gurina ni na yafe masa sbd nasan dalilinsa daga baya na hakan hakama ko babu dalili tinda zamansa nakeyi dole zan fuskanci damuwa da baqin ciki na zamantakewa wanda gashi a yanzu ya wuce,
Ka aje komai ka bar komai ka bari zuciyarka datake tsananin sonsa ta karbesa,
Ka aje fushinka ka fuskanci matsayinsa daya wuce komai da kowa...
Ayau ina fada maka ka dauka umarni ne ko shawara ko baki koma menene ayau ina fada maka ka ajiye duk abinda kakeji bazaka sake disrespecting nasa ba zaka girmamasa zaka bari zuciyarka ta karbesa matiqar kanason naci gaba da rayuwa a matsayin mahaifiyarka........
Da wani irin slow me mugun zafi da wani duhu da wuta dayake ganin suna ci a idanuwansa da kirjinsa ya juyo yana kallanta fuskarsa na qarasa komawa jajir ba kyan gani yana kasa motsawa bakinsa na mutuwa daga furta kowace irin kalma.
Shi kansa sultan din dago jajayen idanuwansa yayi ya kalli Ayanah din wadda idanuwanta sukai jajir wasu hawaye masu tsananin radadin kalman data fada suna gangarowa daga idanuwanta sbd tasan ayau NUAB zai shiga mafi qunci da radadin zuciyar dabai taba shiga ba jin hakan daga bakinta.
Wani irin sanyi dukkanin jikinsa yafara a hankali sbd ayau ya samu kalman datai breaking zuciyarsa kacakaca a take batareda qara kowane second ba.
#MAMUH
09033181070
HAYATEEM
Mamuhgee
153
Hawayen fuskarta dake gudun sosai ya saka sultan takowa gabanta har lokacin zuciyarsa daci take masa sosai sbd ganin yanayi halinda suke ciki a tsakaninsu da babu wata kauna ko soyayyar data wuce tsakaninsu dan kuwa sune haske idaniya da ruhinsa da ayau yake tsaye sbd soyayyarsu daya riqe ya hana kansa sakewa ga kowane irin challenge har suka kawo inda suke yanxu amma gashi suna tsaye cikin jin zafin juna maimakon kaunar dayake fatar su rayu a cikinta.
Rintse idanuwansa da har wani radadi sukeyi NUAB yayi jijiyoyin hannuwansa dana kansa duk sun fito.
Bai iya cewa komaiba ya juya a hankali yabar palon idanunsa na fidda wata zafi,
Binsa Ammi tayi da kallo hawayenta na sake gangarowa tana daga kafa kaman zata bisa ta rungumosa Sultan ya saka hannuwansa biyu ya riqota yana rungumeta a natse sbd a yanzu NUAB din na buqatan space sbd ayau yaji abubuwan da zuciyarsa zata jima tana tafasa bata saukoba kafin ya fahimci gaskiyar da suke kokarin fada masa ya dawo daidai dan kuwa shi kansa yasan kaman yanda yake tsananin kaunar dansa haka NUAB yake kaunarsa kawai zafi ne na rabuwa dasu daya kasa cirewa aransa tin yarintar.
Kuka Ammin keyi a hankali a jikin sultan din tana jin kaman kalamanta sunyiwa NUAB din tsauri.
Zaunar da ita sultan yayi ransa ba dadi shima ya rungumeta yana kasa cewa komai dan haka sukai shiru dukansu.
Shi kuwa yana sako kai kofar Aleey ne ya fara ganinsa fuskansa kawai ya fara kalla bai iya qarasa kallan idanuwansa ba yayi gefe yana buda masa hanya idanuwansa na sauya take sbd ganin halinda ubangidansa yake ciki wanda kusan hayaniya sosai suka jiyo daga ciki a tsakaninsa da iyayensa wanda ba dan adam dayake da daman shiga dan haka duke a tsuru suna jiran iyayen gidansu dukansu.
Wata irin aura ce ta zafinsa kawai ta bugi dukkaninsu dake kofar take kowa yayi qasa da kansa fadawa ma dake hanyar ficewa bangaren zubewa qasa sukai da sauri kansu a qasa sbd tamkar guguwan wuta haka suka ga tahowan tasa cikin wata zafi da zafaffen izzar mulki.
Aleey da keelah ne suka bi bayansa babu wanda idanuwansa basu sauya ba a cikinsu musamman aleey shi keelah kuwa a lokacin ya samu damar wani me laifin akansa abinda suke ji din zai sauka.
Kai tsaye bangarensa suka nufa wanda suna tinkarowa tin daga nesa kowa ya miqe suna shiga wata irin nutsuwa sbd a tafe suna iya hango yanayin ba daidaiba.
Koda ya iso an wangale masa kofa hatta kofar shigewa palo an an bude masa dan haka yana isowa shigewa kawai yayi aleey ya rufe kofar yana juyowa ya bada umarnin ba shiga ga kowa kaman yanda aka saba duk da daman babu me zuwa bangaren bayan masu aikin da suna gamawa suke barin bangaren.
Yana shiga kai tsaye palonsa ya wuce na qurya shima yana isa kokarin daidaita kansa yayi da zuciyarsa ya nufi inda zaiyi sallah ya tada sallar ishai da aka aka fara yabi jam'i daga nan batareda ya iya tafiya masallacinba dan gabaki daya fuskansa ba kyan gani,
Ana idar da sallar jin yayi numfashinsa na sarkewa yana kasa fita daidai hakama wani irin zufan gaske yake fitarwa idanuwansa har wani rufewa sukeyi yarintarsa da duk abinda ya taso a cikinsa yana dawo masa da tinanin da radadin da kaunar dayake wa mahaifinsa me karfi da kishinsa dayake tada duka wani fushinsa,
Miqewa yayi bedroom dinsa ya nufa bai tsaya komaiba tin daga kofar bedroom din yafara bude botiran gaban rigarsa ya zare ya jefar yana zare komai daya baya daya kai tsaye ya nufi glass door din dake dakin ya budeta gabaki har qarshe yana saka kafarsa batareda komai a jikinsa ba bayan tight CalvinK short underwear dake jikinsa fara qal ya isa bakin lafiyayyan pool din dake gurin ruwan ciki na daukan ido yasaka kafa yana shigewa ciki ahankali harya gama shigewa gabaki daya ya rintse ido sanyin ruwan na ratsasa tsananin zafin jikinsa da jininsa ka neman fara karbuwa su daidaita.
****Ammi da Sultan kusan babu wanda ya iya cewa komai a yanayin da suke ciki har ya fice sallan ishai bai iya cewa komaiba bayan ce mata da yayi kada ta damu NUAB din zai sauko daidai babu yanda zaiyi bayan ya gama bacin rai da fushi kuma dole ya bisu hakama daga yau aurensu dasu sun samu cikakkiyar yanci da duniya zata san da sun zama maaurata kuma masu tsananin son juna duk wanda zai mutu ma ya dade bai kwanta ya mutu ba.
Yana ficewa itama barin bangaren tayi ta fito Maa sakinah data kasa tsayawa sbd tension din yayi yawa na abinda yake faruwa a ciki ya sakata komawa tabar bayi biyu suna jiran fitowan tata palo ta zauna tinda ta dawo tayi shiru cikin tsananin damuwan NUAB da itama takeson ya hakura ya aje komai yabi mahaifinsa wanda a yanxu duniya tafara sanin sirrinsa dake boye a ransa cewan babu wanda yakeso fiyeda ransa a cikin yayansa da duniyarsa kaman NUAB din.
Maa tenya ma datasan suna can din hankalinta bai kwanta ba saida sakinah ta dawo kallo daya tayi mata ta fahimci komai ya dauki zafi dan haka itama zaunawa tayi palon tana dan kallan tv sama sama.
Ammi na shigowa yanayinta kadai suka kalla jikinsu yayi sanyi sbd idanuwanta da sukai jajir zuciyarta cikeda daci.
Kallansu tayi tana sauke numfashi me zafi ta qaraso ta zauna tana dafe kanta a hankali tareda sake sauke numfashi ta dago tace
'NUAB ya kasa fahimtar abinda nakeson ya gane,ya kasa fahimtar abinda mahaifinsa yake son ya gane
Bansan tayaya zan fahimtar dashi batareda ya dauka ina zabar bangare bane,
A tsakaninsa da sultan ba maganar na zaba bane maganar ya fahimta ya yadda a yanzu aure mukeyi ba zaman baiwa da ubangidanta ba,
Ayau ya saka na fada masa abinda bansan ya akai bakina ya furta ba.'
Shiru sukai suna sauraranta damuwan sakinah na bayyana ta bude baki tace
'Kada ku ga laifinsa duka sbd duk abinda yakeji yake ciki an dasa masa shine tin yana yaronsa dan hakane ab8j ya tsaya a ransa hakama auren da kukai kun boye masa musamman ke dayake ganin komai yana yinsa ne sbd farin cikinki da baki kariya,
A qalla kafin auren ya kamata ku zauna dashi kuyi sharawa tinda shine waliyin dakike dashi amma tinda duka baayi hakan ba yanzu daukan zafi duka ba shine mafita ba hakuri zaayi a basa lokaci ya fuskanci komai da kansa.'
Shiru sukai dukansu tenya ta amsa zancen da itama fara jero tarihin irin yanda yayi rayuwa tin tashinsa a cikin ganin shi din da uwarsa ba kowa bane face abin takawa a wulaqanta a banza a masarautar karkashin mulkin mahaifinsa wanda shine ya fito ya nunawa duniya din su ba kow bane face mistress dinsa daya gama amfanuwa da ita da 'danta da kuma yanda aka rabasa da uwa da qasarsa aka kaisa qasar da baida kowa baida komai aka jefar dashi tinda qananun shekarun har girmansa ba wanda ya taba nemansa tayaya ake tunanin zuciyarsa zata sake wannan zafin duka a lokaci daya?dole sai ahankali insha Allah zai sake komai.
Hawaye sosai Ammi take gangarowa da jin irin yanda tenya ke jero quncin da suka rayu a cikinsa a cikin masarautar wanda NUAB ya taso a cikinsa ya kangarar masa da zuciya,
Komai dawo mata yayi ta rintse idanuwanta tana jin zafin abinda tayiwa NUAB din sosai kirjinta na nauyi.
Maa sakinah ma nauyin kirjinta yayi ta kasa cewa komai idanuwanta jajir kaman yanda na tenya din sukai sbd sune kadai sukasan radadi da zafin quncin da suka rayu a wancan lokacin a cikin masarautar data zamar musu tamkar maqabarta sbd qunci da baqin ciki tareda kadaici da damuwa.
Bahar datake tsaye duk abinda suke fada da faruwa a kunnenta nauyi kirjinta yayi idanuwanta suka ciko da hawaye tana kasa motsawa musamman ganin hawayen Ammin da kuma yanda ake fadar rayuwar da sukai wadda itace ta busar ta kangarar da zuciyar NUAB wanda ya taso ba soyayya da kulawan kowa ya rayu shi kadai sai soyayyar uwarsa da bata hayyacinta bata san ta kaunacesa ba a lokacin.
Kasa tsayuwa tayi jikinta na tsananin mutuwa da wani irin sanyi zata bar gurin Ammi tafara fadar abinda ta gaya masa ayau din wanda take jin nadamar fada masa hakan duk da tayi hakan ne sbd sakasa ajiye komai ya shirya d mahaifinsa.
Shiru suka sake ba wanda ya iya cewa komai sbd bama me daman tinkarar NUAB din yanzu dole saiya nemesu da kansa zasu iya samun damar magana dashi su dan taushesa.
Bahar data sake yin sanyi dakinta ta koma ta zauna a kan sofa tana kasa motsawa zuciyarta cikeda tinani.
Leylah dake kwance shiru itama tana fama da kanta zuba mata ido ganin yanayinta kafin ta rufe idanuwanta bacci ya dauketa.
Ita kuwa kasa motsawa tayi daga inda take din zaune har tsawon lokaci abubuwa da yawa na yawo cikin kanta cikeda damuwa da mutuwan jiki sbd bayan damuwan da Ammi ke ciki akansa harda fushi da bacin rai me girma tana ciki kan NUAB din wanda shima a daidai wannan lokacin tasan yana cikin matsanancin halin da baya buqatan kowa amma kuma tasan dole wani yana buqatan kasancewa dashi.
Sallar ishai da akai tin dazu ta tashi jiki a mace tayi tana idarwa tai shirin bacci har lokacin jikinta a matiqar sanyaye tana jin rashin nutsuwa.
Zaunawa tayi bakin gadonta tareda dago idanuwanta ta kalli agogon gefen gadonta taga karfe goma har tayi.
Numfashi ta sauke a sanyaye a natse kafin ta miqe tana rasa nutsuwanta kwata kwata ta dauki hijabi har qasa ta saka tana daukan wayarta ta fice daga dakin.
Ko data fito palo babu kowa koina yayi tsit alaman kowa ya shige sbd yanayin da ake ciki na damuwa.
Kofar ficewa take nufa daidai zata saka hannu ta bude kofar aka kirata a natse
Tsayawa tayi cak cikin faduwan gaba me karfi daya sake sanyaya jikinta.
Juyowa tayi daidai Maa sakinah na isowa gabanta dauke da tray me kyau dayake dauke da white and gold tea set masu daukan ido sabbi dal na amfanin LEUL din ta miqa mata sbd daman dakinta zata kai takai masa sai gata ta gani tasan kuma can din zata.
Bata ce mata komaiba miqa mata kawai tayi tace takai masa.
Bayi biyu ne mata naimah da salmah tace su rakata su dauki tray din wanda aka saka sukutum a cikin wata basket me girma da fadi.
#MAMUH
09033181070
: HAYATEEM
Mamuhgee
154
Itama Bahar din bata iya cewa komaiba kuma bata iya dagowa ta kalli Maa dinba sbd kunya da macewan jiki dan haka juyawa tayi a natse ta wuce su Naimah din na bayanta da zazzafan hadin tea din dazai warware kan NUAB din cikin sanyi insha Allah.
A sanyaye take nufar bangaren cikin nutsuwa da tinani kala kala bayinta na biye da ita kansu a qasa har suka sako kai a hanyar bangaren wanda tin daga nesa securities suka hangota hadda aleey dake cikinsu a daren sbd ya kasa shigewa miqewa sukai dukkaninsu aleey ne da kansa ya bude mata kofar yana tsananin jin dadi da farin cikin ganinta tareda jin wata nutsuwa na shigarsa sbd yana tsananin son sanin halinda NUAB yake ciki amma ba ikon shiga dan haka ya kasa barin waje yana cikin securities din dan bazai iya rintsawa ba koya shige.
Barka da zuwa sukai mata a natse dukansu batareda ta iya amsawa ba itama aleey kadai ta iya magana dashi a qataice tana wuce yana biye da ita har kofar shiga ciki ya bude mata ta shige bayin na biye da ita.
A palon farko suka dakata suna ajiye kayan dake hannunsu a table a jere suka juya suka bar palon da bangaren gabaki daya suna komawa inda suka fito.
Suna ficewa aka rufe koina na bangaren sai a lokacin Aleey ya sauke ajiyan zuciya me dan sanyi yana nufar lafiyayyan palonsa ya shige ya nufi bedroom kai tsaye ya shige yana nufar bathroom dan fara wanka tukuna ya huta.
Acan ciki itama ajiyan zuciya me sanyi da sauti ta sake a tsakiyar palon tareda kallan hanyar palonsa na kurya tana jin zuciyarta da jikinta na sake sanyi,
Sake sakin nunfashi tayi me nutsuwa kafin ta durqusa ta dauki tray din din da aka jere mata din ta nufi hanyar dakin.
Tana isa ba maganar knocking sbd tasan baya cikin yanayin da zaa damesa da buga kofa koma yanayin da zai iya cewa a shigo koma yazo ya bude dan haka kai tsaye bude kofar palon tayi ta shiga a natse tana rufewa koina tsit da rashin haske sosai baya palon dan haka kofar bedroom ta kalla tareda daga kafarta ta nufi can din.
Bude dakin tayi a natse ta sako kai tana shigo idanuwanta akan sofa sbd san ganinsa amma baya gurin.
Qarasa shigowa tayi tana rufe dakin da bayanta a natse kafin ta tako zuwa tsakiyar dakin da shima akwai haske amma bame sosai ba.
Duba dakin tafara yi da idanuwanta koina amma bata gansa ba dan haka ta ajiye kayan hannunta akan table tana zubawa hanyar bathroom idanuwanta da sukai laushi amma bataji motsin komaiba dazai nuna alaman yana can.
Juyawa tayi gurin curtains din hanyar pool dinsa data gani a bude tana kalla kafin ta fara takawa ahankali zuwa gurin.
Ba haske sosai a gurin shima hasken bakin pool dinne kadai daya zagayesa kadan kadai a gurin,
Akansa idanuwanta suka sauka yana cikin ruwan ya baya kofar baya gashinsa me tsayi a asake bayansa kadai take iya gani dan haka ta dakata daga inda take tsaye tareda sauke boyayyar numfashi me dumi jiki a mace tana kallansa batareda ta iya matsawa ba ko juyawa ba.
Tsawon sakanni ta dauka a hakan kafin ta daga kafafunta tafara takawa a natse tana nufarsa,
Bayansa ta iso a hankali cikin nutsuwa ta durkusa tana sauke gwiwowinta a qasa tana dan zaunawa kadan akan kafafunta gap da bayansa dan har gwiwanta na dan taba bayansa daga sama da iya shi kadai ne a waje sauran jikin yana ruwa zaune.
Bai motsaba kuma har lokacin idanuwansa basu bude ba a rufe suke cikin tsananin halin da zuciyarsa take ciki tana dauke duk wata rahamar gangar jikinsa.
Idanuwanta ta saukar akan kunnensa ta bayan nasa taga yanda yayi wani irin jajir wanda yake nuni da halinda yake ciki dan haka ta rasa abin fara fada sai kawai ta rankwafo sosai cikin sanyi da nutsuwa takai miqa hannunta a natse ta dora akan fatar kunnensa ta shafa cikeda wata irin kaunar me karfin gaske da baki bazai iya fada ba da kulawa tareda fidda wata irin numfashi me zafi daya feso damuwan da tsananin sanyin da jininta yake ciki wanda ya sauka ahankali kan kunnensa da gefen fuskansa ya sake rintse idanuwansa ahankali batareda ya budesu ba yana jin wani irin zafi na sake taso masa da ratsa zuciyarsa sbd yanda numfashinta ya bayyanarda damuwar datake ciki.
Wani sanyi jikinta ya sake yi batareda da dauke hannunta daga kunnensa ba ta saka dayan hannunta suka akan gefen fuskansa ta shafa a natse tana sako kanta ahankali gefen fuskansa ta bayansa zuwa gabansa sbd batasan wace kalman zata fara da itaba a yanzu dole shi takeson ya fara magana tukuna tasan me zata iya fada masa sbd rage masa damuwan dake zuciya da ruhinsa.
Yanda ta sako kanta gefen fuskansa ta sauke idanuwanta masu laushi akansa tana kalla cikeda kulawa da jin kaman ta zare masa duk abinda yake ji numfashinta na sauka ahankali ahankali kan gefen fuskansa duminsa yana ratsasa yana dawo da tinaninsa akan abinda zuciyarsa take ciki na damuwan da iyayensa dashi suke ciki a daren.
Bude bakinta tayi a cikin tsananin sanyi da nutsuwa da kulawa can qasan maqoshi gap da kunnensa tace
'Please...' Shiru tayi tareda jan wani numfashi mara karfi da sanyi tana rasa abin fadar kafin ta sake bude baki ta kuma furta
'Kada kayi damuwa dan Allah,
I cant se...
Bata qarasa ba sbd yanda muryanta ke rawa ya bude idanuwansa da suke jajir a wani slow yana saukesu a fuskarta.
Kallanta yakeyi batareda kyaftawa ba ko kadan itama shi take kalla da wani gaze dayake sake juyawa kowace irin tinanin dake kansa..
Amminsa ce mace daya da a duk duniya yake iya komai akanta,.ayau ta masa baraza akan matsayinta datake dashi a rayuwarsa akan abinda zai iya ajewa idan tace kawai ya aje batareda ta saka masa wannan zazzafar kalmar ba,
Sai kuma Ayanah bahar wadda itama akanta zai jurewa da fuskanta kowace irin yanayi....
Cikin idanuwanta ya kalla yana sauke numfashi me zafin daya daki fuskanta a hankali ta lumshe ido ta bude akansa kafin ya motsa a hankali tareda dago hannunsa daya ya miqa mata yana rufe idanuwansa tareda hadiye wani nauyi dayake tsaye a maqogoransa ya budesu akanta.
Zare hijabin dayake jikinta tayi ahankali tana ajiye wa gefe cikin nutsuwa kafin ta miqa masa hannunta ta kama nasa tana takowa ahankali zuwa cikin ruwan yana riqe da hannunta batareda ya sake ba.
Ratsata sanyin ruwan sukai ta sauke ajiyan zuciya me dan karfi tana qanqame hannunsa dake riqe da nata tana rintse ido sanyin na ratsata amma kuma