Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   48 / 100

141K to 144K   out of 299.8K words

danne zuciyarta Akan ta jira safiya waye sbd yanzu dare yayi,

Haka dare ya fara ratsowa tana Zaune daram a kujera ta kasa motsawa bare kwanciya sbd kowane lokacin Jin takeyi yaqi Zai iya narkewa a masarautar dan haka hankalinta yake tashi sbd ita Bahar din kadai takeji,

Daqyar taga gari ya fara haske dan haka ta fito ta fice Kai tsaye batareda kowa ya tashi ba ta nufi bangaren NUAB.

Tin daga nesa ta fahimci sabbin da qarin securities dinsa masu yawa ya qaru duk da ya halinta baya a tsaye guri daya Kai tsaye kofa suka bude mata ta shige Bayan ta gama ware ido a cikinsu bataga alamar zancen ya iso bangaren ba dan haka tana sako Kai makeken lafiyayyan palon Kai tsaye dakin Bahar din ta nufa ta budesa ta fada batareda tinanin komai ba.

Ko data shiga Bahar din na Zaune Akan daddumar datai sallar asuba bata tashi ba tayi shiru ta zubawa gabanta idanuwanta da sukai jajir sbd kukan kadaici da kewan mahaifinta ta kwana tanayi Wanda ya saka fuskarta kumbura sosai.

Shigowan Maa ya sakata dagowa a natse cikin sanyi tana ganin itace wasu hawaye masu tsananin dumi suna gangaro mata ta miqe tsaye tana qasa da kanta cikeda sanyin jiki sbd jinta takeyi tamkar a kejin da babu iska ko kadan sbd gabaki daya ko hasken rana bata sake gani ba tinda ta shigo bangaren.

Kama hannunta Maa sakinah tayi cikin nutsuwa ta jata zuwa bakin sofa suka zauna ta dan sake kama hannunta cikin kulawa da tausasa harshe tareda boye damuwan datazo da ita tace

‘Bahar ba nace ki rage yawan kukan nan ba??
Baida amfani zaki kamu da wata ciwon idan Kina yawan kukan nan ki Dena’

Wasu hawayen ne suka ciko idanuwanta amma basu gangaro ba ta dago kyawawan idanuwanta zatai magana aka bude dakin Kai tsaye a natse Wanda ya sakata dauke kallanta daga kofar wasu hawayen masu tsananin baqin ciki suna gangaro mata ta fasa wani sabon siririn kuka a hankali zuciyarta na cikewa da baqin cikin samun kanta a rayuwar da Sam bazata iya ba da kuma samun Wanda take ganin asalin asali baisan menene hankali ba,

Maa sakinah cikin nutsuwa ta juya sedai batasan lokacinda ta dawo da fuskarta ba cikin wata irin rikicewa da kunya da takaicin kasa riqe kanta datai tazo bangaren a daidai wannan lokacin.

Farin wandon bacci ne a jikinsa dogo har qasa amma babu Riga a jikin nasa hakama wandon bai hau daman cikinsa da kyau ba iya inda qugunsa ya fara ya tsaya Ana ganin tambarin sunan farin tomford tight short din dayake jikinsa ta saman Wanda Zai iya saka mata da yawa rikicewan ganinsa a hakan,

Gashin kansa me tsayi ne daure da qaramin black Band a tsakiyar kansa bai Wani kamu ba sosai fatar jikinsa sai daukan ido takeyi,

Akan kunnuwansa dake bacci yaji shigowan mutum palon dan hakane ya fito kuma Kai tsaye nan ya bude dan dubawa sbd ya fahimci yarinyar na tasting din patience nasa bai tsammanin ganin Maa sakinah ba dan haka dakatawa tayi daya kofar tareda bude bakinsa ya gaidata ta amsa batareda ta juyoba duk a rikice sbd ta kasa iya juyowa kallansa a hakan.

Ko bahar din bai kalla ba ya juya yabar dakin yana kallan time a agogon dayake palon ya koma bedroom dinsa.

Maa sakinah kasa magana tayi sukai shiru dukkaninsu na tsawon mintina kafin Maa sakinah tayi karfin halin fidda takardar data dauko tazo da ita ta budewa Bahar din tace

‘Bahar akwai wata doguwar magana ne a tsakaninki da Li’ul ASIM?

Numfashi Bahar ta sauke a sanyaye ta girgiza Kai,

‘Kinsan takardar menene wannan Bahar?
Abinda yasa na fara tambayar ki wannan takardar daga sultan ta fito dauke da sunanki da sunan Li’ul ASIM an zartar da hukuncin basa ke a matsayin imebētinsa…..

Cak hawayen Bahar din suka tsaya daga tsiyaya ta dago ta kalli Maa sakinah cikin wani irin sabon mamakin da bata taba shigaba.

Takardar ta kalla da idanuwanta tana kokarin karanta abinda yake rubuce amma ganinta ya kasa zama daidai ta sake kallan Maa sakinah tace

‘Maa dan Allah zan koma GHAZ bazan iya rayuwa anan ba dan Allah Inason komawa’

Cikin sabon nauyin daya danne kirjin sakinah ta girgiza Kai idonta yana ja tace

‘Bahar bazaki taba komawaba a yanzu sbd akwai aure a kanki Wanda babu Wanda ya San dashi hakama yanzu gashi Kina a matsayin imebetin ASIM Wanda kinma riga kin zama a rubuce dan haka babu abinda zai fidda ki BOYEM kuma matiqar dai a raye kikeso fitar’

Girgiza Kai Bahar tayi tana jin jikinta yana daukan zafi tace

‘Maa babu ko daya a cikin biyun danake so auren da imebetin bazan iya rayuwa anan ba’

Dakatar da ita Maa sakinah tayi sbd da alama zancen bai iso nan ba dan haka bata fatan ya iso tana nan dan haka Miqewa tayi sbd maida takardar kafin ma asan ta dauko hakama ko yayane hankalinta ya kwanta datasan babu maganar komai data hada Bahar dashi ASIM din data danganci kowace kalmar soyayya wadda zata iya zama cikin matsalar hakan amma tinda babu taji dan sauki zata jira taga idan NUAB zai iya kubutar da Bahar din daga wannan mummunan kaddarar dake shirin hawanta ga kuma nasa auren na biyu dake shirin hawa kansa shima.

Miqewa tayi zata fice Bahar tayi saurin miqewa tana gyara babbar rufar sallar dake jikinta tana biyota a baya.

Wucewa Maa sakinah tayi batama San Bahar din na bayanta ba saida suka Kai tsakiyar palon Maa ta juyo tana kallanta da mamaki tareda rage sautinta tace

‘Bahar ki koma zamanki a nan yanzu shine babban tsaron da zaki samu da kariyar da kaf BOYEM sultan ne kadai ya isa ya fiddo ki amma bayanshi babu Wanda ya isa.

Girgiza Kai Bahar tayi tana cewa

‘Bazan iya zama ba ni kadai Maa dan Allah mu tafi tare’

Girgiza Kai Maa din ke kokarin yi Bahar tayi saurin yin gaba cikeda tsananin damuwan bazata iya tsayawaba ma bare ta zauna idanuwanta na sake cikowa da hawaye.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laoualiHAYATEEM
Mamuhgee

83
Fitowa Bahar tayi da sauri daga kofar palon tana kokarin qarasa fitowa securities suka miqe gabaki dayansu suna tabbatarda tsare kowace kofar batareda sun dauke idanuwansu akanta ba,

Jin tayi kaman zata Dora hannu akai ta zunduma Ihun da ko zuciyarta zata samu sassaucin abinda take ji ta juyo ta kalli Maa tareda fara tsiyayar hawaye ta riqeta da dan karfi tana cewa

‘Maa kada ki barni anan dan Allah ki tafi dani Zuciyana fashewa zeyi dan Allah Maa’

Yar hayaniyar ce ta fidda aleey Wanda kunnuwansu suke sharp shima Akan kowace motsin bangaren daga waje.

Ganin Bahar ya sakasa qarasowa yana dauke idanuwansa daga kallanta shima ya bude Baki ya gaida Maa kafin ya gaida Bahar din wadda batama jin komai tsananin quncin barin bangaren take ji.

Waya Aleey ya fidda ya saka kiran NUAB yana dauka cikin baccin daya koma take aleey ya sanar masa abinda yake faruwa a kofar na Bahar ta tsaya Akan saita bi Maa.

Katse wayar yayi tareda saukowa gadonsa ya fito wannan Karan babu komai a jikinsa Bayan tight short din Wanda ya saka lafiyayyar fatar jikinsa bayyana sosai tana Wani daukan ido tareda kakkarfan jikinsa
A yanda yake yana bacci a hakan ya fito babu abinda ya damesa yana fitowa dukkaninsu suka sauke Kai sbd girmamawa suna gaidasa.

Akan Bahar idanuwansa masu tada tsigan jiki a daidai lokacin sbd baccin daya taso suka sauka tana jin saukan idanuwansa akanta taqi juyowa saima sake riqe hannun Maa tayi wadda itama bata juyoba tana cigaba da tsiyayo hawaye.

Kallan seconds yayi mata batareda yace komai ba kafin ya kalli aleey yace a barta ta tafi kawai sbd yasan bama Wanda Zai iya komai akanta.

Bai bude Baki ya furta ba kallan aleey kawai yayi ya Juya Wanda aleey yasan me hakan ke nufi ya kalli securities yace su bari ta tafi kawai.

Bada hanya sukai suna bata hakurin da bataji bata gani fatarta kawai tabar gurin.

Suna barin bangaren ta sake riqe hannun Maa da dan karfi tana goge hawayenta da hannu daya zuciyarta na dan samun sassauci.

Suna isa bangaren wishmah Kai tsaye daki suka wuce Bahar na shiga ta sauke ajiyan zuciya me sanyi a boye tana Zaunawa kan sofa ta dafe goshinta tana rufe ido tinaninta na dawowa damuwa da tsananin jin tsanar nan din yana sake shigarta da gaske takeyi ANJOM take so tafi son can Akan nan din.

Maa sakinah toilet ta shiga tana fitowa ta samu ta dan kwanta dan kanta ciwo yake itama sosai sbd bata rintsa ba kuma a yanzu ma da Bahar din ta biyota tsoronta da zulluminta yafi qaruwa.

Baccin da bata tsammata bane ya saceta me karfi Wanda Bahar ma data dade Zaune shiru cikin damuwa Salmah na shigowa gyaran dakin da zata fita sai kawai ta miqe a sanyaye da babbar doguwar Riga a jikinta ta bita zuwa kitchen cikinsu ko zata samu dan sassaucin damuwan datake ciki.

Karfe goma na safe NUAB ya da securities dinsa suka bar cikin masarauta zuwa Wani business da shine dole zaiyi sealin nasa hankalinsa kwance ya tafi sbd yasan koma me ASIM zeyi hukuncin da zai masa ko mahaifinsa bazai qwacesaba dan haka ya tafi ba shakkar komai.

Karfe biyun rana tanayi dukkanin shirye shiryen wankan lalle dana fara gyaran Amarya Leylah da mahaifinta ya aiko dukiyar gaske dan gyaranta da zaa fara daga yau din a inda ake gyaran kowace macen jinin BOYEM kuma a gurin ake gyaran kowace imebeti sbd itama sultan zata zama tasa dan haka NUAB na ficewa takardar ranar auren ta kuma fitowa daga sultan wadda ta sake rikita masarautar da fara shiri da murnar auren Wanda zaayi a sati biyu masu zuwa.

Komai da komai na musamman na gyaran mace zuwa matakin karshe na fitowanta mace ya kammala daga bangaren tenya dan haka Kai tsaye Bayin bangaren ta fara tarawa batareda Shan wuya ba kuwa ta samu Bahar din a cikinsu dan haka ko toilet bata bari ta tafi daga inda take tsaye tasa aka jata zuwa inda zasu.

Suna fitowa sakon kira daga sultan ya samu tenya dan haka ba bata lokaci ta aika su ita kuma ta wuce.

Bata jimaba ta dawo da umarnin sultan me Zafin gaske daya sakata cikin wasu irin manyan shakka da zullumi harma da tinani me tsoro Kala Kala sbd Kai tsaye kebataccen gurin da daga Bahar har Leylah bazasu fitoba sai Angama musu komai tas tukuna hakama babu Wanda zai san a ina suke a cikin masarautar har a kammala ko wanene bazai sani ba wannan umarninsa ne dan hatta ita bazata fitoba sai komai ya kammala.

Cikin shakka aka kaisu Wani sabon bangaren da babu Wanda yasan dashi an riga an tanadar musu komai dan haka ko yawo babu me shiga bare fitowa daga su se bayin da aka tanadar musu.

Koda suka isa Bahar na cikin mummunan halin damuwa me girma da baqin cikin da batasan ma yata zata furta ba sbd kowace dama an rufe mata dan haka Kai tsaye Wani lafiyayyan babban dakin dayake komai iri daya da Wanda aka kai Leylah aka kaita tareda rufo mata kofa aka barta tsaye tsakiyar dakin tana bin kofar da idanuwanta da sukai jajir.

Silalewa tayi ahankali tsakiyar dakin tana zubewa qasa tareda dunqule jikinta guri daya tana Jin hawayenta na kafewa sbd girman halinda take jinta a ciki.

Tayaya zata zama imebetin kowa a duniya Bayan ita din ba baiwa bace,
Ba siyanta akai ba,
Jinin sarauta ne yake yawo a jikinta kuma komai lalacewan tata sarautar mulki dai mulki ne,
Tayaya zata zama macen da amfaninta kwanciya da biyan buqata ne?
Tayaya zata zama imebetin Wani wanin ma Wanda yake matsayin dan uwa ga wanda akwai igiyoyin aurensa akanta Wanda a yanzu koma yayane tana fatar zafinsa ya kubutar da ita ga wannnan masifar data samu kanta.

Tenya kuwa babban gyara zatai wannan Karan sbd Matar NUAB dinta ba matar da zatai wasa da gyaranta bane ko kankani hakama imebētin ta ASIM zata samu komai dakyau daidai da Leylah sbd ta cika umarni da tsarin al’ada.

Karfe hudu daidai tana bugawa aka fiddo su zuwa gurin wankan dayake cikin inda suke bayi na jere suna jiransu.

Bahar ganin inda kaddara me muni ta kawota kuka ta fasa mai tsima zuciya tana qanqame jikinta a lokacinda ruwan lallen masu dumi sosai da Wani irin kamshi suka fara ratsata.

Leylah dake cikin baqin cikin ganin Bahar din da zallan asalin kyau datake dashi batareda tambo ko daya a jikinta ba komai nata nutsuwa da kwanciyan hankali kawai yake nuna duk da a cikin kuka na Wani irin mummunan baqin ciki da tashin hankali take Wanda hakan kuma yake dan sanyaya zuciyar Leylah din tareda ganinta cikin ruwan lallen auren NUAB dinta.

Dukkanin yanda al’ada ta tanada na jiqon su a cikin ruwan lallen masu dumi da qamshi tareda wasu abubuwan haka akai musu wuni guda sai yamma sosai suka koma dakunansu zuwa lokacin qarfin Bahar ya fara qarewa gurin kuka yanzu tsoro taji yana shigarta tana fatar zuwan NUAB a Karan farko na rayuwarta sbd shirin gaske gadan gadan akeyi na tabbatarda zamanta imebētin da tafison ta mutu tabar duniya da hakan ta kasance da ita,

Acan kuwa Maa sakinah koda ta farka bataga Bahar ba Jin tayi tana Neman zarewa sbd samun tabbacin an tafi da ita kenan.

Rawa da Wani irin fizga jikinta ya fara yi ta kasa zama ta kasa tsayi sai ta nufi hanyar dakin Ayanah ta dawo sbd batasan me zata fada ba tinda a daure take da mugun Alkawarin da Ayau bataga ranarsa ba duk da sunyi hakan ne dan hana dawowan ciwon Ayanaah dan kila bazata iya daukan labarin Abaas baya duniya ba ya tafi yabarta bar abada sedai a mafarki.

Fitowa tayi a karo na biyar tana zuwa duba NUAB ko ya dawo amma bai dawo ba dan haka ta sake dawowa.

ASIM duk da bangaren mahaifiyarsa tamkar Ayau Ana zaman makokin mutuwarsa ne sbd tarin baqin cikin da suke ciki tamkar zuciyoyinsu zasu bindiga su watse haka suke ji amma shi a zuciyarsa yau tafi masa kowace rana sbd tabbacin zuwa Yanzu imebētinsa ta shiga ruwan wankan lallen daya wanketa daga budurwa zuwa macen da zata tare.

Tsananin farin cikin dayake cikinsa ne ya saka a fada ya wuni cikin manyan fada da aketa meetings da zama Kala Kala Akan auren NUAB da imebetin ASIM.

Sai dare sosai motocin NUAB suka sako Kai masarautar dan haka Kai tsaye Hutu yake buqata yana shigewa aka rufe kofar bangarensa sai safe kuma.

Asubar fari tenya ta tadasu tareda jiqa su a cikin ruwan madarar da wasu abubuwan Wanda suka saka jikinsu mutuwa sosai basu kammala ba sai karfe goma kowacensu na komawa daki baccin abinda yake cikin abinda suka sha ya daukesu a buge babu Wanda ta sake motsawa alaman farkawa bacci sukeyi sosai me karfin gaske.

Karfe Tara Maa sakinah na safe ta isa bangaren NUAB bai farkaba a lokacin dan haka zaman jiransa ta dasa sbd tin jiya wayoyinsa a kashe suke haka ta wuni kira babu me shiga gabaki daya ta fice hayyacinta sbd hatta bangaren da Bahar zata zauna a matsayin imebeti har an fara shirinsa da sunanta da komai.

Aleey ne ya fara fitowa yana ganin Maa ya mata kallan seconds take ya hango ba lafiya gaidata yayi tareda kallan kofar dakin da Bahar take ya dawo da kallansa kan Maa din wadda gabaki daya hankalinta kaman baya jikinta dan kuwa ko rufewa idanuwanta da sukai jajir basu yiba a Daren bare rintsawa.

Time Aleey ya kalla yaga lokacin tashin NUAB beyiba amma bayajin ko wace matsala ce Maa tazo da ita zata bari ya barsa sbd dole abu biyu ne kodai Amminsa ko GHAZs princess.

Kai tsaye hanyar bedroom dinsa datake a killace baa ma ganin hanyar ya nufa yana daga wayarsa dan saka kiransa batareda shiga dakin ba.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laoualiHAYATEEM
Mamuhgee

84
Cikin bacci a natse ya miqa hannunsa ya dauki wayar da aleey ne kadai yake kiransa da ita sbd emergency,

Yana dauka baya buqatan magana maida sexy idanuwansa na bacci masu tayar da gashin jiki yayi ya Lumshe maganar Aleey daya fara masa bayani a natse tana shiga kunnuwansa daya bayan daye a kammale.

Bude idanunwan nasa yayi a gabaki daya a hankali batareda ya motsa ba bare cewa komai,
Kashe wayar yayi Bayan ya dan Lumshe ido yana jefar da ita gefen gadonsa dayake tsakiyar dakinsa cikin wani irin tsarin dayake da daukan ido da kyau da aji.

Baro aleey yayi yana fitowa daga hanyar wadda ta saka Maa sakina kallan hanyar sai taga ba NUAB din bane ta miqe tareda ficewa Bayan ta cewa aleey tana Neman NUAB din da gaggawa idan ya fito.

Tana barin bangaren kafin ta isa bangarensu aka fara shigowa da wasu irin Kayan al’adar shigar Leylah lalle komai na sake daukan harama.

Zama tayi a tareda Ayanah a palon tana tayata farin cikin dole da hidimar datake yi zuciyarta na sake ninkuwa a cikin tarin baqin ciki da zullumi tareda Neman mafitar da a yanzu itama ta yadda Bahar din tabar BOYEM tin bama yanzu ba sbd wadda ma take anan din sbd ita batasan wacece ita ba gashinan tana farin cikin NUAB yayi aure da wata daban batareda tasan da akwai Bahar din a duniya ba.

Kaman daga sama batareda sanarwar komai ba qamshinsa suka fara jin a sako Kai dan haka a tare suka juya da kansu hanyar shigowa palon suka kalla daidai nan yake sako kansa yana sanye da three quarter din farin jeans na Hss da farar sleeve shirt ta anioyosh fuskarsa Amminsa ta kalla cikeda mamakin ganinsa a lokacin duk da bai shigo ba yau din amma yanzu ba lokacin shigowan tasa bane,

Gaidata yayi cikin kulawa da kauna tareda rankwafo wa yai kissin tsakiyar kanta a hankali kafin ya Hadiye wata nutsuwan datake calmin nasa ya juyo ya kalli Maa sakinah itama ya gaidata nutsuwansa na hade har lokacin,

Amsawa tayi zatai magana ya Katseta cikin nutsuwa da cewa

‘Ina take??

Kallansa Maa sakinah tayi tareda dan satar kallan Ayanah wadda ta kallesa da dan mamakin wa yake tambaya.

Kasa basa amsa Maa sakinah tayi tana kokarin miqewa dan barin palon ya sameta a daki sai idanuwansa suka sauka Akan tarin Kayan dake palon ya tsayar da idonsa Akan rubutaccen sakon da dole daga sultan ya fito.

Amminsa

48 / 100