun san baya kuran hakan, rai a Sace yace.
"Uwata kace ai tunda ita ai ka haifa ba niba

23 / 72