Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   55 / 100

162K to 165K   out of 299.8K words

tsare cikin yaran tsadaddun caterers da aka dauko daga wata qasa tana isowa table din yan Echoes din kanta a qasa cikin uniform dinta sa suke fes sunfi wata designer din tsari da kyau harma da kudi ta fara jere musu ruwan madara me dumin da ake kawowa dan dumama ciki da bawa fatar jiki lafiya.

Dagowa Zee tayi ta kalleta tace

'Allah sarki Sannu da kokari naimah ina salmah ne??

Sauke kai ta sake dan yi qasa girgiza kai alaman Salmah dai kila marigaya zata bi.

Dariya me karfi suka kece da ita gabaki dayansu suna tausawa salmah din wadda da alama Salman dinta na Asim zata bi.

Hidimar biki aka ci gaba da ita a tsare babu tsiya babu talauci babu qaranta koina da komai arziki ne kawai ake saki ana wasa dashi cikin harkar arziki ta masu abun duniya.

Ammi ma a tare take cikin manyan matan duniya da duniya tasan dasu suna bata girmamawa sosai cikin wayewa da ilimi sbd kasancewanta mahaifiyar sultan NUAB me manyan mutane a qasashe daban daban,

Hakama jamaar sultan yasar suna nuna girmamawansu sosai da tarin kulawa ga Ayanaah din wadda ayau duniya ita kadai ma take kalla a matsayin tararuwa ga 'danta sultan LEUL NUAB hakama tauraruwa ga sultan me murabus Yasar almazz sbd babu wanda yaga haile ko Asim, sai 'yayanta mata da akan dole suka shiryo suka fito hidimar sbd gudun asan halinda su hailen suke ciki hakama babu wanda ya tambayi inda suke,

Maraki ma tana gurin ta iso cikin ado me tsarin gasek da koina na jikinta ke daukan idanuwa da adon gwalawalai sedai babu farin ciki ko rahama ko daya a cikin tsakiyar zuciyarta sbd abinda idanuwanta suke gane mata a yanzu shine asalin son da acan baya ma basu gani komai ba a idon sultan akan ayanah,

Baya wani kallanta amma kallo daya yayiwa Ayanah daga inda yake zuwa inda take wanda yayi akan idanuwan marakin jin tayi duniyarta ta tsaya cak,

Abu ne ta gani wanda a yanzu da baya mulki babu wanda zai iya kutse a cikin rayuwar da duk ya zabawa kansa dan haka taji gashin jikinta ma suna miqewa tsananin kishin da babu abinda zai mata bayan kaita ga ciwon zuciyar da zata mace a banza yana rufeta tana jin inama bata samu kanta a rayuwa cikin wainda babu wanda ya taba sanin mahimmancinta har kusan shi wanda ya ajiyeta din,

A yanzu da baya mulki zuciyarsa batada shamaki,rayuwarsa batada shamakin bayyanarda dukkanin abinda yake ransa ko burinsa ga kowace mace ta jinin sarautar boyem da wadda ba jininn sarautar boyem ba yanada ikon auren kowa babu shamaki a wane matsayin take ita?

Nauyi kirjinta yayi mata tana dago idanuwanta ta zubawa ayanah dake zaune a cikin manyan mutane suna kokarin samun kusanci da sanin juna da ita tana kallanta batareda kyaftawa ba tinanika da dama suna dawo mata a zuciya na rayuwar da ayanah ta samu a matsayin imebēti da ita bata taba samu ba,

Su aslam ma dake gurin zuciyoyinsu zafin dayake ciki zai iya babbaka gurin da wuta sbd wani irin abinda basu taba ji bane yake yawo a jininsu musamman aslam datake tabbatarda maganar mahaifiyarsu ayau cewan Ayanah ghaz itace silar dukkanin wani baqin ciki da kuncin rayuwarsu da har abada idan bata bar duniyaba bazasu taba samun farin ciki ba,

Leylah ma bata iya fitowa taron ba tana dakinta ta rufe kanta cikin tsananin baqin cin rayuwar datakejin kaman ta kunnawa bangaren gabaki daya wuta sbd wutar dake cin zuciyarta ta tsana me tsananin gaske datakewa bahar,

Tinda safiyar ta waye bata fitoba hakama Kusan kowa ya manta da ita sbd lamarin da suka tashi a cikinsa ayanah kuwa dukkanin zuciyarta koda ake kowace hidimar tana akan Bahar da batasan tayaya zata fara kallanta a cikin idanuwanta datajin kaunarta a kowane lungun na jijiyar dake gudanar da jini a gangar jikinta,

Jin takeyi zuciya da ruhinta na tsananin matsuwa da son saka Bahar din a cikin idanuwanta da gangar jikinta amma tana daurewa sbd tsoron abinda zata iya ji.

Maa sakinah ma sam bata sake tinawa da leylah dinba sbd dawowan Bahar da kuma rashin ganin fitowan Leylah din dan haka hidimarta kawai takeyi hankali kwance da farin cikinta wani akan wani tinda 'dansu NUAB shine mai iko da mulkin qasar a yanzu da kuma bahar dinta datake a cikin koshin lafiyar da a yanzu tana cikin tsaro da ikon Allah.

Wuni akai cur ana bikin wanda sai dare aka watse zuwa lokacin babu wanda bai gaji ba matiqar gaske dan haka har dare sosai baqi basu gama watsewa ba sai tsakiyar dare kowa ya gama watsewa masarautar ta dauki tsit wanda sai ankwana biyu kafin cikakken motsinta ya dawo  sbd hutun da zaayi na hidimar da kowa gajiya ta ratsesa.

Sultan NUAB ma yana isa bangarensa a cikin daren take aleey shima da keelah suka nufi dakunansu suna barin sauran securities din da zasu ringa sauyin juna wasu na hutawa,

Cikin ruwan zafi sosai masu fidda wani hayaqin qamshin dayake hade da qamshin shower gel dinsa na Aesop na wanka ya shiga a cikin bathtub din ya kwanta tareda rufe idanuwansa zafin na ratsa kafafu da fatar jikinsa yana warware masa duk wata gajiyan dake tattare dashi wanda bai taba samun kansa a cikinta ba tinda ya kafu ya gina ghaz empire dinsa.

Ya dan dauki lokaci a ciki kafin ya fito yayi brush ya fito daure da towel gashin kansa na tsiyayar ruwan da dole ya goge ta busar da gashin nasa dayake cin kayan gyaran da kudinsu kadai zai iya tada wani business din,

Dogon wandon bacci kadai ya saka jikinsa na fidda wani lafiyayyan qamshin tsadaddiyar designer body mist dinsa na Sol de janeiro cheirosa ya sake gashinsa batareda ya kamasa ba ya kwanta kai tsaye tareda lumshewa fararen idanuwansa yana sauke numfashi me sanyi da nutsuwa dan samun cikakkiyar hutawan da babu me ganinsa a gobe kwata kwata.

Acan ma koda Ayanah ta koma itama kai tsaye bedroom dinta ta nufa batareda tasan bahar ta dawo bangarenba ta kalli agogo tana tinanin a wane halin Bahar take ciki a yanzu gashi ba zata iya zuwa ba yanzu dare yayi sosai hakama NUAB yana can tasan zai bata kulawan daya kamata dan haka itama wanka tayi ta rage gajiyarta kafin tayi shirin bacci ta kwanta tareda lumshe idanuwanta ta rufe batareda tabbacin baccin zai taho mata ba dan kuwa zuciyarta na tsaye ne cak guri daya wato akan tsananin matsuwan haduwa da Bahar.

Koina tsit yayi kowa yayi bacci cikeda gajiya da samun nutsuwa da farin ciki tareda har kwanciyan hankali,

Shi kansa aleey ayau baccin kwanciyan hankali da farin ciki yake dan kuwa daga yanxu baida shakkar komai akan Bahar da Ammi a duk inda suke cikin boyem da masarautar boyem din babu wanda zai iya tabasu sbd kuwa kai tsaye mutum yasan mutuwarsa ce yake tabawa.

****a cikin tsakiyar daren daidai wannan lokacin a bangaren Aslam da dukkaninsu suke har lokacin sbd bullet din da aka cire musu su biyun duka batareda sanin kowaba hakama su hailen da Asim din suna cikin wani matsanancin halin da suke buqatar ganin manyan likita koma fita zuwa wata qasar matiqar anason hannun Asim da kafar hailen taci gaba da moruwa.

Suna dawowa daga gurin taron daqyar Aslam ta iso bangaren sbd baqin cikin dayake neman makantar da ita da mummunar ranar da ayau suka sheda da idanuwansu na wani ya karbi mulkin boyem ba Asim ba a kuma lokacinda Asim din da mahaifiyarsu suke kwance cikin mugun hali.

Suna shigowa meryam da babu ta inda ta hango musu nasara sbd a bayyane komai yake Tin farko NUAB ne mahaifiyarsa a zuciyar sultan ya boyesu ya juyar da kowace kiyayyar da zata illata su zuwa kansa,

A yanzu duniya gabaki daya tana iya ganin soyayyarsa me zafi a bayyane cikin idanuwansa dayakewa Ayanah ghaz da 'danta,

A yanzu kam indai sune a qasan zuciya da ruhinsa duniya zata sheda hakan sbd baida kowane shamaki akansu,
Baida kowace iyaka akan ayanah ghaz,
Baida kowane sharadi na sarautar dayake riqesa daga mallakarta da samunta tareda rayuwar da duk yakeso da ita wanda ita ta hango hakan a tattare dashi wanda Aslam bata nutsu ta gani ba sbd wani kallo ne yakewa ayanah da dukkanin nutsuwa da ruhinsa wanda bata taba ganin yayiwa mahaifiyarsu ba bare ma ta taba ganin kowane irin namiji yayiwa mace wannan kallan,

Kallo ne da kai tsaye yake bayyanar da wata tsimammiyar soyayyar da ba ayau take ajiye a gurin da babu wanda ya taba shigarsa ba,
Soyayya ce datake hade da kaunar da babu sirki tareda sallamawa gabaki daya ga wanda akewa ita,

Gashin jikinta ringa tashi yayi tana jin kowace buri da rayuwarta na narkewa suna zubewa qasa a banza sun riga sun rasa komai a wannan fadan sbd ayau ayanah ghaz ta samu dukkanin abinda suke tsananin buri da yaqin nema da rai da lafiyarsu.

Silalewa tayi a qasa bakin gadon da Mamen su take idanuwanta a bude kafe guri daya sunyi jajir ba kyan gani dukkanin qunci da baqin cikin datake ji tana gani a abinda yake faruwa yana shiga kunnuwanta zuwa zuciyarta amma bata iya motsawa ba sbd kusan bata iya dogon motsin komai da jikinta,

A yanxu take tabbatarda rayuwar data rayu a cikinta ta aure da soyayyar mijinta ta mafarkin da baitaba zamowa gaskiya bace,

Ayau ta zuciyarta tana dandana wani zallan baqin ciki da qunci tareda heart break na zambatarta da Mijin datake aure yayi wanda bata taba dandanawa ba.
#MAMUH
09033181070

HAYATEEM
Mamuhgee

98
Rufe idanuwa haile tayi ahankali wasu hawaye masu tsananin zafi suka gangaro daga cikinsu suna bin gefen fuskarta dake kallan sama batateda koina na jikinta ya motsa ba sbd dukkanin nadin da akai tana kwance tana jin komai yana ratsa kunnuwanta sbd koina sautin ratsawa yakeyi a masarautar da wajenta sbd koina kake kaji yanda nadin yake gudana,

Meryam ma data zube gefen mahaifiyar tasu wani irin kuka ne mai tsananin tsimar da zuciya dayake fitowa daga qasan zuciyarta tattare da wani irin dukkanin sarewa daga kowace irin samun nasarar rayuwa,

Kuka sosai takeyi mai wani irin sautin dayake shiga kunnuwan haile tana kasa bude nata idanuwan itama hawayen na gangaro mata jikinta na wata irin rawa mai tsananin radadin baqin ciki.

Aslam data kasa kukan ta kasa iya cewa komai zaunawa tayi a kujera tareda rafka wani irin tagumi tana rintse idanuwanta da sukai jajir suna mata radadi me tsananin gaske,

Shiru sukai dukkaninsu babu motsin komai a dakin bayan na kukan meryam dake tashi ahankali wanda sautinsa ke isa har dayan dakin Aslam din wanda Asim yake kwance yana jin kowane irin sauti a cikin kunnuwa da zuciyarsa suna yaga dukkanin abinda zuciyarsa take riqe dashi tin yarinta,

Rintse idanuwansa yayi wasu zafafan hawayen shima suna gangaro masa masu tsananin ciwo da radadin rayuwarsa data tsaya cak guri daya a yanzu,

Salman ya mutu ya barsa ayanzu baida amintaccen yaronsa da shine yake tsaya masa a komai kuma sbd hidimar nadin sarautar su aleey sun tattara komai sun rufe zancen kaman ba babu wanda ya mutu sbd kawai kada ma hayaniya ta tashi haka akai janaizar wainda suka rasu din tareda su salman din aka rufe tinda safe kafinma nadin sarautar batareda kowa yasan da hakan.

Hawaye ne suka gangaro masa sosai babu kakkautawa yana damqe hannuwansa duk da azabar dayake ji,

Abu dayane yakejin yana riqesa ga rayuwa a duniyar shine BAHAR wadda yasan tana raye bazai taba iya dakatawa ba saiya sameta a rayuwarsa ta zama mallakinsa sbd tin farko ai tasa din ce,

Bahar itace soyayyarta da bayaji baya gani zata saka yayi yaqi da karfin hali ya nema lafiyarsa ya warke ras ya kwatota zuwa rayuwarsa da bazata taba moruwa ba batareda bahar a cikinta ba.

Aslam ma data ga bazata iya cigaba da kallansu a wannan halinba suna buqatar neman lafiyarsu da gaggawa dan da ita ne zasu iya tsayawa su fuskanci komai su tsayu akan komai da suka wahaltawa dan haka a cikin daren ta sake bugawa dan tabbatarda shirin tafiyarsu ya kammala zuwa india ganin likitoci kwararri da dr ya nemar musu dan a cikin gaggawa takeson subar boyem batareda angama duka shagalin bikin sarautar ba dazai hana a gane halinda suke ciki.


****Washe gari da safe babu wanda ya tashi da wuri a cikin masu iko da masaurautar a yanzu sbd hutun gaske suke buqata musamman da a ranar babu baqin da zasu shigo masarautar sbd sai sultan ya huta da kyau sai jibi baqi zasu iya fara shigowa bankwanan tafiya da taron karshe.

Bahar sai kusan karfe goma da mintina ta farka cikin samun lafiya da karfin jiki tareda jin ta samu dawowan kuzarinta da nutsuwanta.

Maa sakinah bata dakin dan haka kai tsaye toilet ta nufi tareda brush da wankan da bata samu karfin yi ba dakyau jiyan.

Da ruwan dumi sosai tayi wankan ta fito daure da towel tana nufar gaban mirro Maa ta shigo dauke da tray qarami dayake dauke da ruwan tea na herbs masu kyau da zuma ta nufota tana kallanta a sake tace

'Lokacin shan magani yayi'

Juyowa bahar din tayi ta kalleta tana dan sanyaya fuska sbd bata son maganin,

Murmushi Maa tayi tana ajiye tray din tareda daukan zuma ta zuba a cup da tea din yake ciki ta juya a natse ta dauka ta nufo bahar din ta miqa mata,

Tana karba juyawa tayi ta dauko mata magani ta dawo gurinta tana zaunawa gefen gado dayake kusa da gaban mirror din tana jiran tasha dan tea din saita bata maganin,

Daqyar tasha maganin maa ta miqa mata tissue ta goge bakinta tana juyawa dan fara shiryawa.

Babu wani abu bayan body oil datake shafawa da sai body milk me sanyin qamshin da yake kama fatar jiki shima kamshinsa ya ratsa duk inda ka shiga wanda yake asalin na shuwa arab(SHUWA INCENSE AND MORE 07042293387)

Doguwan riga ta saka tareda zaunawa gefen Maa sakinah wadda salmah ta shigo ta jerewa breakfast dinsu a dakin.

Tana zaunawa breakfast dinsu sukai a natse kaman yanda suka saba duk da bataci sosai ba dan yanayinta da bai gama dawowa daidai ba.

Suna gamawa har lokacin babu wanda ya fito dan haka basu dauka akwai wanda ya farka ba dan haka kwantar da kanta maa tayi tafara gyara mata gashinta a natse da kulawa tana bata labarin yanda akai nadin sarautar duk da itama bata hallara ba amma dai kusan taga komai a tv a lokacin da akeyi.

Shiru bahar din tayi tana sauraronta cikeda nutsuwa da sanyin jiki tareda tinanin yanda zuciyarsa zata iya tafiyar da milkin dubban miliyoyan mutane da qasa guda.

Ajiyan zuciya ta sauke ahankali cikin sanyi tana sake lumshe idanuwanta ahankali sbd jin jikinta na sake sanyaya ta lafe a kafafun Maa din wadda take cigaba da gyara mata kai ahankali tana mata fira me sanyaya zuciya.

Salmah ce ta shigo ta tattara kayan abincin da suka ci ta sake gyara dakin ta fice,

Wuni sukai cur abinsu a daki batareda fitowa ba Maa na sake tarairayarta tana dan ta sake warwarewa daga zazzabin data warke,

Sunyi nisa a abinda sukeyi cikin kwanciyan hankali har lokaci ma yaja sosai cikin nutsuwa sukaji knocking din kofar a natse wanda ya saka Maa sakinah dan waiwayawa ta kalli kofar tana qarasa daurewa Bahar din gashinta me kyau da tsayi tana goge mata gaban fuskarta da wipes me kyau.

Bude kofar dakin akai kai tsaye batareda an sake bugawa ba wanda kamshin daya saka maa din sake juyowa a natse ta kalli kofar ya shiga hancin su duka biyun amma bahar din bata waiwayo ba.

A maimakon Sultan NUAB da qamshinsa ya ratsa hancinsu zuwa zuciyoyinsu Ayanah ce tsaye a bakin kofar idanuwanta a kafe kan BAHAR wadda bata juyoba.

NUAB ne da kansa ya kawota har kofar dakin batareda yace mata komai ba kawai yayi mata Alkwarin fada mata komai tareda kaita har inda Abaass yake idan lokacin daya kamata tasan komai din yayi ya kuma sakata alkwarin bazata sake tambayarsa ba har sai ya fada mata komai da kansa idan komai ya lafa din ta kuma yadda da hakan duk da zuciyarta zata quntatu da yawa da hakan,

Shine ya bude mata dakin maa din da bahar take ciki ya juya yabar bangaren batareda waiwayowaba sbd kada ya sauya alkawarin barin bahar din Amminsa ta samu lokacin datake so da ita.

Dago kafafuwa Ayanaah tayi ahankali tana sakowa cikin dakin a sanyaye har lokacin idanuwanta na akan bahar dake kwance akan kafafun Sakinah batareda ta juyoba,

Sakinah ce jikinta ya fara mutuwa da yanayin datake hangowa Ayanah tafara shiga na tsananin kaunar da batada sirkin da zaka iya bada rayuwarka da abinda rayuwarka ta mallaka akai datake yiwa Bahar ta saki kan bahar din tareda zame kanta cikin kulawa ta ajiye akan pillow tana miqewa tsaye dan matsawa ta bawa ayanah guri.

Jin hakan ya saka bahar juyowa a natse tana rashi zaune cikin sanyi da mamaki daidai nan Ayanah ta iso gabanta ta tsaya cak idanuwanta akanta tanajin kaman zuciyarta da kirjinta bazasu iya daukan girman kauna da soyayyar dataji tana yiwa Bahar dinba.
#MAMUH
09033181070


HAYATEEM
Mamuhgee

99
Wata irin mutuwa jikin Bahar yayi a lokacin da idanuwanta suka sauka akan macen da itace rayuwar mahaifinta wanda bai hada matsayinta da girmanta da kowaba a zuciya da rayuwarsa,

Ayau da babu rayuwarsa a duniya itace macen datafi komai da kowa daraja a zuciyar namijin da ayanzu kuma shine ya shigo rayuwarta,

Bayan duka maza biyu ita kanta wani irin yanayi me karfi da bazata iya fadan koma menene ba take ji akanta duk da babu kusanci ko wata haduwa a tsakaninsu,

Fuska da kammanin mahaifinta sak da sak take gani a kowane gefe na kammanin fuskar Ayanah ghaz wadda takeda matsayin da kaf a duniyar mazaje biyu zuwa uku da babu me shi,

Wasu hawayen kewan Baa dinta ne suka ciko mata idanuwanta wanda take jin inama ba itace ayau din take haduwan fuska da fuska ba da Ayanah ghaz,
Inama mahaifinta ne wanda hakan shine burinsa har ya bar duniya,

Ya ganta amma a daidai lokacinda daqiqun zamansa duniya ya qare,
Ya ganta a numfashinsa na qarshe batareda ya ambaci sunanta ta amsa ba kaman yanda shine burinsa,

Sauke idanuwanta tayi ahankali tana kasa iya cigaba da kallan halittar da zuciyarta take jin kaman tana kallewa mahaifinta itane dan cika masa burinsa amma zuciyartata bazata iyaba sbd shine kadai take gani a fuskar ta ayanah ghaz dan haka ta fara kokarin dauke idanuwanta

55 / 100