Garkuwa 1 Complete Hausa Novel

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Romance

Chapter   11 / 72

30K to 33K   out of 214K words

murmushi tace.
"Gasheshen naman tattabarune Ya Salmanu barima in koma ciki inci rabona inci na Addana".
Kafin ya ankarama tuni ta juya da sauri tayi cikin gida.


Ajiyan zuciya ya sau?e tare da kallon Aysha dake jingini da bakin kofar zauren,
Cikin sanyi yace.
"Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?".
A hankali tace.
"A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kin rama kena".
Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace.
"Ga wuri kizo ki zauna mana".
A hankali tace,
"A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana".

"Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?".
Salmanu ya faWa a hankali.
Da sauri tace.
"Eh".
Kanshi ya Wan rausayar tare da cewa.
"Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?".

A hankali ta zauna gefenshi Wan nesa dashi.
Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace.
"Gaya min me kike tsoro?".
Kallonshi tayi cikin yin ?asa da murya tace.
"Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar ala?armu ya zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana son abinda zai cutar da kai".
Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace.
"Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan ta?adirin, domin baki cancanci zama matar mushurkiba".
Da sauri tace.
"Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare mgnar ta koma kunnenshi".
Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buWe. Numfashin yaja jin ?amshin naman a hankali ya fara ci, saida yaci Waya kab sannan ya rufe kwanon yace.
"Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon".
Cikin yanayin nitsuwarta tace.
"A a kaci kawai Ya Salmanu".
Da sauri yace.
"No kada kimin musu".
Shiru tayi jin yaci gaba da cewa.
"Muddin dai ina raye in sha Allah.
wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk azabar da zai shayar dani na shaWi in Sha Allah zan aureki".
Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu.

A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da budurwarshi suna Wan hirarsu
Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin komai.

Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa.
"Ummey".

"Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba mata,
ganin hakane yasa a hankali tace.
"Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru,
Cikin kulawa da sha?uwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace.
"Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?".
Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace.
"Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa Baba ArWo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?".
Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa.
"To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi".
Kai ta juya tare da cewa.
"Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko".
Murmushi Ummey tayi kana tace.
"Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki".
da haka suka konta bacci.

Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu, dan yanzu yanayin sihirinshi ?aruwa yakeyi sosai,
Wasu lokutan ba hawa ba sau?a sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan Satarshi tama fi ta baya ?arfi, ya dage wai zai bawa Shatu ta?i fir daya matsama kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta.

Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda zai faru ya hana yarda da kowa, gaba Waya kuma yanzu ?abilar Sachamawan nan masifa tu?uru suke neman fulanin Bani dashi sabida ba?in ciki da hasadar ganin yadda shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake, gyaWa, gujjiya, riWi, da dai sauransu.

Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma.
To waWannan abubuwan sune suke ?ara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da al'barkasu a jikinsu.

Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi shaWi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin ba.
Kowa in yaji da Salmanu za'ayi ana tausaya mishi domin shi mutunne mai laushin jiki shiyasa tun yana ?araminshi aka meda hankali kan karatun da yakeso, hakane yasa yayi karatun shi yanzu haka yana zama cikin Shikan ne inda yakeda shagunan kayan tireda sabida bazai iya noma da kiwo ba, kuma Alhamdulillah kasuwar ta amsheshi. Shiyasa shi zuwa yakeyi Rugar Bani Win.

A can ?asa mai tsarki kuwa,
Yau kwanansu Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da Sittinshi goma da zuwa, to kasan cewar zasu gudanar da aikin Umarne yasa tun randa suka cika kwana uku da zuwa suka tafi, Madina,
Kuma sun bar mgnar batun Jazrah cewa sai sun gama gudanar da aikin Umararsu kafin su shaida mishi, kana in sun dai-dai ta da Jazrah sai su shaidawa Mai alfarma Sarki Jalaluddin, shi kuma yaje har ?adamaya ya shaidawa mai daraja sarki Nuruddeen Bubayero, da kuma Habeebullah, batun auren in yaso su shirya suzo ayi Waurin auren.

To yau kwanansu takwas a Madinah kuma yaune suke shirin dawowa makka.

Kullum sai sun gaisa dasu Hajia Mama dasu Jalal.
Kullum yakan kira Juwairiyya.

Da maraicin suka isa cikin Makka kai tsaye masarautar suka wuce.

Bayan sun gaggaisa, Sheikh Aliyu yace suje su huta, kafin su gaisa da Sheykh Abdulkareem domin yana tare da manyan ba?i.

Haka kuwa akayi, bayan duk sunyi wonka suka dawo falon Sitti.

Suna zaune cikin shiga ta al'farma a wuri na al'farma, an zagayesu da dukkan kayan jin daWin rayuwar duniya,

Sitti na zaune bisa tsakiyar falon akan wani tattausan carpet, Jannart da Jazrah suna gefenta, cikin shiga ta al'farma,

Sheykh kuwa zaune yake bisa wata lumtsimemiyar kujera kana sawunshi na kan wasu tim-tim masu masifar kyau da taushi, wasu kyawawan larabawane guda biyu suke zaune a gaban Sitti sawunta dake bisa tim-tim Win sukeyiwa tausa.
Yayinda wasu hadiman kuma ke shirya musu ababen ci dasha dangin yayan itatuwa kamarsu, Inabi, tupa, ayaba, dabino, gabaruwa, sai zam-zam kana, saisu shawarma and pizza da kuma wasu irin manyan Foodflaks da aka cikasu da dan?awa-Wan?wal dajaja sai sauran abincinsu na larabawa.

Haroon kuwa gefe yake kusa da Jannart suna Wan taSa hira.

Wayarshi ce ta fara ringgin a hankali, idonshi ya Wan juya ya kalli wayar ba tare daya juya kanshiba,
Da idonshi ya nunawa hadimin dake gefenshi wayar,
da sauri ya Wauko wayar ya mi?a mishi, ganin Hajia Mamace ya sashi amsa kiran.
Kara wayar yayi a kunne cikin girmamawa yace.
"Barka da dare Hajia Mama".
A can gida kuwa cikin wani irin salo na musamman Hajia Mama ta rufe idanunta tare da cewa.
"Uhum ka manta Jabeer mu nan yammane".
Idonshi ya Wan Wago ya kalli agogon dake jikin ginin, a hankali yace.
"Haka nefa Hajia Mama. Ya gida yasu Jalal".
Murmushin jin daWi tayi tare da cewa.
"Suna lfy gasuma nan kusa dani, Jamil ne ya tsokano Jalal shine suka shigo sunata muzurai".
Kanshi ya jingina da jikin kujerar, a hankali yace.
"Hajia Mama kiyi musu faWa kice su barifa sun girma".
Murmushi mai sanyi tayi tare da cewa.
"Na gaya musu sunma daina gasu nan sunata hira kuma".
Gyara zamanta tayi kana taci gaba da cewa.
"Ina Sitti na?". A ta?aice yace.
"Gata nan kusa dani".
Cikin yanayin jin daWi tace.
"Bata waya". To yace kana ya mi?a Sitti daketa kallonshi wayar, da sauri ta amsa tare da karawa a kunne, murmushi tayi jin muryar Hajia Mama na cewa.
"(Allah beddu sabbugo Sitti), Allah ya ?ara nisan kwana Sitti". Amin Amin tace, kana suka gaisa cikin tsananin jin daWi.
Bayan sun gama wayarne kuma Juwairiyya ta kira Jannart nan suka gaisa ta bawa Sitti wayar hirar tasu kab kan ya Jafar ne. Saida suka gama wayarne ta kalli Sheykh dake kishin?iWe ya lumshe ido a hankali tace.
"Juwairiyya tace , yau tun safe Jafar ya shiga sashinka yayi ta nemanka Waki Waki, da bai gankaba ya?i fitowa sai kuka yake tayi, har saida yammane da Jalal ya dawo gida shine ya lallasheshi ya maidashi sashinsu.
Hannu tasa ta share hawayenta da ke kwaranyowa, Haroon ma hawayen ne ke zubo mishi,
Haka Jazrah da Jannart,
Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace.
"LamiWo ya gaya min Wazu da mukayi waya".
Shiru sukayi baki Wayansu, a hankali Haroon ya mi?e kwance tare da faWawa nazari mai zurfi.
Nan kuma kiran Umaymah ya shigo wayar Sitti still hira sukayi sosai wanda ta kontar musu hankali kafin, sukayi sallama da juna.



Yau jumma'a ne gajeren lokacine basa kai yamma a wurin kiwo, kafin azahar suke dawowa, shiyasa yau Shatu tace da ita za'aje kiwo.
Dariya kawai sukayi mata dan sun san ba iya jurewa zatayiba amman tunda ta kafa ta tsare cewa dole zataje, sai aka barta.

Kasan cewar basu kai yamman bane yasa kuma suna tafiya da wuri.
Bayan duk an kunce dabobbin gaba Waya, hakama sauran makiyayan baki Waya, sahu- sahu shanayen keta wucewa.

Sun tafi tun shida da rabi na safe,

Kafin zuwa tara na safe sunyi nisa cikin wurin kiwonsu, inda nan kuma Aysha ta samu su Hindema sunzo kiwo, wanda su kullum dama suna zuwa.

Wani irin hadarine mai ?arfi ya taso daga ?asa, ganin hakane yasa, Gaini kwallawa Shatu kira wacce take can cikin ?an uwanta mata makiyaya, jin shiru bata amsa bane ya nufi wurin da suke zaune,
Cikin kula yace.
"Aysha tashi keda Hinde dasu Mero duk ku tafi gida, kunga hadarine mai ?arfi ke tasowa daga ?asa da alamun za'ayi ruwa mai ?arfi".
Cikin ?arfin hali da son wasa cikin ruwan da taketa hari murya a sanyaye tace.
"Ba komai ya Gaini zamu jiraku ai lokacin tashi kuma ya kusa ko?".
Su GiWi dasu Aro da sauran makiyayan ne sukace.
"Ya Gaini barsu mana ba kiwo zasuyi ba ai makiyayin shanu da tumaki baya gudun ruwa duk yawa shi".
Cikin jin daWi sukace, eh mana,
Shi kuwa Ya Gaini murmushi kawai yayi tare da cewa.
"Shike nan yau zakusha dukan ruwa".
Murmushi sukayi sukace "Babu matsala". daga nan mazan duk suka koma wurin kula da dabobbin nasu da suka du?ufa cin koren ciyawa.

Su kuwa Shatu da Hinde a hankali sukaci gaba da tafiya, sosai tsarin wurin da yanayin shigar suturar dake jikinta yayi tsananin dacewa da ita.
Doguwar rigace irin tamu ta fulani, yadin farine, sai daga samanshi akayi mishi kolliya da zaron huWu, mai color red white, blue, yellow, and green, wanda aka ?awata saman rigar da kolliyar zanen Wawisu, inda daga kafaWunta har zuwa saman ?irjinta, duk an shimfiWa zaren, bisa wuyan rigar mai V.
sai kuma hannun rigar shima duk an zagayeshi da kolliyar,
Kana sai tsakiyar rigar dai-dai kan ?ugunta shima an ?awatashi da wannan kolliyar ulu irin namu na fulanin daji,
Kana sai ?asar rigar can itama an ?awata da wannan zaren.

Sai dogon gashin kanta da yake zube a kafaWunta, yayinda daga saman goshinta kuma tasa, bandana amman irin namu na fulani mai kalolin ?a?an tsakiya, ta zagaye kanta dashi, sai kolliyar da tayi a fuskarta irin ta asalin fulani, a goshinta zanen kan shanu tayi, shaidar cikekkiyar bafulatanace, sai kuma ?asan lip Winta na ?asa zuwa kan Wan gemunta shi kuma taja zane da kuma yin Wigo-Wigo a gefenshi.
Sai wata kekkewar jakar sakan ulun mai kalolin kolliyar jikin rigarta data rataya a hannun damanta, wanda cikin jakar kuma ruwan shantane a ciki sai sassanyan kinWirmo da goran zuma, sai Wan sandar mu ta gado, takalman sawunta irin sau cikin nanne daku mutanen cikin birane kuke masa la?abi da tashi kabi shanu.
Tayi masifar kyau a cikin wannan shigar tamu ta gado, kyau iya kyau farar fatarta ta baiyana tamkar balarabiya gashin girarta ya konta lib lib.

A hankali suke Wan tattaki a cikin dogayen saunukan, da koriyar ciyawa da tayiwa ?asanshi ?awanya. suna Wan tafe
Suna Wan tsinkar ya'yan kanya da gwandar daji da suke cike da wurin ChaSSulle wato tsada.

Hadari kuwa sai gamgami yakeyi gabas da yamma kudu da arewa, ko ina yayi dib babu motsin komai sai nasu dana dabobbin su,
Iska ta tsaya cak koda ganye Waya baya kaWawa duhu ya kareWe illahirin yankin.

A hankali Hinde ta kalli sararin samaniya cikin tsoron ganin gaba Waya duniyar tayi ba?i??irin ko ina yayi dib, hakanne yasata Wan zaro ido tare da cewa.
"Kai Shatu, kalli sama, fa hadarin nan yayi duhu da yawa gsky mu tafi gida".
Da sauri ta Wago kanta kana tasa hannunta na hagu ta Wan kare saman goshinta kaWan, ware idanunta tayi ta kalli sararin samaniya, wani irin azabebben firgita da tsorone ya rufeta wanda yasa ta juya da azaban ?arfi ta ruggume Hinde dai-dai lokacin, sukaga wani irin tartsatsin azabebben igiyar...!






Dan Allah da Manzonsa in dai kin san zaki sayi littafinane Wan ki fiddashi na ro?eki da Allah da Manzonsa da darajar su. Kada ki saya bana so, ki ri?e kudinki.




By
*GARKUWAR FULANI*
=???

=?J??=?????=?
?>?4?
*GARKUWA*

PAGE 9

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

=??????=?
?>?4?

*FREE PAGE*

*TURO KATIN MTN NA ?ARI UKU KACAL ta wannan number 09097853276 DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA littafin GARKUWA, ba tare da ha??in kowa a kankiba. Akwai Special Group shi kuma na 1k rak, ki turoshi ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai ta WhatsApp 09097853276*


~Ga masu bu?atar kayan gyara na amare, akwai set-set masu kyau, a ?ananan robobi masu sau?in kuWi, akwai kuma na manyan robobi masu zafi, akwiasu dai-dai da tsarin al'jihun mai ?arfi da mai rauni, ina araha ina hana bashi. Koda kuWinka saida rabonka, kayan Kamfani daban dana shago.~

*Al'ummar Hausawa mazauna Saudiya wannan shafin nakune kyauta gareku, domin jiya da yau saida mai zaton babu wasu masu karanta littafi sama daku. Nasha mamaki da sanyin safiya naita cin karo da numbers Win ?asa mai tsarki suna ta antayo min manyan kuWi na ?asa mai tsarki tun ina ?idaya numbers Win +966 har dai abun yaci tura sabida yawansu, ashe daga zauren Umar Maisanyi sukayi ta antayowa gareni. Godiya mai tarin Yawa Umar maisanyi mai Tsakar gida You tube limamin tsakar gida*



Wal?iya mai tsananin haske da tartsatsi wanda saida ya haska gaba Waya, dajin ya zamana, har kana iya ganin inuwar dogayen bishiyoyin wurin da sukayi musu ?awanys.
Wani irin tsoro da firgici da karkarwan ne ya bijirowa Aysha.
Cikin dauriya da sabo da ganin ire-iren irin waWannan ababen a wurin kiwo, Hinde ta kamo hannun Shatu tare da cewa.
"Kai Aysha babu komai fa wal?iyace kawai fa kai".
Sai kuma tayi dariya tare da cewa,
"Uhum a hakan kike tunanin jurar taraddadin da muke gani cikin tsaunuka in muna kiwo".
Janye jikinta tayi daga jikin Hinde, hannun tasa ta tattare gashin kanta dake baje a kafaWunta, tubkeshi tayi cikin, fidda numafashin tsoro take karisa addu'o'in datake tayi a bakinta, a hankali taja da baya ta jingina da jikin ?atuwar bishiyar Gamji dake gefensu, jingina kanta tayi jikin bishiyar gamjin tana jin yadda zuciyarta ke harbawa, pat-pat da azaban ?arfi domin tasan Hinde bata san me idonta ke shirin hango mataba,
ita kuwa Hinde, a gabanta take tsaye ya zamana sun fuskantar juna.
Su Ya Gaini kuwa sun du?ufa kiwonsu kamar dai yadda suka saba, ruwa ko iska ko zafin rana da ?ishi baya kora makiyaye daga kiwo a daji ya dawo gida.
So duk kowa yana yankin da yake bawa dabobbin tsaro, sam basuma hango su Aysha sosai.

Ita kuwa Shatu idonta dake lumshe ta fara ?o?arin buWewa sabida wani irin tashi da taji tsikar jikinta nayi.
Hinde kuwa ido ta zuba mata tana ganin yadda ?irjinta yake sama da ?asa alamun tsananin firgita.
A hankali ta ware manyan kyawawan idanunta.
Wani ?aton curi, dake can bayan Hinde ta zubawa ido sabida wani abu da take gani kamar haya?i yana fitowa ta ?ananan ?ofofin curin. Ita kuwa Hinde bata san meke wakana ba sabida, ita baya ta bawa curin, asalima yanzu kanta ta Waga sama tana shan ruwan dake cikin goranta.

Ita kuwa Shatu so take ta janye idanunta daga kan wannan CURIN amman sai taji ta kasa, bugun da zuciyarta keyine ya tsananta, lokaci Waya jikinta ya fara tsuma da karkarwa zufa mai azabar zafi ta fara tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta.
Yayin da zuciyarta. Ke harba jini one litter. A Cikin ko wanne one second. Bakinta ta buWe da nufun furta addu'o'in dake jere a zuciyarta amman sai taji ta kasa, zuru-zuru tayi da idanunta lokacin da taga wani dogon abu yana fitowa daga cikin babban ramin dake tsakiyar CURIN nan, a hankali ta Waga kwayar idanunta sama tana bin abin da kallo, wani irin dogon numfashi taja, ganin abun nan yana mi?ewa yana yin sama, abun dogo kamar igiya sai dai kuma yanada zane kala-kala red, yellow, green, blue.
Kuma abun biyune Waya a sama Waya a ?asa, cikin ranta take iya ammabaton sunan Allah ganin zahiri fitowar bakan Gizo daga cikin curi Allah ya nuna mata, ras zanen bakan Gizon nan yayi kama da kalolin kolliyar jikin rigarta,
Kanta ta Waga sama, tana bin Bakan Gizon da kwayar idanunta, tana gani har ya haura sama can ya konta a gicciye gabas da yamma kudu da arewa, kana

11 / 72