Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   60 / 100

177K to 180K   out of 299.8K words

kai tsaye da itane zaayi tafiyar goben dan zuwa itama ta huta ta samu sauyin muhalli.

Kafesa da idanuwanta tayi tareda tsayawa cak har lokacin hannuwanta suna cikin nasa riqe,

Mamaki ne ya bayyana a fuskarta kai tsaye sbd ba tsammani taji zancen da bata ma gama ganewa ba duk da daman a cikin ranta tana jin inama zata bi su Bahar din can qasar sbd zatafi samun nutsuwa da farin ciki idan tana tareda bahar din duk inda take amma kuma yanayin dayake fuskar NUAB din yana nuni da kaman hukunci ne ya yanke akanta.

Numfashi me sanyi ta fitar tareda bude baki baki tace

'Hayateem,Umarni ne wannan ko hukunci kokuma raayina kakeson bi??

Sauyawa idanuwansa sukai ahankali yana kafeta dasu cikeda matsananciyar kauna me karfin gaske dayake jin inama duka babu wannan a cikin dadi ne zai dauketa su tafi duk inda zasu tafi dan tayi yawo a cikin yancinta,

Zare hannuwansa yayi daga nata a natse kafin ya zagayota da hannunsa daya zuwa jikinsa ya rungumeta ta gefensa yana dan lumshe ido ya bude baki yace

'Ammi ki sani Hayateem bazai taba umartar Amminsa ba sbd kece mace mafi darajar da babu ta a gurinsa duk duniya hakama kinfi karfin kowace hukuncina,
Inason nesanta ki da kowace irin damuwa da mutanen da zasu sakaki damuwan ne,
Na sani kinason bin 'yarki dan hakanne nayi miki hakan kije kin samu yancinki daga yanzu ke 'yantacciya ce daga masarautar boyem da duka masu mulkin boyem...'

Ahankali tsigar jikinta ta ringa miqewa sbd kalmar data cire ran samu kenan a rayuwarta har abada bayan qarar da shekarunta a cikin zama cikakkiyar baiwar Masarautar boyem,
Bata taba saka ran samun yanci a wannan shekarun datake dasu a yanzu ba,
Bata taba tinanin rayuwar samuwan yancinta zata tahoba daga bakin 'dan data haifa ba,

Ayau bayan shekaru da barowanta Anjom tin daga kuruciya ta samu yanci..

Dago kanta tayi tareda kafe NUAB da idanuwanta da sukai jajir a take tana kallansa hawayenta na qafewa tsaf hannuwanta na dan rawa duk da yancin yaxo mata a lokacinda bai dameta ba kaman a baya data so yancin kaman rayuwa amma taji dukkanin nauyin dayake kanta da dabaibaiye da rayuwarta suna sauka da warwarewa tana jinta sakat kamar an kunce mata matsatsen daurin rayuwa.

Ajiyan zuciya ta sauke me karfi tareda komawa jikinsa ta rungumesa tareda bude baki tace

'Hayateem Allah ya saka maka da mafificin alkhairinsa,.
Allah ya qara maka imani da tsarkin zuciya ya baka kariya daga kowace irin illa ta bayyane data boye,
Allah ya baka ikon mulkin qasarka cikin Aminci da kwanciyan hankali,
Ni baiwa kuma imebēti kuma wishmah Ayanah ghaz ina godia gareka da samun yancin da har abada kuma shikenan.'

Bai iya cewa komaiba rungume din yayi sukai shiru tsawon lokaci kafin ya saketa yana sanar da ita yanda tafiyar nata zai kasance da kuma gidan daya tanadar musu na zama acan din ba wanda aka fara tanadarwa Su maa sakinah din ba sbd su samu isashen wadatan gida da space yanda ya kamata.

Kasa cewa tayi aa sbd tabbas tafiyar da samun yancin sunzo mata a bazatar da bazata taba iya qin tafiyar ba dan haka farin cikinta ta fitar ta nuna masa na hakan tareda amincewa zama gidan daya tanadar musu amma da sharadin sam basa buqatan securities sbd Bahar da bata buqatan hakan sam.

Bai musa ba ya amince suka sake dan tattaunawa da bankwana sbd da safe zasu wuce kuma shi bazasu samu ganinsa da safen ba,

Miqewa yayi ya fito daga dakin Ammin na tareda shi zuciyarta cikin wani tsatsan sanyin farin ciki da samun nutsuwan da bata taba samun kanta a cikinta ba,

Maa sakinah dole itama zaiwa bankwana sbd kusan duk matsayin dayake bawa Amminsa yana basu itada Maa tenya dan haka kai tsaye dakin da maa sakinah din take Amminsa ta nufa dashi batateda yasan dakin waye ba itama Ammin sbd Sakinah na dakin ne kawai ya saka ta nufi dakin dashi sbd a yanzu bata wani son kusancinsu sbd bawa kowannensu daman fuskantar abinda yake gabansa tukuna daga baya ayi maganar idan zaman nasu zai yiyu ba dole ba tilas bazata taba riqesu da alkawarin da su iyayensu sukai ba matiqar basa kaunar hakan sbd taga alaman kaman babu me raayin hakan a cikinsu musamman a yanda yanzu kwata kwata ya shafe babin tina kowace irin alaqar dake tsananinsu koma tace kamar ya mance da akwaita a masarautar da rayuwar.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

108
Ammi ce ta saka hannu ta bude dakin kai tsaye batareda jiran komaiba ta saka kai fuskarta cikeda walwalan farin cikin dayake cikin zuciyarta shimfide,

Qamshinsa ne ya saka Bahar juyowa a natse ta kalli kofar sbd muryan Ammi taji amma kuma hancinta qamshi daban yake shaqo mata,

Ba zato tana juyowa din idanuwanta suka sauka akansa yana tareda Ammin kyakkyawar fuskarsa ta sake wani irin fresh fatarsa ta sake samun cikakkiyar hutu da nutsuwan data rasa na kwanakin baya kafin karban mulki na tashe tashen hankalin da aka ringa yi,

Idanuwansa masu daukan hankali da tada tsigar jiki akan Maa sakinah suke wadda take kallansa cikeda Murmushi da farin cikin ganinsa tana cewa

'Bahar koma kan gado ki qarasa hada kayan'

Tin bata qarasa ba bahar din ta miqe a natse ta kwashi kayan undies din nata tabar kan kujeran tana komawa kan gadon batareda ta juyoba.

Qarasowa yayi ya zauna a natse kujeran dake dakin batareda ya kalli komai na dakin ba bare sanin na waye,

Gaida maa din yayi a taqaice yana sanar da ita tafiyan da zasu yi din tareda Amminsa yafara kokarin yi mata bankwana itama.

Ammi gurin Bahar ta isa wadda take kokarin cusa kayan kayan akwati batareda ta nade ba duk da bras ne da panties sai halfvest dasu skintight masu laushi.

Zaunawa tayi gefen gadon tana riqe hannun bahar din tace

'Ringa gyarawa kina miqowa ina jera miki kada ki sakasu a hakan'

Dagowa Bahar din tayi ta kalli Ammi da idanuwanta da suke da wani sirrin kyau ta dan sake murmushi tana cewa

'Tohm Ammi.....' fitar sautin kalman tata wadda ta sauka cikin kunnuwansa a karan farko bayan lokaci me tsayi wanda sautin muryan kanta ta sauya sbd nutsuwan data samu a yanzu din daban yake da duka baya farkon zuwanta ya sakasa dago idanuwansa da suka sauka akanta kai tsaye batareda ta motsa ba cikin wata irin isa da izza tareda kamewa.

Saukan idanuwansa akanta yasaka taji su akanta ta hadiye wani numfashin da shi kadai ne ya iya ganinsa,

Sake hadiye numfashin tayi tana jin nutsuwanta na neman dan rikicewa daga cikinta amma daga waje a natse take babu abinda ya sauya daga nutsuwanta da suke gani ta fara kokarin nade kayan gabanta din batareda tinawa da menene su din ba tafara daga bras din masu shegen kyau da daukan hankali da tsada tana nadewa bama tareda tasan yaya zata nade din ba sai kawai tafara juyasu a hannunta tana sakawa cikin akwatin.

Maa sakinah ce ta fara miqewa tana daga wayarta da aka kira tabar dakin tana kallan Ammin tace wayarma kamar ita ake nema.

Ficewa sukai daga dakin wanda ya saka Bahar jin numfashinta fitarsa na sauyawa zuwa da karfi da sauri amma ta dake ta hana hakan bayyanuwa taci gaba da abinda takeyi wanda ganin hakan ya saukar da idanuwansa a natse akan abinda takeyi din wanda yake iya hango rikicewanta duk da dakewa da basarwanta.

Baida niyar tsayawa batawa kansa lokacin kallanta amma ganin yanda take yi dinne ya sakasa kasa dauke idanuwansa masu rikitarwa akanta dan kuwa ko inda yake ta kasa iya juyowa ta kalla.

Wata farar low-back padded bra ta daga tana kokarin nadewa ta tura akwatin ya miqe tsaye zai fice dakin ta dago a natse tareda miqewa tsaye da dan sauri sbd tinanin gurinta yayo idanuwanta na sauka kansa da wani irin sauri da hana rikicewanta bayyana.

Dakatawa yayi daga tsayen ya kalleta idanuwansa na sauyawa da takaici ya juyo ya tako zuwa inda take tana ganin hakan tayi saurin komawa ta zauna tana saka hannunta da dan sauri cikin kayan gabanta sbd ya juya ya tafiyarsa tinda ta gane fita zaiyi ba gurinta yayi niyar zuwa ba da farkon,

Jin yana gap da takun da zai kawosa gap da ita ya sakata kwasar kayan gabata zata miqe mitsaye ya tsaya cak a gabanta wanda hakan ya sakata sakin kayan kayan hannunta a gadon wasu white panties dinta suna bayyana a sama.

Kallo daya yayi musu ya dauke idanuwansa cikeda takaicin sakarcin datake aikatawa ya kalli fuskarta ya bude baki a cikeda isa da izza yace

'Kinayin hakan ne dan na gani????

Da wani irin tsananin baqin ciki da faduwan gaba ta dago ta kallesa batareda tasan ma ta dago din ta kafesa da idanuwan nata masu kyau itama tama rasa abinda zata fada masa sai kawai ta juya ta saka hannu zata fara kwashe kayan tukuna ta samu amsar yaba masa...

Riqe hannunta yayi tareda juyo da ita wanda haduwan fatar tafin hannunsa dana fatar bayan hannunta jin sukai wani dumi a lokaci daya yana bin fatar jikin nasu wanda hakan ya sakata kwace hannunta tana jin ranta na soyuwa sosai da kalmansa dan haka a zafafe ta kwashi kayan zata ma bar gurin,zuciya ta cita takasa barin gurin ta maida kayan akan gadon ta zube ta dago ta kallesa har lokacin batasan mema zata ce masa ba sbd idanuwansa dake kafe akanta suna yanke duk wata kalmar bakinta datake hadowa gurin fada masa.

Ganin wutar bacin rai dake ci a cikin idanuwanta datake kallansa dasu ya sakasa kallan kayan data ajiye din dan sake qularwa da tafasa zuciyarsa ya bude baki zai sake yabo mata maganar da zata iya fasa zuciyarta hannu ta saka ta rufe bakinsa batareda shiri ba sbd ko a yanzu jin zuciyarta takeyi kaman zata fashe,

Saukar hannunta a bakinsa ba tsammani ya sakasa loosing balance dinsa sbd saida ta daga qafafunta ta samu hannunta yakai bakin nasa wanda hakan ya saka kirjinsu haduwa ba tsammanin su dukan.

Bayan da yayi ya saka itama data taho din loosing nata balance din sbd bata dauka zai tafi bayanba dan haka kusan a tare suka tafi dan haka ya zagayota da hannunsa daya sbd hanata faduwa wani gurin da zata iya illatuwa ya dafe dresser din dake bayansa da hannu daya suka jingina da ita.

Wani irin kallo ne ya sauke idonsa akanta yana yi mata har lokacin yana zagaye da qugunta tana manne a jikinsa kirjinsu a hade yana jin bugawan zuciyarta na sauka a hankali a kirjinsa.

Janye jikinta tayi da dan sauri a natse tana qin kallansa ta bude baki tace

'Ina buqatan kasancewa a dakina ni kadai'

Bakinta da yayi maganar ya kafe da ido yana juyar maganar tata a cikin kunnuwansa sbd shine me bada umarnin kasancewa da duk wanda yakeda buqatar haka hakama shine me sallama da korar duk wanda baya buqata a gabansa da idanuwansa,

Jin yayi baima gane me kalamanta suke nufi ba dan kuwa ko Ammi da sultan da suka haifosa basu taba basa wannan umarnin ba shine yake bayyana a lokacinda ya so yaga dama ya kuma tafi a lokacinda yaso yaga daman hakan.

Wani iri yaji kalman ta dakesa sosai yama rasa shima me zai ce dan haka zai nuna mata shine kadai me bada umarni da buqatan kasancewa a duk inda yaga dama da duk wanda yaga dama a boyem sbd tasan ita a gabansa ba kowa bace da zata iya bada wannan maganar akansa.

Ba tsammani taji ya kama hannunta a cikin isa da iko tareda kamewan data sakata jin gabanta faduwa taso zare hannunta da wuri amma ta kasa samun hakan dan haka yana nufar kofa da sauri ta kallesa ta sake bude baki tace

'Ni kaine nace ka fita bawai.....

Juyowa yayi da karfin gaske yana fixgota jikinsa ya fado masa da karfi ya kalleta da idanuwansa da suka sauya sbd har ransa yaji zafi da bacin ran kalamanta dan haka kafin ta qarasa fadar wasu irinsu din ya fizgota din yana sakar mata azabar datafi duka zafi da idanuwansa da suka saka jikinta dan daukan rawar da bata gama bayyana ba ta bude baki tanason sake fadar kalamanta masu zafi amma suka bace mata a baki ta dauke idonta akansa tana kokarin zare hannunta da yayiwa mugun riqo ya jata yaci gaba da tafiya da ita.

Bude kofar dakin yayi ya fito da ita tana ganin hakan ta daure fuska sosai tana kasa kallan kowa sbd bazata iya nuna rauninta a bayyane ba akan abinda yake faruwa ba dan haka koda ya ratso palon da ita dukkaninsu Ammi dake zaune binsu sukai da kallo musamman leylah dataji bugun zuciyarta na tsayawa cak sbd riqone ne da fata da fata yayi mata me kyau da gaske,

Shuraim ma kallo daya yayiwa riqon ya maida kallansa akan fuskar Bahar wadda take daure da alaman bata kaunar koma menene yake faruwa ko kadan daya hada jikinta da NUAB din,

Wani iri yaji a zuciyarsa na tinanin ina NUAB din zai tafi da bahar wadda yake fatar koma menene ya kasance hukunci ne na wani laifin zata karba bana wata muamalar daban ba,

Itama leylah addua taji zuciyarta nayi me karfin gaske akan allah yasa hukunci ne na laifi Bahar din zata karba ba wani abin ba,

Zuhrah kallo daya tayi musu ta dauke kanta tana cigaba da duba wayarta datakeyi,

Ammi ce data kasa hakura ta bude baki zata hanasa tafiya da Bahar din Maa sakinah da zuhrah suka kalleta lokaci daya dan hanata
Maa sakinah ta dan bude baki tace

'Barshi sun saba koyaushe a cikin irin hakan suke,
Shi fushinsa da zafinsa a kusa yake koyaushe ita kuma bata iya kwantar masa da kai sosai,kusan koyaushe hakan ne yake kawo tashin hankalin tsakaninsu amma yanzu tinda rabuwa zasuyi daga yau din barsu kawai'

Shiru Ammi tayi tana fatar kada fushin NUAB din ya kasa control yayiwa bahar din wani abu dan haka duk sai taji hankalinta ya rabu biyu duk da tasan NUAB fushinsa akan mace ba daya bane ko daya dana sauran mutane.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

109
Kai tsaye bangaren ya fito da ita a hannunsa har lokacin yana riqe da hannunta idanuwansa a dan sauye,

Yana sako kai na fitowa daga bangaren bayi da securities da fadawan dake gurin a jere duka qasa sukai da kansu cikeda shakkar kasa dagowa sbd Babu sultan da a kaf tarihin sarauta ko bata boyem ba dake riqo macensa a bayyane idan ba LEUL boyem dinba daman sanin kowane me rai ne a boyem cewan sultan NUAB LEUL boyem baturen da baima san al'ada da kunyar mulki bane dan haka dole jamaar masarautar ne zasu kiyayewa idanuwansu da zasu iya rasawa gurin gane ganen abinda yafi karfinsu.

Aleey ne ya iya dagowa kadai ya kalli fuskar LEUL din nasa yaga alaman zuciyar da fushin a sama suke kuma da alama ghaz princess ce ta kunnosa dan haka ya dan maida kallansa akan bahar itama yaga fuskarta a hade take sosai dan haka ya dauke kansa daga kansu yana shigewa gabansu tarea keela sauran fadawan na bayansa sai securities a bayansu suma.

Kokarin barin hanyar bangaren sukeyi Asim da da nasa sabbin securities din suka sako kai hanyar dan isa bangaren mahaifiyarsa da suka iso a cikin daren ranar batareda sanar da ko sultan dawowansu ba sbd a yanxu sultan din kansa maqoyinsu ne da suke jin tsananin xafinsa sosai a zuciyarsu amma a zasu fuskancesa a ruwan sanyi kaman yanda a ruwan sanyi zasu fuskanci komai duk da ba lallai su iya hakan ba tinda zuciyoyinsu a zafafe suke tin asali akan komai da kowa ma,

Aslam ce da meryam a tareda Asim din sbd daga bangaren Sultan suke sai a lokacin sukaje suka gaidasa tinda suka dawo a jiyan,

Akan Aleey idanuwan Asim suka fara sauka take yaji wani irin dumi me sanyi yana sauka a cikin jininsa sbd bayan Aleey daya isar da idanuwansa suka sauka akan Bahar wadda idanuwanta suka dago a natse itama ba tsammani ta gansa ta kallesa cikeda mamakin ganinsa sbd harma ta manta dashi a rayuwar duk da ita baida laifin komai a gurinta sbd bai taba cutatar da ita ba bare yi mata wani abin daya cutatar da ita din bayan imebēti dayaso maidata kuma tinda aka tafi da ita zuwa bangaren gyara a wancan lokacin bata dake jinsa ba bare ganinsa ba sai ayau din,

Ya sauya sosai sbd ya samu nutsuwa gangar jiki da hutu duk da jinya yayi batareda sanin kowa ba,

Yanda Asim din yake kallanta zuciyarsa na sake tsimuwa da wata tsaftacciyar soyayya da kaunarta me karfi da jin duka a yanzu duniya bayason komai harma da mulkin indai zai sameta ta ishesa rayuwar da duk yake so yayi a duniya,

Akan hannunta dake riqe cikin na Sultan NUAB idanuwansa suka sauka yaji wani irin zafi ya ratsa zuciyarsa me kaifin gaske yana dan yunqurawa zai nufota keelah ya dage gefe da gaban rigarsa da babu komai a jere jikinsa bayan bindigogi guda biyu da wasu irin daggers masu tsantsan hadari batareda ma ya kalli Asim din ba kaman baima san yunkurin dayake yi ba na nufosu suna cigaba da tafiya,

Aleey ma dan gefensa ya kalla yana kallan inda NUAB yake batareda ma ya juyoba sbd yana ji a jikinsa gurin ya qarasa daukewa da dumin dayake jin zai iya zama makashi duk da Babu alaman ko kallan inda Asim da yan uwansa suke yayi baima san sune a gurin ba dan baya kallan kowa bare bawa kowa mahimmanci dazai ganesa,

Aslam ce tayi saurin saka hannunta ta kama na Asim din cikin nata tana dakatar dashi daga kowane irin motsi batareda barin ma NUAB ya ankare dame yake shirin aikatawa ba tana jin zuciyarta na neman hawa da baqin cikin kasa hakura da Asim yayi da bahar wadda alamu duka sun nuna ba alkhairi bace sam a rayuwarsa da tasu gabaki daya harda mahaifiyarsu,

Suna tsaye cak Sultan me mulkin kujeran boyem ya gama wucewa da tsaronsa kafin Aslam ta wuce gaba idanuwanta a jajir hakama meryam kasa cewa komai tayi sbd mamakin da baqin cikin yanda NUAB yana qaninsu amma ko alaman yama sansu a rayuwarsa kwata kwata babu,

Asim ma daya kasa iya komai daga qafafunsa yayi yana bin bayan su aslam din zuciyarsa a toshe yana neman dalilin dazai fitar da Bahar boyem koma qasar gabaki daya ya bita ya kubutar da ita daga wannan rayuwar datake samun kanta a ciki ta rayuwa da NUAB wanda kwakwalwansa

60 / 100