Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   23 / 100

66K to 69K   out of 299.8K words

take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare
Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah
Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma,
Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take
Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k
Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k.
Zuzeam ventures
08144015291

*******
Doctors din guda biyu na masarautar tin tsawon shekaru masu dan dama da basa karban kowace haihuwa sai ta asalin Matar sarki qananun su ne suke karban haihuwan imebētis amma Ayau sune sultan da kansa ya bada sakon umarnin kiransu amsar haihuwan wishmansa Shiyasa Haile bata samu damar samunsu a masu karban haihuwant wannan Karan koda kuwa Ana iya samun damar dan aike ya fita a lokacin naqudar to ba samunsu zatai ba sbd suna Akan wishmar BOYEM,

Ajiyan zuciya suka ringa saukewa suna kallan babyn Wanda kukansa mai karfin gaske ya cike dakin da bangaren gabaki dayansa harma daga wajen GHAZ chambers Ana jiyo kukan nasa.

Ita kanta tenya ajiyar zuciyar ta ringa jerowa ba kakkautawa kafin ta bude Baki da karfi tana cewa

‘MashaAllahhh,Barakallahu laka fi’l-mawhubi lak,wa shakarta’l wahib,wa balagha ashuddah,wa riziqta birrah.
ALHAMDULLILLAH YA ALLAH’ ta qarasa fada da karfi tana karban lallausan showel fari tas hannuwanta na rawa ta dunqulesa tana dawo da kallanta Akan Ayanah cikin rawar murya tace

‘Allah ya qara miki Nisan kwana da lafiya tareda albarka me dorewa UWAR BOYEM GABAKI DAYANTA TA YANZU,
UWA GA ZAKIN BOYEM,
UWAR MAZAJEN BOYEM,
UWAR ME BOYEM NA GABA.

Sakinah rawa jikinta ya dauka da karfin gaske tana juyowa da karfi ta tsira wa babyn hannun tenya din ido bata ko kyaftawa.

Ayanah ma duk da bata hayyacinta bata dawo daidaiba bude jajayen idanunwata tayi zufanta na qaruwa ta zubawa hannun tenya ido tana kasa gasgata da gaske namijin da qasar BOYEM da qasoshi da dama suke jira shi ta haifa,

Hawaye ne suke kokarin ciko idanuwanta na fargaba tsoro da tsananin tausayi da son danta da rikicin qasar gabaki dayanta yake jiransa.

A daidai wannan lokacin bangaren HAILE shima wani Tiriri ya dauka na samuwar cikar Buri dan kuwa itama namijin ne ta haifa Wanda ya sakata kokarin tashi da kanta dan isar da sakon haihuwar ‘da namijin ga sultan tin kafin Ayanaah ta haihu sbd farin cikin samun cikar burin shekaru ya mantar dashi Ayanah da kowa menene zata haifa.

Hanata Miqewa likita ke kokarin yi tareda yarta harma da fetto sbd jinin da babu sosai a jikinta kuzari tareda azabtuwar datai sosai tayi pale sosai suka dage cikin tsananin kulawa da kauna dan komai ze iya faruwa da ita idan ta tashi tsaye amma Sam taqi yadda da hakan rungume take qam da babyn tana kokarin Miqewa zuciyarta a rufe bata Jin ko zata rasa ranta zata iya jiran Ayanah ta haihu batareda sultan yafara sanin ta haifa Zakin qasar BOYEM ba,

Miqewa tayi suka miqe dukansu tareda riqeta zuciyoyinsu da hankalinsu duka a tashe da mugun tsoro da tashin hankalin hukuncin laifin da suke kokarin aikatawa na Binta su fita,

Wani jinin ne ya kuma gangarowa daga qafafunta Wanda ya saka hankalinsu sake tashi dake sauri bayi biyu sukai saurin durqusawa suna goge mata jiki da towel me dumi da suka matse daga ruwan Zafin da aka goge mata jiki gabaki daya.

Sake shiga tashin hankali su fetto da likitar sukai harma da ‘yarta sbd hatta ita Haile din hukunci zai iya hawa kanta dan babban tsatsauran dalilin daya saka wannan tsaurin yake a masarautar lokacin haihuwan kwace mace shine hana cutatar da kowace jaririn da zaa haifa ko uwarsa kokuma sace jarirai musayarsu dan haka baa yanzu wannan dokar take ba tin asalin asalin kafa masarautar yake.

Jiri ne sosai da rashin isashen jini ke Neman zubar da ita amma a haka suka riqeta dan suma bazasu taba son imebetin ta haihu batareda sultan yasan an samu magajin BOYEM ba,

Taku daya biyu sukai suna daga qafafunsu su hudun a tare zasu fito dakin wata kakkarfar sautin qarar da baa taba kada wa ba tin tsawon shekarun da sultan YASAR ya hau mulki bace ta ratsa kunnuwansu cikin sanyi da rikitaccen yanayin daya saka dukkaninsu Sakinta cikin mugun firgita da ficewa hayyacin dan kuwa sautine dayake fadawa BOYEM da duniya gabaki daya MAGAJI kuma ZAKIN BOYEM ya sauka a duniya tsohuwar imebeti sabuwar wishmah AYANAH GHAZ ta haifosa.

Shigar sautin kunnuwan Sultan YASAR da gabaki daya manyan masarautar boyem a lokaci daya suka zube qasa suna yiwa Allah sujjada batareda ma sun sani ba,

Haile kuwa Numfashi daya ta fitar bugun zuciyarta ya tsaya cak sakamakon sautin sakon daya ratsa kunnuwanta ya Harba cikin kwakwalwanta ta zube a gurin jaririn hannunta yana subucewa daga hannunta zuwa qasa,

Cikin wata gaggawa da tashin hankalin dayake Ninkuwa Akan mugun shock din dasuke ciki fetto ta tare babyn koina na jikinta na rawa da kakkarwa,

‘Yarta Aslam ce tayi saurin tarota jikinta itama jikin nata yana rawa sosai da firgici tareda tsananin tsoro sukai qasa har ita har mahaifiyar tata sbd batada karfin da zata iya riqeta tinda jikinta a sake yake kaman babu rai a jikinta,

Dr Kadee ce tayi saurin bin Aslam din qasa tana tayata riqe Hailen itama jikinta rawa yakeyi da firgicin yanda duk wahala da azabar da suka sha ta tashi a iska labarin haihuwan Ayanaah ghaz ya fara shiga kunnuwan sultan YASAR da qasar BOYEM harma da duniya gabaki daya.

Fetto babyn ta rungume jikinta tareda budesa sa sauri taba duba idan yana raye babu abinda ya samesa daga faduwar taga lafiyarsa kalau sedai tinda aka haifesa baya wani kuka saida ya fadin ya fasa kuka sosai Wanda ya sakasu sauke ajiyan zuciya suna tattalar HAILE din dan maidata shimfida a bata taimakon gaggawa.

***A daidai wannan lokacin kuma sautin qarar ya ratsa kunnuwan Zuhrah dake Zaune daqyar sbd azaba da rashin lafiyar da kowace gabar jikinta keyi a cikin wani irin kurkuku mara Kyan gani,

Tinda aka sanar da Masarautar kaf cewa imebeti AYANAH GHAZ na naquda ta tashi Zaunen idanuwanta dake ciwo basa gani sosai ta bude su tareda daga Kai sama ta qurawa sama ido tafara jerowa Ayanah da abinda zata haifa addua jikinta na rawa tana fadawa Allah adduarta Akan yar uwarta
Bata Dena addua da fadawa Allah ya tsayu Akan rayuwar babyn ayanah dinta ba har saida sautin ya ratsa kunnuwanta Wanda ya sakata rufe idanuwanta ahankali tana silalewa qasa kwance tareda fashewa da Wani irin kuka mai ratsa zuciya tana gode wa Allah da bai karbi ran ayanarta gurin haihuwa hakama wata irin tsananin kewarta da kaunar son ganinta a lokacin ta saka sabbin hawaye gangaro mat a tana Jin tsananin so da ganin abinda Ayanah ta haifa musu ta rungumesa a jikinta taji duminsa tareda sakawa rayuwarsa albarka da fada masa sun yafe masa ita da ‘yan uwanta da basa raye sbd kaddarar haihuwansa a jinin BOYEM ce ta lalata tasu rayuwar da babu gyara a cikinta har abada.

Rufe idanunwata tayi hawayen data manta rabon datai yi su sbd kuka ma kansa ya gujeta sai Ayau din datake Jin kewa da tsananin son Ayanah da ‘danta suna ratsata.

****A kuma wannan lokacin ne sultan YASAR ya dago daga sujjadarsa ya daga hannu sama yayiwa Allah godia yana jerowa dan nasa addua me tsananin karfi,

Danyen zinari aka fara fitowa dashi a tray mai shegen kyau aka fara kyautarsa a matsayin tukuici hakama duka manyan dake cikin farin ciki mai tsanani da annashuwa suka fara gabatar da tukuici ga AYANAH GHAZ da kyautar data ringa girgiza mutane da tabbatarda Ayau burin qasar BOYEM ya cika na shekaru,

Ko da tenya ta fito daga babban kofar fitowa bangaren Wishmah gabaki daya wasu irin securities ne da bayin da zasu rakata har zuwa fada Sbd Mai BOYEM dayake hannunta.

Gabaki daya Wani irin Juyawa tenya taji kanta na yi sbd tarin bayi da securities da suka cika hanyar dan kawai rakiyar Magajin BOYEM ga mahaifinsa.

Kafafunta sanyi sukeyi mata a duk lokacinda tayi Taku daya na tafiya zuwa fadar mai girma sultan YASAR dauke da jaririn dayafi kowane ‘da daraja a qasar BOYEM yana dunqule cikin farin lallausan bargon daya babu hannun Wanda ya shiga duniya Bayan nata saiya shiga hannun mahaifinsa kafin ma ya shiga hannun mahaifiyar data haifesa,

Kai tsaye hanyar fada suka isa babyn na rungume a jikin Tenya data ke Jin sabuwar duniya ce yake kafuwa a BOYEM daga lokacin da ‘dan nan ya gado duniya.

Isowarsu bakin kofar fadar da Wani irin tsit akai tareda wangale mata kofa Sauran securities da bayin suka tsaya daga kofa ta sako kafarta ta dama ta shigo tana Takawa cikin nutsuwa tana nufar karagar mulkin BOYEM da sultan yake Kai idanuwansa masu tsananin kyau da kwarjini suna kan hannuwanta biyu dake rungume da hasken dayake tsaya zuciya da idaniyarsa,

Dukkanin Wanda yake cikin makekiyar fadar da Taku ne me yawa kafin Ka isa karagar daga bakin kofa kowa idanuwansa Akan hannun tenya yake suna fidda silallan zinari a gabansu suna ajiye wa qasa inda duk tenya ta taka ta wuce matsayin tukuici gareta ita kanta Wanda hakan ke saka kafafun tenya rawa da farin cikin datake Jin kaman zata some tin daga lokacin da magaji ya shiga hannunta.

Ko data isa gaban sultan YASAR a hankali ta zube Akan gwowowinta tareda daga masa magajin BOYEM tana miqa masa kanta a qasa tana zuba masa Wani irin Kirarin daya saka fadar dama masarautar yin tsit sautin muryanta me karfi ce kawai taje tashi tana amsa Amon kirarin datake wa sultan YASAR da magajinsa.

Wasu manyan sarkokin zinari ne aka fito dasu Ana tsayawa gefenta dasu
Sultan da hannuwansa ke rawa miqawa yayi ya dauki babyn dake kan hannunta yana ambatar sunan Allah da sautin daya saka kowa maimaita sunan Allah din,

Ita kuwa tenya sultan na dauke babyn daga hannunta aka fara dora mata sarkokin zinarin tukuicinta tayi qasa da Kai tana zubda hawayen farin cikin samun cikar Buri.

Addua da huduba sultan ya daga babyn yayi masa tareda rungumesa jikinsa tsawon mintina uku kafin ya dago idanuwansa da kwarjinsu ya sake cike niimar gurin ya bude Baki da sautin daya saka tsigar jikin duk Wanda yake gurin tashi ya ambacesa da sunan daya saka masa Wanda duniya zata kirasa dashi,
‘LEUL NU’AB ALMAZZ YASAR BOYEM’

#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali*_HAYATEEM_*
Mamuhgee

39
*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Bononza bononza
Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka
Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah
-Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani,
-Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba,
wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online
Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare
Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah
Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma,
Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take
Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k
Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k.
Zuzeam ventures
08144015291

*******
A take gabaki daya fadar kowa ya miqe tsaye suna sakawa LEUL NUAB albarka cikeda wata irin girmamawa da shauqi
Su kuwa bayi gabaki daya cikin fadar dana kofa da waje zubewa sukai qasa kawunansu a qasa suna masa adduar securities ma qame wa sukai suna sare maza da addua.

Tenya da gashin jikinta ke tashi yana qarawa bude Baki tayi ta ringa jero sabbin kirari da addua kafin sultan ya maida mata Almazz din hannunta ta amsa Bayan ta miqa tukuicinta ga bayinta kafin ta miqe tsaye
A lokacin ne aka fara fitowa da wasu sabbi trays masu dauke da sarkokin da suka sakata rungume LEUL da kyau sbd rawan da hannunta yakeyi,

Tukuicine ga Wishmah AYANAH GHAZ na hasken idanuwan da ruhin data basa Wanda zuciyarsa bazata taba mantawaba da wannan feeling din da itace tafara basa shi dan kuwa koda zai samu wani haihuwan namijin a gaba to tabbas wannan feeling din na farko na daban ne daya bude zuciyarsa ga abubuwa da dama ya kuma kulle wasu kofofin dake zuciyar tasa da dama.

Bayin tenya dana wishmah dinne suka fara shigowa a hankali suna jeruwa suna daukan tukuicin Ayanah Wanda ya ringa fitowa daya bayan daya daga masu boyem dake cike a fadar harma da wainda ke isowa a lokacin da securities dinsu dan samun raya farin cikin lamarin batareda bata lokaci ba,

Tukuicin MARAKI ne itama ya iso a lafiyayyan tray din silver mai kyau an rufesa da wani golden kyalle mai kyau da daukan ido itama set din sarkar kafa ce data Kai sai sarkar hannuwa biyu duk na gwal masu kyau marasa nauyi,

Karba akai Bayan ansanar daga inda kyautar ta fito take bayi suka zube suna miqa godia ga jakadiyarta data kawo sakon tareda bayi biyu.

Tarin kyautar isowan LEUL duniya harya fi na mahaifiyarsa da aka bata tukuicin haihuwar sa dan kuwa shi haka ake zuba silallan zinari a cikin kyautar da ake masa kaman baa san zafi da ciwon su ba tamkar abin banza,

Shiru babu dan sakon Haile na miqa taya Murnarta ga sultan bisa ga wannan gagarumin cikar burin da babu kamarsa da Allah ya cika masa,

Tenya data matsu a koma da LEUL gurin mahaifiyarsa ta sakasa a jikinta itama taji duminsa zuciya da ruhinta su samu sassauci shima ya samu shiga jikin mahaifiyar data haifesa duminta ya ratsashi Miqewa tayi tana sake godia suka juya zasu fice tareda tarin kyautitikan da zasu sauya rayuwarsu da duk ahalin da zaa haifo a zuriar su,

Taku biyu tayi aka qwalla sanarwar shigowan me isar da sako daga bangaren Haile dan haka take tenya ta daya cak sbd dole ne tsayawan kowa idan zaa isar da sakon masu boyem,

Fetto ce ta sako Kai a cikin fadar kafarta ta dama itama ta fara sako wa a cikin fadar koina nata rawa yakeyi amma ta kanne zuciyarta babu abinda take tsananin marari Bayan isa gaban sultan ta isar da labarin haihuwan magajin sa daga Haile datake matarsa ba imebeti ba dan kuwa a tsatsaurar dokar boyem matiqar akwai ‘da namiji daga Mata to ‘dan imebeti bazai taba zama magaji ba dan haka da confidence mai girma ta tinkaro tsakiyar fadar dauke da farin showel itama a hannunta babyn dake ciki na kwance A ciki yana bacci hankali kwance.

Tenya kafe idanuwanta tayi a hannun fetto din zuciyarta na dan bugawa da tinani masu tsauri da girma Kala kala sbd idan idanunwata suna gani daidai baby ne a hannun fetto din Wanda da alama shima baa jima da haihuwansa ba,

Gabaki daya wainda ke fadar tsaida idanuwansu Akan hannun fetto sukai cikeda mamaki da shiga tinanin ko yan biyu Ayanah ta haifa Sai yanzu Dayan ya fito to amma ganin jakadiyar HAILE kuma sako daga bangaren Haile akace ya saka kowa aje tinanin yan biyu aka haifa.

Fetto na isowa tsakiyar fadar me girman gaske zubewa qasa tayi ahankali kanta na qasa ta daga babyn cikeda kulawa da girmamawa me girma tafara zubo masa kirari kafin daga karshe ta sanar dashi queen HAILE ta sauka awa daya da mintina arbain da tara da suka wuce Wanda sakamakon cikin datake Reno ne ya sakata karban hutun zuwa tiraka kuma tayi hakan ne sbd kebe kanta ta samu jinya da Renan ciki mai nutsuwa kuma a cikin yardar Allah ta haifo asalin magajin boyem.

Da tsananin mamakin daya dakatar da komai kowa ke kallan hannun fetto din shock na kama kowa,

Tenya ma wani irin dum taji kunnuwanta sunyi ta rungume LEUL da karfi kirjinta tana kasa dauke idanuwanta Akan hannuwan fetto zuciyarta na nauyi da tsananin mamaki da tashin hankalin maganar fetto din kafin ta maida idanunwata Akan sultan YASAR da shima shiru Yayi idanunwansa Akan fetto tsawon seconds kafin ya maida idanuwansa Akan babyn hannun nata ya kallesa yana mamaki mai tsananin daya dan bayyana.

Tsit koina da kowa yayi Ana rasa abin fada sbd magana dai a Kai tsaye take babu wani kwana kwana kowa ya fahimci komai da fetto ta fada babu abinda kowa zaice bai ji daidai ba kokuma Neman karin bayani akai Kai tsaye itama HAILE magaji ta haifarwa Masarauta.

Sultan da yayi shiru yana kallan babyn kawai suke jiran bayani daga garesa Wanda shima kai tsaye yaji komai daidai ba buqatan kowace tambaya Akan qarin bayanin komai,

Mintina aka share kafin sultan ya sauke Numfashi me sanyi tareda dauke ajiyan zuciya mata sauti zuciyarsa na ratsuwa da wani sabon farin cikin samun wani hasken idanuyar da baima San dashi ba dan haka hannuwansa ya miqa a natse cikeda kulawa da soyayya mai karfi ta uba ga ‘dansa ya amshesa tareda rungumesa a jikinsa na mintina shima yana masa addua kafin yayi nasa huduba ya daga sa sama ya ambacesa da,

‘LI’ULI ASIM YASAR ALMAZZ BOYEM’ (prince Asim yasar almazz boyem)

Take kowa ya maimaita sunan suna saka masa albarka tareda addua duk da baaji shauqin na ratsa jini da kwakwalwaba kaman farkon amma shima sunyi Murna sosai da kasancewansa sabon prince din boyem hakama yau rana ce mafi girma da tarihi tinda aka haifar musu jaruman babys biyu a daya rana.

Kyauta da tukuici aka fara fiddawa Ana bawa fetto itama sedai kasancewan baa San da haihuwan ba bata samu kyauta irin wadda tenya ta samu ba sultan kuwa kyautarsa da tukuicin sa daidai iri daya yayi da wadda yayiwa NU’AB,

Cikin karfin Hali da dake wani zuciya fetto ta karbi ASIM tareda dagasa tayi masa kikarin daya saka kowa yin tsit dan kuwa Kai tsaye da asalin magajin sarki ta kirasa bayan sultan ya riga ya Ambaci NUAB da magajin BOYEM.

Dagowa sultan yayi da fararen idanuwansa da sukai wani haske da kwarjini sbd yanayin dayake ciki a yau din zai kalli fetto

23 / 100