Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   97 / 100

288K to 291K   out of 299.8K words

yayi kissing lips dinta tukunaya fice.

Maa sakinah data kasa nutsuwa da rashin dawowan bahar din batai bacci ba sai dataji sun dawo ya fice tukuna ta samu nutsuwa ta kwanta tana fatar ma ayi bikin da zaayi idan su Ammi sun dawo bahar din ta tare kowama ya huta.

Washe gari bata tashi da wuri ba kaman yanda shima bai tashin da wuri ba sai guraren 10 suka hadu a gurin cin abincinsa dayaxo da kansa ya dauketa suka tafi acan sukai breakfast sbd daman maa sakinah ba kunyarta suke ji ba kuma itace bata saka musu ido ko saka musu iyaka dan haka tinda suka gaidata da safen suna bangarensa bata sake ganin kowannesu ba sai dare da bahar ta dawo ta kwanta.

Kulawa ma da komai na tattalin datake mata komawa yayi hannunsa dan haka maa ta kama kanta ko doguwan fitowa batayi dan kadama tsautsayi ya sakata ganinsu tinda so daya idanuwanta suka ganar ma da dawowa da bahar dinma a hannuwansa yake daukota yakaita har dakinta ya gama shiriricewa acan kafin yafita ya fice.

Bayin masarautar kaf gabaki daya tinda yazo suka dena fitowa koina idan ba aiki zasuyiba suna gamawa suke bacewa bame sake fitowa sai an nemesu wani aiki dan haka masarautar tayi tsit iya su kadaine ke shaaninsu a bangarensa cikin wata fitinanniyar soyayyar dake neman kashesu amma har lokacin ya kasa saduwa da ita sbd bayason abinda zai taba lafiyar cikinsa ko daya duk da kusan likitocin duniya sunfi goma daya tintiba sun tabbatar masa da babu komai dazai faru insha Allah.

Wata fitinanniyar soyayya suke zubawa ako yaushe bangarensa cikin zafafan yanayi da shauqi su wuni suna abubuwansu kafin dare yayi ta koma.

A wannan yanayin da suke ciki ya share kusan sati daya harda qarin kwana dan haka gabaki daya hakurinsa da juriyarsa neman qarewa takeyi gashi bayason mata komai sai angama bikin da akace zaayi an basa ita zai tafi da ita Moscow inda yakeda likitocinsa a villa dinsa ta yanda kome zai biyo baya zasu duba masa ita batareda sanin kowaba dam bayason duniya tasan da 'dansa sai haihuwansa saiya gama tabbatarda tsayuwan cikin nasa ko bayan yana nunawa mamansa soyayyarsa tukuna zai koma da ita.

Ita kanta zuwa lokacin yafara bata tausayi sbd ba qaramin hali yake shiga ba amma ya hana kasa kasancewa da ita dan haka ya fara shirin komawa dan shi su Ammi suke jiran komawansa su taho gabaki dayansu da sultan kansa.

Tinda ya fara maganar komawa ita kuma taji kaman zata kwanta ciwo sbd mutuwan da jikinta da fara kewansa tin bai tafi ba.

Shi kansa yanajin yanayin nata amma dole daman zai koma yana tabbatar mata tareda mata alkwarin daga ranar da aka daura auren Maa sakinah a ranar zai dauketa su tafi dan fara nasu zaman auren na har abada.

Rungumeta yayi a jikinsa yana kissing tsakiyar kanta da babu komai kamshin cikin gashinta na bugo masa ya lumshe ido tareda kama fuskanta ya dago ya kalla kafin yakai bakinsa akan nata ya tsotsa tukuna ya sake rungumeta yana cewa

'I love you Ayanah Bahar Ghaz'

Tashi tsigar jikinta sukai gabaki daya suna miqewa sbd yanda ya fada kalman da wani sauti mara hayaniya da zallan taushi da ratsawa tareda qarashi yana dora bakinsa akan fatar kunnenta kalmomin na shiga kunnenta direct.

Dagowa tayi cikin slow ta kalli fuskansa ya lumshe mata kyawawan idanuwansa masu haske da zafin kwarjini yana sake rungumeta itama ta rungumesa tana lafewa sosai a jikinsa.

A gurinsa ta kwana a ranar kuma maa batama bi ta kansu ba bare ta gane hakan hakan.

Da safe bayan sun gama komai sun fito hannunta yana cikin nasa suka fito fuskansa sanye da wani tsadadden black versace shades fuskansa a kame da wani irin zallan iko da isa da mulki.

Har palo suka isa gurin maa sakinah tayi saurin dan zare hannunta tana tahowa gurin maa din ta zauna gefenta duk jikinta a sanyaye kaman ma zatai zazzabi.

Gaidata yayi sukai magana sosai kafin yayi mata sallama ya miqe ya fice.

Bata iya rakasa ba shima cewa yayi kada ta fito suka wuce tareda securities dinsa suka bar anjom.

Maa sakinah dataga tayi wani sanyi bata ce mata komaiba saima gyaran da tenya ta bari data fara yi mata dan kuwa alamu sun sake tabbatarda ana gama bikin tarewa zatai shikenan.


******Su Ammi ma dik wani shirin tafiya sun kammala dan haka shi din kadai suk jira gashi sultan yana samun sauki sosai ga kulawan dayake samu daga matarsa ta musamman,

Ba shi kadai ba hatta Asim sun tsayu akansa da nuna kulawa me yawa da kauna sun saka ya sake sosai ba laifi musamman da Ammin ta tsaya a tsakiya ta sake shigar da kauna da shakuwa sosai harma da tausayi a tsakaninsa da sultan.

Sosai yake samun nutsuwa da kwanciyan hankali tareda rayuwan dabai taba samu a baya ba duk da ciwon rashin mahaifiyarsa daban yake har abada bazai goge ba amma ya samu nutsuwa sosai fiyeda yanda bai tsammanata ba daga mutanen dabaiyi tsammani ba.

A cikin qanqanin lokacin har yan uwansa yayi kokarin jansu a jiki yana shigowa mutane dasu da sake bude rayuwansu da idanuwansu ga rayuwa da mutane da zuciya daya ba kaman baya ba da sukaita fama da lalurar wahala.

Maraki ko sultan bata iya kira tai masa gaisuwaba bare jajanta masa da jin lafiyarsa sbd sanin yanzu ayanah ghaz ce dashi tako ina dan haka ya sake ficewa daga ranta tanajin ta sake tsanar jin ko sunansa bare sake rayuwar aure dashi ta hakura kwata kwata bazata yadda ta qare irin yanda haile ta qareba.

Mai girma yunar shima ya iso da nasa iyalan duka tsaf dama wasu manyan jinin boyem haka suka ringa isowa daya bayan daya dan abubuwa da yawa,dagaisuwa da dubiya da kuma daurin auren da akaiwa manyan gayyata zuwa anjom ghaz.

Manyan boyem ne suketa dira suna sake saka qasar daukan manyan qasa da tsaro sbd hidimar bikin kusan tanata matsowa.

Tenya ce da zuhrah suka fara wucewa da zuriar Tenya da suma suna nan sun iso suka fara isa dan fara shirin daya dakata sbd rasuwan.

Cikin saa tafiyar su Aslam suma ta kammalu zuwa umrah dan haka cikin kwanciyan hankali suka shirya mahaifinsu ya basu kudi masu yawa duk da dukkaninsu sunada dukiyar,
Asim ma kudi ya basu masu yawa hakama Ammi da kanta ma sai data basu tana musu fatar dawowa lafiya sbd kusan saaninta ba wani girmansu tayi ba sosai.

NUAB dukkanin wannan hidimar da akeyi nasu ayyukan sarauta sunyi masa yawan dayake son clearing nasu kafin lokacin daurin auren sbd daga can tafi zaiyi zai kuma kwana biyu baya nan.

Asim zai barwa ayyukan daya gama yadda dashi akansu sbd yana son fara cire masa kowane rauni da saka masa karfin hali tsayayyar zuciyar da babu rauni ko girgiza ko daya a cikinta hakama shine wanda zai bawa mataimakinsa da har lokacin baa nada ba na baya ne tin lokacin sultan akai har yanzu bai fidda takardar hakan ba sai bayan dasu Sultan suka tattara suka wuce Anjom tukuna.

Hakan ya saka duniya ta sheda baa bawa Asim din matsayinba sbd mahaifinsa dan uwansa yaga cancantarsa ya basa dan haka take aka fidda labarai da jaridu ana yadawa cikeda mamaki da farin ciki harma da fara manta abinda ake neman riqewa akansu sbd mahaifiyarsu.

Asim ba qaramin mamaki da shock ya shigaba daya samu takardar daga sultan LEUL NUAB dan abune da bai taba tsammani ba a daidai lokacinda yake kokarin barin qasar gabaki daya musamman da ayanzu baida mahaifiya.

Leylah kanta zubewa qasa tayi tana yiwa Allah sujjada sbd farin cikin ganin wannan ranar dan kuwa a matsayin da Sultan LEUL ya basa kusan cika masa burinsa akai na zama me mulkan boyem dan kuwa a duk lokacinda NUAB baya nan shine me ikon da mulkin boyem dan haka kasa riqe farin cikinta tayi ta rungumesa tana fidda hawayen farin ciki.

Mai girma yunar ma yayi farin wanan lamarin sosai take ya fara shirin qaddamar da taron nadin Asim din da zaayi kafin ranar Bikin Sultan LEUL NUAB din da matarsa da zaayi acan anjom dan kusan shine yafi yada duniya ba asalin auren da zaa daura ba na kadir.

Bayan isarsu sultan anjom lafiya labarin ya samesa shine da kansa ya kira NUAB ya miqa masa dukkanin godiyansa ga abinda yayiwa Asim din kafin Asim din shima yaje da kansa yasaka hannun karban matsayin wanda akai agaban dukkanin manyan fadar masarautar boyem ana farin ciki da tayasa murna.

Dole leylah ta jira daga tafiyanta anjom sai idan ya tashi su tafi tare sbd hidimar bikin da zaayi na nadin.

Su aslam suna can suka ji dan haka suka shiga farin ciki da murna amma basa nan dole nysah ne ta tattaro ta dawo da yayanta duka sbd hidimar.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

179
Securities masu zaman kansa aka ware masa na masarauta sbd sabon matsayinsa da kuma ba musamman da NUAB ya basa a matsayin kyautar sabon matsayinsa dan haka take rayuwar ta sauya masa dan kuwa babban bangarensa da bayi ne suke gadinsa take ya samu sauyi securities masu karfi suka maye gurbin bayin.

Ita kanta leylah take tafara jin kanta da matsayinta ya sauya dan kuwa hadda securities mata itama guda biyu aka ware baya dan haka hidima sukeyi sosai itada nysah da sauran zuriar haile da suka taho.

A ranar da akai nadin sarautar a ranar duniya ta sake tabbatarda karfin da LEUL NUAB yake dashi dan kuwa fitowansa da tsakanin tsaronsa daban yake hakama aura dinsa daban take ko acikin dubbannin mutane sbd kwarjinsa kadai sai daya saka gurin da duniyar cikin boyem din daukan tsit daya bayyana.

****Anyi hidimar bikin nadin matsayin Li'uli Asim Almazz cikin farin ciki da babban taro da miliyoyan jamaa da zubar da dukiya kaman baa san zafinta angama lafiya kalau masu tafiya sun tafi masu shirin tafiya ma sunata yi kafin kuma a sake tafiya bikin Sultan me boyem da kansa.

Tinda aka gama hidimar bikin Asim din babu wanda ya sake ganin Sultan LEUL saida aka kwana biyu yana hutawa sbd yana buqatan cikakkiyar nutsuwa da hutunsa ya dawo daidai kafin tafiya haduwansa da Sultanah dinsa.

Ko Aleey hutawa sukai abinsu hankali kwance da jiran ranar tafiya tazo musamman komai na wucewansu Moscow daga can daya gama musu shirin komai kaman yanda LEUL ya bada umarni.

Shi kansa Asim hutu yake buqata sosai dan haka shima babu wanda ya sake ganinsa nysah ma da zasu wuce sedai suka zo bangarensa cikin basa girman matsayinsa da ayanzu ganinsa ma sai ansanar masa sukai masa bankwana yayiwa yayanta kyautar zinari me kyau ya bada motoci daga bangarensa aka kaisu har airport.

Bayan ya samu damar hutawa dakyau komai ya fara tafiya daidai likitocin da zasu fara duba matarsa da cikinsa akai akai a matsayin antenatal ya nema dan su fara bi masa lafiyan babynsa ana kiyaye girmansa cikin koshin lafiya har zuwa lokacin haihuwansa.

Leylah farin cikinta haka kawai take jinsa,kome take a yanxu farin ciki takeji batajin damuwan komai ko shakka bare fargaba sbd babu abinda a yanxu ubangijinta bai bata ba bayan jiran haihuwa lafiya musamman yanda Asim yake bayyanarda soyayyarsa me tsafta akanta da cikinsa dake jikinta.


******Acan Anjom suma hankalinsu a kwance yake da sabuwar rayuwar da kusan kowa ayanzu ya samu,

Sultan yana samun sauki sosai sosai sbd likitocin dake bibiyan lafiyarsa cikin kwarewa da kulawa,

Ita kanta Ammi wata irin kulawa take basa dakyau kaman qaramin yaro gashi anan babu kowace takurawa ko rashin sakewan tarin bayi da jamaar masarauta hankali kwance suke rayuwa ba kowane shamaki ko kiyayewa kauna ce a bayyane da soyayya me zafi da basumasan suna bayyanawa ba,

Su maa sakinah sosai suke tayata bayyanawa da bawa sultan dukkanin kulawanta da soyayyarta dan hakanne ma yake samun saukin sosai sosai sbd har takawa yafara yi da kansa sedai da yar sanda me kyau da aka tanadar masa hakama a cikin bedroom dinsa zuwa palo da bathroom da dining duka yana iya tafiya zuwa da kansa batareda komai ko sandar ba idan zai fito ne gurin jamaar gari da mutanen fadar masarautar anjom din daya sake musu sosai da kulawa zaman majalisa sukeyi suyi firarsu sosai da labaran tarihin anjom dayake duk sun manyanta kamansa dan haka suka zama abokan firarsa tinda bawai zuba mulkin akeyiba kawai rayuwar kwanciyan hankali da nutsuwa tareda kaicewa daga hayaniya da nauyin mulki da sarauta ya sakasu dawowa nan dan haka anan din ma bawai mulkin zasuyiba kawai dai duk wani abin dazai taso dayake buqatan mulkin sarauta zasuyi fuskancesa aji dashi a wuce gurin batareda ana zaman fada ba irin sosai tinda Ayanah ce a matsayin me mulkin Anjom din shi kuwa bazai iya barinta daukan wannan nauyinba zai tayata ji da komai a cikin nutsuwa da sanyi ba hayaniyar mulki tinda an zuba hukumomin zartar da hukunci da adalci wa kowa a garin hakan ya dauke nauyi sosai na sarautar anjom din.

A bangare daya tattali da kulawa sukeyi wa Bahar da cikinta sosai musamman da tafiya zatai daga hannunsu ta tafi gidan miji sai kuma haihuwa idan ya aminta da barinta dawowa haihuwan kenan.

Ita kanta Bahar din tinda Amminta ta dawo ta warware sosai ta koma kaman ba ita dinba laulayin duka ya saketa lafiya kalau take jinta kaman batada komai duk da masifar son cikinta takeyi kaman yanda kowa yakesonsa sbd tana son ganin jininta dana NUAB hakama jinin da shine kadai yake nata jinin na asali wanda take fatan yaxo lafiya ya rayu lafiya.

Maa sakinah ma hakanan take jin jikinta na sanyi itama kuma a kwanakin sbd kwanakin auren da suketa qarasa tahowa tanajin kaman ba ita din bace zatai auren data gama fidda rai da tsammanin yinsa tin a kuruciya ta cire rai kuma Allah bai bata iko da damar ba sai ayanzu data manyanta dan haka sai tana jin fargaba ma dayin auren da tsoro.

Ga Kadir haryanzu basu taba kebewa sunyi ko gaisuwa ba sedai su gaisa a cikin mutane kaman koyaushe batareda ta iya kallansa ba dan jin takeyi kaman bazata iyaba.

Maleketenya kuwa ba abinda ya dameta shirin Amare takeyi back to back har saida ana saura kwana uku cif bikin ta gama komai datake musu tsaf daga nan aka fara shirin gagaruman walimar da zaayi ta Bahar da Maa din amma dai ita maa bata cikin kowane shiri na amare Bahar ce kawai akaiwa shirin Amaren Ghaz a ranar da zaayi walimar kenan.

Dukkanin masu ado da kwalliyan dazasu shirya bahar daga Boyem aka daukosu musamman hakama kusan garin anjom a cike yake da 'yan jarida da media da baqi da qarin tsaro tako ina a hakan ma cikin mai boyem bai isoba sbd a wannan karan duniya tasan bikin aurensa akeyi hakama ansan yana tafe anjom kowane lokaci.

Leylah data matsu ta isa Anjom din jin tayi kaman ta riga su Asim din isa sbd su saima daren ranar zasu isa Amma sam yaqi barinta tafiyar dan baiga abinda zai sakasa barinta tafiya ita dayaba da ciki a jikinta duk da yasan tareda tsaro zata isa amma bayajin nutsuwar hakan gwara kawai ta jira su isa tare.

*******Baccin Safen data saba A ranar walimar wadda daga ita sai daurin auren gobe shi takeyi hankali kwance abinta su kuwa masu shirinta suna babban dakin da aka ware dan shirinta acan sun jere komai tinda safe suna jiran ta gama baccinta koda kuwa ze kai rana ko wuce nan ma to zasu jira sai tagama ta tashi tukuna ayi mata komai sbd asalin ikon da a yanzu itace zata ringa bugasa a qasar boyem kaf da sbd a yanzu datake Queen Bahar mata guda daya tak ga Sultan NUAB ALMAZZ itace macen datafi kowace mace daraja a boyem din da kewayenta sbd matsayinta,

Sbd kasancewanta a anjom yanxu da kowa yasani ana fara bikin ya saka ba iya daga boyem ba masarautu da dama sun aiko gudunmawar bada tsaronsu ga Anjom da tarin dukiya mai yawa da bayi masu yawa tako ina wanda ya saka gabaki daya garin ya sake rikicewa da harkar mulki da dukiya kawai tareda arziki.

Tin ana saura kwana uku da bikin babu wanda ya sake saka bahar a idanuwansa sbd hana kowane ido sauka akanta da cikinta sbd sauyawanta gabaki daya zai saka duk wanda ya dora idanuwansa akanta ya kasa daukewa hakama ta shiga matakin da babu wanda zai sake dora idanuwansa akanta sbd zamanta cikakkiyar matar Sultan me boyem a duniya yanzu dan haka kallanta ya zama kusan haramun ga kowa bayan shi sai dolenta maana iyayenta dana mijinta sai kuma bayinta na kusa da ita sosai masu hidimarta wainda suke wainda Amminta ta zabesu tin yanzu su naimah ne tin na baya.

Ayau din da wani irin yanayi me wuyan fassarawa ta tashi musamman da Ammi itama tin jiya take jin sanyin jiki sbd rabuwa da Bahar din shikenan kuma sai dai ziyara,
Hatta maa sakinah sanyi jikinta yayi na rabuwa da bahar tinda ita da Ayanah suna tare zasu qarasa rayuwa tare insha Allah tinda duk inda mazajensu suke basu taba rabuwaba suna tare.

Kafafunta ta ziro qasa tana miqewa tsaye tashinta bacci kenan karfe goma da rabi harma da mintina.

Wayarta tafara juyawa ta kalla a natse tana sauke numfashi me hade da ajiyan zuciya me sanyi sbd yau kwanansu uku kenan cif basuyi magana da juna ba sbd zuciyarsa data kasa riqe jinta batareda yana ganinta a gabansa ba kuntar da duka kwanciyan hankali da nutsuwansa hakan yakeyi dan haka suka dena waya kwata kwata sedai text wanda shima sai so daya a wuni ranar gobe yake jira ranar da zai kalleta a zahirance ya karbeta a matsayin matar daya karba kenan har abada sai mutuwa ta riga ta shiga hannunsa da gidansa kenan.

Bathroom ta nufa tana zare rigar sama ta kan kayan baccinta tana isa ta shige tana rufo kofar.

Brush tayi tana gamawa ta qarasa zare komai nata ta isa ga ruwan wankanta da baa jima da hadawaba ta farka ta saka kafafunta ta shige ahankali tana rufe idanuwanta sbd wani dumi da qamshi da suka ratsata lokaci daya.

Ta jima sosai tana wankan kafin ta fito daure da towel me dan girma a jikinta tana goge gashinta da wani ta iso gaban mirror ta zauna tana kallan kanta tana goge jikinta cikin sanyi da nutswa tana jin kowace gabar jikinta na fidda wani sirrin qamshin daya kama fatarta

97 / 100