Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   54 / 100

159K to 162K   out of 299.8K words

danne abinda takeji dan barin Hayateem dinta ya fuskanci wannan ranar da zata zata fara gina tarihi me girma a rayuwarsa.

Manyan baqi daga qasashen kusa dana gari da duk wani jinin boyem dake duniya fara halarta sukai a qasa da masaurautar boyem wanda yake tsananta tsaron qasar ayau gabaki dayanta da masarautar sbd tsaron har yayi yawan da hankali ma bazai daukaba,

Kayan nadin sarautar da sultan ya jima da tanadar masa aka aiko daga bangarensa wanda sakon ya iso da bayi kusan sama da ashirin tareda kadir suna daukan idanuwa tamkar zinari sai asalin zoben zinarin dayake dauke da adon black diamonds a cikinsa na sarautar wanda wata narkakkiyar dukiya me tarin yawan gaske sultan ya batar gurin qerosa daga qasar Kuwait me dauke da sunan SULTAN NUAB 40 wanda kowane sultan me mulki saiya mallaki nasa.

Isowan sakon bangaren Amminsa ya saka ammin tasa bada tukuicin dukiya me tsananin gaske hakama su tenya da maa sakinah saida kowannesu ya bada tukuicin zinari me yawan gaske kafin daga baya suka dauki kayan Ayanah na gabansu suna bayanta dauke dasu da bayi sama da goma suka nufi bangarensa dan mahaifiyarsa ce zatai shirinsa a bisa al'adah.

Koda suka isa ya fito wanka yana sanye da fararen kaya tas riga body hug da farin dogon wando fuskarsa tayi wani irin haske asalin kwarjininsa yana fita a natse yana kwantar da tsigar dukkanin wani me kallansa.

Amminsa ce kadai ta iya isa palonsa na kurya sai Maa sakinah da tenya wainda suka tsaya daga nesa Ammin tasa ta tako tana isowa garesa yana tsaye ya kasa motsawa ya zuba mata idanuwansa yana kallanta dukkanin jikinsa na mutuwa da wani irin dumi da zafi.

Itama wasu hawaye ne suka cika idanuwanta tana qarasowa rungumesa tayi ahankali tareda sauke ajiyan zuciya tana bude baki tace

'Daga yau ina rokon allah ya baka dukkanin kariya har ranar da ranka zai bar jikinka,
Ina rokon ka samu dukkanin kariya da rayuwa me albarka da jin dadin da kwanciyan hankalin da baida kishiya har ranar da zaka sauka wannan mulkin lafiya.'

Hannuwansa biyu ya saka ya qanqameta jikinsa sosai yana rufe idanuwansa yana rokon allah ya karbi adduar mahaifiyarsa akansa.

Mintina suka bata a hakan kafin suka saki juna ta kama hannunsa ta zaunar dashi sai lokacin su maa suka iso suka fara bata komai na sarautar a hankali tana saka masa tana shiryasa.

Hannuwanta biyu ta saka ta dauki zoben dayake daga mahaifinsa ta saka masa kafin ta zaro nata kyautar ta chain din asalin azurfa da aka saka sunansa a jiki da manyan baqaqe da larabci wanda tin a shekaru tayi masa shi ta saka masa a hannun da agogon dubban daruruwan dollars suka siyesa ta kama hannun takai bakinta tayi kissing ahankali tareda jero masa wata irin adduar data sakasa sake rungumeta yana kissin tsakiyar kanta.

Maa sakinah ce ta dafa kansa a hankali itama ta karanto masa adduoi masu kyau da tsafta kafin maa tenya itama tayi masa a daidai lokacin komai ya kammala masarauta ta hallata ta cika maqil da wasu irin manyan mutane tako ina ga medias daban daban da bazasu taba kirguwa ba hakama mutanen NUAB din da turawan kasashe daban daban kusan duk sun bayyana wainda zasu iya zuwa a short lokacin da aka sanar.

Duk wani babban fada na yanzu dama wainda sukai retire da murabus suna bakin kofar bamgarensa a jere a tsaye tareda wasu irin securities dan jiran fitowansa dan rakiya garesa zuwa fada wanda haka tsarin yake.

Aleey ayau din tsaron daya zuba a masarautar boyem ya wuce dukkanin hankali sbd tako ina yaronsu ne a cikin shirin da basu taba zamaba na rayuwarsu,

Idanuwan aleey da duk wani ghaz member a bude suke sharp suke hatta yaransu da duka suka qasashe da sukai isowan gaggawa a shirye suke tsaf da bawa kowace daqiqa ta ranar kariya a ransu.

Karfe goma sha biyi daidai ne lokacin fitowansa dan haka dago manyan idanuwansa da ayau tsantsar mulkin dake jininsa yake bayyana yayi ya kalli agogo sha biyu da hamsin da tara,

Juyawa yayi ya kalli hanyar kofar dakin da babu wanda ya shiga har lokacin sbd har lokacin bata farka ba sbd kwanan datai da wani mummunan zazzabi me karfin daya hanata baccin lafiya sai bayan asuba.

Juyo da kansa yayi ya daga kafafunsa yana takawa a natse da kamewa tareda tsantsar ikon dayake yawo a jininsa ya nufi kofa wadda yana isowa aleey ya wangale ta take dukkanin mai rai dake gurin suka gyara tsayuwa suna sauke kansu kaf a lokaci daya cikeda wata irin girmamawa da wata qarar da aka saki data tabbatarwa duk wanda yake ciki da wajen masarautar jiran nadin SULTAN LEUL NUAB ALMAZZ ya fito.

Take masarautar ta dauki wani irin tsit duk da dubban daruruwan mutanen dake cikinta da zagayenta shiru koina yayi.

Securities kuwa take suka sake dauke wuta da qamewa cikin kowane position nasu.

Aleey dayake shine a gaban NUAB din da wasu securities da bama sa jin kowane yare bayan na harbewa without any second thoughts,

Wasu irin qananun zafafan full loaded pistols ne a jikin aleey a boye kusan guda hudu da wata wuqar da kai tsaye zata yanka ko jijiya nawa ne a inda aka sokata tayi musu yankan cin ledar bera.

Keelah ma dayake daba bayan NUAB din tareda manyan boyem da suka taho rakiyar sultan din zuwa fada a loade yake da munanan makamai a cikin jikinsa fuska babu sauki ko a kadan a wannan lokacin.

Kai tsaye fada suka isa wadda yan jarida daga nesa inda aka kebe musu suka fara hasko hasken flashers nasu tako ina kowane sahu da motsi yana daukewa saina isowan sultan me boyem da ghaz da Moscow.

Sultan yasar dayake zaune tinda sultan da yan rakiyarsa suka sako kai a cikin fadar ya zuba masa idanuwansa batareda ya daukeba yana jero masa wasu irin karfafan adduoin da zasu basa kariya da ikon mulkinsa cikin aminci da kwanciyan hankali.

Babu bata lokaci aka gabatar da nadin sarautar wadda tako ina ake fitowa da wasu irin trays na danyan zinarin da shine kawai yake daukan idon koina.

Sultan ne ya taso a daidai lokacin da ake farawa ya tsaya a gaban NUAB din gabatar da sauran al'adar da manyan asalin boyem ke yi a lokacin nadin.

A daidai lokacin da ake kammala komai aka dauko hular datake matsayin rawanin mulkin da zaa saka masa,

A daidai lokacin daya daga cikin securities da aka bari acan gadin bahar ya iso fadar da kansa har gurin aleey dake can gefe a tsaye batareda ya zauna ba dan bazai taba iya zaunawa ba a daidai lokacin bai yadda komai ya shammacesa ba musamman da basuga motsin Asim tako inaba da mahaifiyarsa basu san me suke shiryawaba.

A gurin kunnuwansa ya sanar masa da bahar ta farka amma ba lafiya ba tanata amai ta fito tanason barin bangaren amma basu bude kofar ba.

Aleey kallan NUAB yayi wanda ya basa umarni me karfin gaske cewan ko wane lokaci ne yake a ringa sanar dashi abinda ya shafeta kai tsaye without any delay.

Kallan taron manyan duniyar dake gurin yayi da abinda akeyi wanda duniya gabaki daya take shedawa live a gidajen tv da live shows da media da ma wainda ke shadawa a gaban idanuwansu.

Numfashi aleey din ya sauke tareda tinkaro NUAB din wanda aka kawo hular zaa saka masa ya dan rankwafo cikeda girmamawa ya fada masa daidai lokacin shugaban fadar jinin boyem daya zuba shekaru shine yake nadin sarakunan boyem ya tsufa ya daga hular zai saka take NUAB din ya riqe hannunsa da hannunsa dayake cikeda lafiyayyan karfi da lafiyar fata yana dago idanuwansa da suke jajir tinda aka fara nadin ya dakatar dashi daga saka masa nadin hular darak3 ta asalin saqin sunan boyem da akai da ruwan zinari.

Sultan dayake ganin hakan cikin iko da nasa mulkin kai tsaye ya riqe hannun NUAB din batareda an gane meyake shirin faruwaba na barin gurin da NUAB din zaiyi ya kalli aleey da idanuwansa akan ya koma inda yake a qarasa gamawa.

Baya aleey yaja yana komawa sbd shima yasan babban qaramin aikin mai gidansa ne barin gurin da duniya zata sheda abinda yayi.

Qarasa nadin sarautar akaci gaba dayi cikeda tsantsar iko da farin ciki da kafar da sabon tarihi a qasa da masarautar boyem.
#MAMUH


HAYATEEM novel
700
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

96
Kammala nadin akai tareda daga tutar datake dauke da sunansa aka ambaci sunansa kowa da duniya ta sheda a matsayin sabon sultan na boyem me daraja dan haka kowa miqewa yayi cikin sautin daya ratsa kowane lungu na masarautar akai masa barka da sheda wannan rana me tarin daraja da kafar da sabon tarihin da zai dora boyem akan hanyar kalar nasa mulkin da ake fatan ya zamo alkhairi me girman gaske.

Daya bayan daya manyan masarautar boyem masu matsayi a yanzu da wainda ma basa dashi da wainda sunyi sun sauka suka ringa zuwa suna sana sakawa matsayinsa albarka da addua cikin girmamawa wanda hakan ne ya dauki lokaci.

Bayan ana gama wannan sallah akai a cikin babban masallacin masarautar wanda ya dauki mutane fiyeda lissafi mutane masu dibbin yawa har waje wadda hatta ita sai da aka ringa dauka live ana nunawa duniya sallar sultan ta farko a cikin dubban jamaar da suka halarci taron nadin.

Ana gamawa abincin zaa ci wanda anan ne zaayi biki na al'adu da abubuwan nishadi da dama till down dan haka ake bawa sultan daman komawa ya sauyo kayansa daga kayan nadin sarautar.

Dukka wannan abin da akeyi zuciyar sultan NUAB tana rabe ne a cikin tinanika guda biyu wainda suke bayyane a idanuwansa da suka sauya matiqar sosai duk da yayi iya kokarinsa gurin dan sakewa yana gaisawa da mutane sosai sbd babu qaramin mutum a gurin.

Lokacin tafiyarss sauyawa da yar hutawar da batafi ta rabin awa ba zuwa awa daya kai tsaye barin gurin yayi tareda personal securities dinsa da securities na masarautar da daga yau suma suna tsaye a gurin basa kariya.

Tin a hanya yana tafe cikin nutsuwa da kamewa tareda zallan ikon mulki dayake yawo a jininsa ya dan kalli aleey a natse batareda doguwar hayaniya ba yace a kira doctor.

Fidda waya aleey yayi kai tsaye yana kiran likitansu da zaiyi gaggawar biyosu sbd yana masarautar shima gurin hidimar bikin.

Suna isowa bangaren nasa wanda tin daga nesa securities ne masu karfin gaske zagaye da gurin take suka sake gyara tsayuwa dan masa barka da isowa batareda baki ya furta ba sbd shima bai iya amsawan dan haka kai tsaye ciki yake kokarin nufa bayan an wangale masa kofar shigewan da sauri.

Sauran securities din gabaki daya kaf duka burki suka ci a bakin kofar suna jeruwa gefe daban bayan ya shige aka rufe kofar ruf gurin ya sake daukan tsit.

Hatta aleey bai shiga ba daga kofar ya dakata yana jiran isowan Dr.

Shi kuwa yana shiga wata ajiyan zuciya mara sauti ya sauke a hankali tareda numfashi me zafi yanajin zuciyarsa na dan samun sassaucin halinda take ciki na karba da hawa mulkin da bai taba tinanin hawa ba arayuwarsa,

Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa ya cire dukkanin kayan sarautar da suke jikinsa dayake jin kansa very uncomfortable a cikinsu,

Yana zarewa bathroom ya fada tareda sakarwa kansa ruwan dumi da suka ratsasa yaji yana dawowa NUAB dinsa,
Bai wani bata lokaci ba ya fito wankan a natse ya shirya tareda sauya kaya zuwa marasa nauyi ya duba wayarsa dake kawo haske yaga kiran aleey dan sanar dashi dr ya iso tin dazu.

Fitowa yayi bayan ya ajiye wayar ya fara nufar dakinta kai tsaye yana shiga a qasa ya ganta zube ta dunqule guri daya tana wani irin rawan sanyi idanuwanta a rufe fuskarta tayi ja.

Qarasawa yayi kai tsaye baice komaiba ko tsayawa komai a natse ya dauketa daga qasan yana nufar bakin gado da ita ya ajiye a hankali.

Qatuwar jacket ya dauko ya saka mata tareda hulan sanyi me kauri akan kayan dake jikinta kafin ya sake daukota ya fito da ita palon yace dr ya shigo.

Dr na shigowa cikin sauri da nutsuwa ya fara dubata sbd dukkanin aikin NUAB bayason gaggawa a natse yake so da buqatar ayi masa komai nasa bare a yanzu da ake maganar lafiya da rayuwa.

Mintina sosai dr din ya dauka yana dubata kafin ya fidda magani kusan guda uku ya bata tareda daura mata qaramin drip sbd aman datai sosai y dan tafi da ruwan jikinta.

Dr na ficewa haka ya kuma daukanta da drip din ya maida daki tareda daga wayarsa ya kira maa sakinah dan kawo mata abinci da bata kulawa.

Kafin zuwa maa sakinah tini lokacin komawansa bikin da zaa sake farawa yayi amma bai fito haka yabar dubban jamaa anata jira har sai da maa sakinah ta iso tukuna ya fito daga dakin ya sake shiryawa cikin wata shigar daban data fiddo wani asalin zazzafan kyansa da kwarjininsa tareda bayyanarda shi din matashin sarki ne da zai zuba zazzafan lokacinsa akan mulki.

Yana ficewa Maa sakinah ta shiga dakin a cikin tsananin kewan bahar din datai wadda ta kwana biyu bata gani ba dan haka sakawa tayi bayin suka jere komai suka fice ta qarasa gurinta ta zauna bakin gadonta tareda bude baki zatai magana Bahar din ta shige jikinta tana rungumeta tareda fara hawaye masu sanyi tana cewa

'Maa dan Allah kada ki tafi koina ki zauna tareda ni kokuma ki tafi dani can'

Shiru maa din tayi tana rungumeta jikinta sosai tace

'Bahar Allah ya baki lafiya tukuna amma ke yanzu matar Sultan ce a masarautar nan baya kamata ace kina fita yawo koina koma komawa wani bangaren'

Shiru bahar din tayi tareda batareda ta fahimci maganar kwata kwata ba ta Girgiza kai tana cewa aa ita dai tanasonta a kusa da duk inda take.

Shiru kawai Maa din tayi batareda tayi sabuwar magana ba ta saketa tana nufar toilet ta hada mata ruwan wanka me zafi da qamshin wasu irin turarikan wanka na SHUWA INCENSE AND MORE 07042293387 wainda suke na asalin masu kama jiki su wuni fatar jikinka tana qamshi me sanyi da ratsa zuciya.

Dawowa tayi ta kamata zuwa toilet din sbd ruwan drip din ya qare,

Wanka Bahar din tayi a sanyaye sbd ta dan samu karfin jiki daga ruwan da aka sakama mata tana gamawa ta sake brush ta fito daure da towel gashinta a daure tsakiyar kanta a sako sako wanda bama itace ta daure ba da kanta duk da batai tinanin shine ya daure mata dinba.

Maa sakinah cikin kulawa da sangartawa ta tsaya bayanta bayan ta zauna kaman yanda ta saba yi mata ta warware mata gashinta ta dan gyara mata sama sama ta sake dan daure mata kaman yanda ta gansa baa matseba ko kadan,

Tayata shiryawa tayi kafin ta dauko mata kayansa kaman yanda ta saba sune kadai sitirar datake sakawa ta saka wando da rigar datai mata mugun yawa hakama wandon ko zaman qugunta baya yi.

Sallah tayi tana idarwa maa ta zuba mata madara me zafi sosai da zuka tafara sha a hankali harta dan sha sosai kafin ta ajiye maa din da kanta ta ringa bata abinci tana lallabata sbd ta saba zuwa lokacin ta gama sangarta bahar din duk da ma bahar din bata gama sake damuwarta da rayuwar data tasoba gaba daya.

Tana gama cin abincin maganin ma itace ta bata da kanta tasha daqyar sbd batason magani sam bare irin wannan din,

Suna gamawa rokon maa tafara yi akan su tafi su koma bangaren can batason zaman nan din.

Yanda ta dage ne ya saka maa fidda wayarta ta saka kiran aleey ta sanar dashi duk da ana cikin hidima sosai haka aleey ya isa ya sanar da sultan NUAB din,

Dan shiru yayi kafin ya dago manyan fararen idanuwansa batareda ya jiyo ba yace abarsu su tafi din.

Aleey barin gurin yayi ya isa bangaren da kansa yayi musu jagora har bangaren Ammi wadda bata bangaren suna gurin hidimar sbd tinda angama nadi bikin yanzu da akeyi kaman lunch ne kowa ya halarta maza da matan duka jinin boyem da masu matsayi tareda masu muqamai na qasashe harma da abokan business dinsa mata masu karfi a duniyar business suma.

Tenya ma da sauran bayin da securities din da aka tanadarwa Ayanah din duka suna can dan hakanne ma bata nema bahar ba tabarta ta huta kaman yanda suka duba kafin fitowansu bangarensa dazun sukaga tana bacci sosai.

Suna shigowa daki ta nufa tana shiga ta sauke ajiyan zuciya sbd samun dawowan cikakkiyar nutsuwanta.

Kayan jikinta tafara zarewa a natse cikin rashin karfin jiki kafin ta sauya da wasu ta isa ta haye gadon dakin ta kwanta tana sake samun nutsuwan gangar jiki data ruhi.

Maa sakinah ma farin cikinta da kwanciyan hankalinta taji itama ya dawo ganin bahar din a gabanta ta dawo mata a cikakkiyarta dan haka fara kokarin bata labarin nadin da akai yau din gaske tayi wanda ya saka Bahar shiru jikinta na wani irin sanyi da mutuwa,

NUAB a matsayin SULTAN na qasar boyem gabaki daya?
Yana a matsayin SULTAN a dazu ya taho gareta ba NUAB zallah data saniba.

Numfashi mara sauti ko kadan ta sauke daga zuciyarta tana lumshe idanuwanta ta rufe a hankali batareda ta furta kalma ko daya ba amma dukkanin abinda maa take fada akan zamowan NUAB din sultan dazai mulkin dubban miliyoyin mutane tana jin saukan kalaman cikin kunnuwanta,

Acan kuwa cikin babban makeken Palace hall din masarautar boyem din wanda yake a tsare da wani irin tsarin dayake bayyanarda tarin arziki ba qarami ba masarautar boyem take dashi tareda wayewa da ilimi dan kuwa komai na gurin class da dukiya me yawa yake nuna,

Tamkar fadar masarautar gurin yake komai golden da black ne dan haka gurin yake daukan ido kaman ka shiga fadar da aka qera da zinari,

A tsare cikin burgewa da daukan ido komai yake na tables kala kala na cin abinci wanda babu kalar tsadaddiyar abincin da babu wanda qwararri professionals akan girki suka dafa da tsarawa.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

97
Hidimar aka fara wanda kowa yake a tsare a waye ba hayaniya duka jamaar Echoes suma sun halla a tables daya farin cikinsu ya kasa tsayuwa Musamman 002 Asia,003 Zulee da Zee Amiru,Ummu Asim,Maman Anees da Amina Maikatifa Abinci kawai suke ci idanuwansu sun kasa tsayuwa guri daya  sai ganin jamaar su sukeyi suna qarasowa,

Naimah ce a cikin manyan bayin da aka zaba dan shigo da abinci a

54 / 100