Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   83 / 100

246K to 249K   out of 299.8K words

ta nemesu shima ba dakinsu taje ba jinsu shiru ya saka ta aika naimah dubowa saigashi naiman tace basa nan,

Maa sakinah data san babu wanda ta kwana a bangaren duka su biyun sbd taje da daddare dubosu ba kowa kuma har wani dare tana dakin tana gadinsu amma ba wadda ta dawo dan haka shiru tayi batace komaiba har naiman ta dawo ta sanar da Ammin basa nan.

Shiru Ammin tayi amma batai tinanin komaiba tinda suna tare tasan NUAB bazai samu ganin Bahar din bama tinda suna bangaren Zuhrah.

Wayar zuhrah taso kira taji ko suna can din sai bataga wayarta ba sai kawai ta share ta kama wata hidimar.

Babu wanda ya sake fitowa dan haka basu hadu ba sai after 11.

Bahar ce ta fito da wayar Ammin a shirye cikin kayan shan iska marasa nauyi sosai riga da wando ta nufi dakin Ammin ta shige.

Wayarta ta kawo mata ta gaidata tana shigewa gefenta ta zauna tana amsa tambayan datake mata akan wayarta data ga sakon gaisuwan da zarah yar tenya datake aiko mata kullum.

Anan leylah ta sameta ta gaida Ammin itama tana ficewa dan wayarta da Mum dinta ke kira dan amsawa.

Bata fito dakin ba Maa ta shigo dakin dauke da tray din dayake dauke da madarar data dafa mata me karfin gaske ta ajiye kan table tana zaunawa akan kujera itama tana shiga firar da sukeyi cikeda kulawa sunayi akan wani hukuncin da Abaa dinta ya taba yankewa batareda ya iya mulki sosai ba a anjom suna dariya maganar na shigar Ayanah datake jinta har zuciyarta da farin ciki da dariyan jin yanda Abaas yayi mulkin anjom batareda taimakon kowannensu ba shi kadai.

Sakinah ma dariya takeyi suna maimaita lokacinda yake tamkar mace bayason ace shine zaiyi mulkin Anjom yafison Ayanah tayi ya bita.

Bawa bahar din mug cup din dayake fidda hayaqin madarar Maa tayi ta karba suna cigaba da firar su cikin nishadi da kewan Abaas wanda a yanzu koyaushe adduarsu bata yankewa akansa da sauran iyayensu da Nurat.

Fara sha tayi a hankali tana dan bata fuska kadan sbd karfin madarar dan haka bakinta ya mutu ta rage magana tana sha a hankali tana saurarensu tana murmushi da yar dariya jin irin kuruciyar da mahaifinta yayi wanda firan take mata dadi sosai sbd batada labarin da ako yaushe yake mata dadi da bata gajiya da sauraro irin firar mahaifinta.

Nishadi sukeyi sosai suna firar tana sauraronsu tana murmushi tana shan abinda yake hannunta a natse tana lafe gefen Ammi.

Qamshinsa ne ya fara ratso su dan haka maa dake dariya sosai ta dago ta kalli kofar daidai nan ya sako kai da sallamarsa me nutsuwa da kamewa tareda wani irin iko.

Ammin itama kofar ta kalla har lokacin fuskanta dauke da dariyarta me kyau datake tino mata farin cikinta na baya data rasa a tareda rayuwa da iyaye da yan uwanta.

Ganin nishadin dasuke ciki ne ya sakasa qarasowa fuskansa daukeda wata natsatsiyar annushuwa da kwanciyan hankalin da shima yake tattare dashi wanda kasancewan 'yar Ammi a boyem din yake basa.

Zaunawa yayi a gefen Ammin a natse cikin kwanciyan hankali ya kalleta ya gaidata cikin kulawa da kauna kafin ya maida kallansa kan Maa itama ya gaidata.

Amsawa sukai dukkaninsu cikin kulawa da kauna suna kallansa da sauyin dayake tattare dashi na wata sabuwar nutsuwa da kwanciyan hankalin dasuke iya hanga a tattare dashi amma ba wanda zai iya tambaya.

Kan Bahar ya dawo da kallansa a natse ya kalli cup din hannunta da abinda yake cikinsa tana sha ahankali batareda ta iya dagowa ta kallesa ba sbd batason ma Ammi taga ko kallansa tana yi.

Maa ce ta kalleta tace

'Yar Ammi bazaki gaida Sultan guda ba gashinan kinyi shiru?

Faduwa gabanta yayi ta dan dago ta kalli Maa din wadda ta kafeta da ido,
Kan Ammi ta maida kallanta taga Ammin ko kallanta bataiba dan haka ta juyo da idanuwanta a hankali akansa ta kallesa shi kuwa ya kafeta dasu kaman zai janyota jikinsa.

Bude bakinta tayi cikin nutsuwa da kokarin sakewa tana hana kowace fargabanta fita ta gaidasa.

Sai a lokacin ya dauke idanuwansa daga kanta sbd yanda komai nata ke shigarsa a daki daki,
Zai iya kasa riqe kansa ya kama hannunta sbd jin sautin muryanta da yanda ta gaidasa din tana kallansa da mayun idanuwanta dake warware duk wani lissafinsa.

Amsawa yayi kafin a sake cewa komai ta miqe a natse da cup dinta a hannunta tabi ta gefensa ta fice daga dakin tana bar masa wani qamshinta daya shiga hancinsa dakyau.

Wani numfashi ya hadiye yana kamewa dakyau batareda yabita da kallo ba harta fice tukuna ya dawo da nutsuwansa cikakkiya akan iyayen nasa suka fara magana.

Maa ce ta kallesa tana gyara zamanta da dukkanin nutsuwa tace

'LEUL kaje ka samu ganin mahaifinka kuwa?
Duka munsan kasan baya nan tsawon wannan lokacin yana can tareda mu a uk dan haka tinda ya dawo ya kamata duk matsayin da kake dashi kaman yanda kazo ka gaida mahaifiyarka kayi mata barka da dawowa shima kaje ka samesa kayi masa gaisuwa da barka da dawowan sbd duk koma menene kowa yakeji matsayinsa na uba,sarki,Mahaifi kuma mijin mahaifiya ya wuce komai'

Shiru Ammi tayi sbd yanda zuciyarta ke harbawa da yanda komai zai bayyana NUAB ya fahimta,

Shi kuwa shiru yayi yana sauraran Maa din,
Tinda ya dawo sun hadu so daya dayaje ya samesa da kansa suka gaisa amma bayan nan basu sake haduwa ba sbd bayajin akwai abinda zasu iya zaunawa su fuskanci juna su tattauna a tsakaninsu.

Numfashi ya sauke me sanyi da nutsuwa kafin ya dago ya zubawa Ammi idanuwansa sbd duka wannan maganganun yasan abinda takeso aka isar mata a gurinsa,
Itace take son ya samu Sultan su daidaita sbd zuciyarta na son hakan,
Zuciyarta bazata iya fifita son datake masa akan na sultan ba shiyasa take masa hakan har itace ayau take kasa masa magana sedai ta saka ai masa magana duka akan sultan.

Dawo da kallansa yayi akan Maa ya bude baki baki a natse yace

'Insha Allah Maa'

Yana fadar hakan sallama yayi musu ya miqe ya fice batareda ya cewa Ammin komaiba sbd koyaushe akan sultan sosa zuciyarsa takeyi tareda danne matsayinsa na 'danta dayake yaqi da jin zafin sultan akanta amma sai tana mantawa da hakan tana zabar sultan kuma tana boye masa tana daukansa da masa kallan wanda yake tsakiyarta da farin cikinta na son rayuwa da mutumin da 'yanci wannan ya kasa bata yana matsayin sultan wanda yake kam mulki sama da shekara talatin.

Yana fitowa Aleey kallo daya yayi masa yasan zuciyarsa ba dadi dan haka babu doguwar magana suka wuce Fada dake cike ana jiransa ayau akwai taro da zaman fadar.

Koda suka isa fadar tsit koina yayi sbd shigowansa da aka sanar.

Yana shigowa kowa kansa yayi qasa niimar gurin na gauraya a natse da qamshinsa da zuwa yanzu duk wanda yake shiga fada dashi yasan qamshinsa hakama zazzafan kwarjininsa ya gauraye gurin.

Koda ya isa kan karagar mulkin boyem din tini Aleey ya isa ya tsaye a gerenta daman keelah na tsaye daga bayanta cikin jikinsa babu kalar makamin da babu a soke boye.

Yana zaunawa daga waje securities masu karfi suka dakatar da kowace irin kaida kawo a hanyar fadar ba shiga ba fita saiya fito kuma kowa zai samu yancinsa.

Kusan wuni yayi a fadar bai samu kansa ba sai kusan yamma dan haka yana fitowa daga fada kai tsaye aika sakon zuwansa akai gurin sultan yasar wanda yayi mamakin jin zuwan nasa duk da Ayanah ta sanar masa a waya cewan Maa dinsa sakinah tayi masa magana amma kuma shima daman yana buqatar ganin nasa dan haka koma menene zuwan na NUAB din zai kawo yana shirye dashi dan kuwa lokaci yayi dazaisan uwarsa ta auru.

Shi kansa NUAB din ayau yana son fuskantar sultan ne a karo na karshe insha Allah akan mahaifiyarsa wadda a yanzu baida ikonta yana son yayi masa iyaka da ita sbd kaucewa abinda babu a addini hakama a karan karshe zai sanar masa da zai bar boyem da ita bazata taba dawowaba da zama.

Wannan tabbatacciyar magana ce da zai tabbatar masa sbd shine me cikakken ikon mahaifiyarsa ayanzu idanma sultan din ya manta zai tinatar dashi hakan a tsanake sbd yasan ya rasa damarsa har abada.

Saida yayi wanka ya huta bayan sallan magrib ya nufi bangaren mahaifinsa wanda yake zaune a natse shima yana jiransa da sadakin mahaifiyarsa daya ajemasa yana jiran ranar basa.

Koda Sultan me mulkin boyem LEUL NUAB ya iso bangaren sultan me murabus yasar kadir yana tsaye bakin kofa yana jiran isowansa cikin nutsuwa da Girmamawa.

Aleey ne da keelah a tareda shi sbd ziyarar bata buqatan hayaniyar tsaro tinda gurin mahaifinsa ne yazo.

Kadir ne yayi masa rakiya da iso har palon da sultan yake hutawan yana zaune yayi fresh dashi hutu da kwanciyan hankalin da duk yake nema a rayuwa yanzu ya samu duniya tasan ya mallaki Ayanah ghaz halak malak kadai ya rage wanda shi baya buqatan hakan idan 'danta kawai ya sani ma ya ishesa duk da idan har danta ya amince ya karbi aurensu to dole duniya zata sheda ta sani sbd tsaftata alaqar.

Dagowa yayi yana zaune kafarsa daya akan daya yana duba abu a waya fresh fruits a table din gabansa kallan Fuskan NUAB yayi wanda shima huta da kwanciyan hankali da wani azababben iko da izza ke bayyana tattare dashi na zafin mulki ta uba data uwa da kuma na empire din kansa daya kafa.

Aura ce ta cike gurin ta uba data 'da dake nuna zallan iko da izza dan haka ficewa kadir yayi a hankali a natse yabarsu su kadai.

A 1 seater din dake facin sultan yasar NUAB yake zaune ya dago cikin nutsuwa ya kalli mahaifinsa bai ji komaiba na damuwa ko wani yanayin a natse ya bude baki ya gaidasa yana kallan abubuwan da sultan din zaiji daga bakinsa.

A natse sultan ya amsa yana qarawa da masa kirarin sarauta a natse dan bude filin da abinda zai gabatar masa.

NUAB dayake sauraransa numfashi ya sauke yana dagowa ya kallesa cikin isar iko da izza zai fara magana sultan ya miqa hannunsa gefensa ya dauko silallan zinarin dake gefensa ya ajiye a gaban NUAB din da suke dauke da sunan Ayanah ghaz baro baro a jiki.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

152
Yana ajiye wa bayansa ya mayar a natse ya jinginar a kujeran dayake zaune har lokacin kafarsa daya na akan daya ya zubawa NUAB idanuwansa wanda shima a natse ya dago idanuwansa masu kyau ya kalli sultan din kafin ya maidasu a natse akan abinda ya ajiye masa a gabansa ya zuba musu ido yana kalla.

Shiru sukai dukansu idon kowannensu na kafe akan abinda yake gaban nasu suna kalla,

Sultan jiran tambayar NUAB yakeyi duk da yasan bazai taba tambayarba koda zasu shekara a hakan koda kuwa menene bazai taba bude baki ya tambaya dinba sedai shi daya ajiye koma meye ya fada da kansa idan ba hakan ba zai gaba abinda ya kawosa ya miqe ya ficewansa.

Dan haka ajiyan zuciya mara sauti sultan ya sauke yana maida kallansa kan fuskan NUAB wanda ya dago shima yana kallansa ya bude baki yana kai hannunsa daya a natse ya tura silallan gaban NUAB din yace,

'Ina gabatar maka da sadakin mahaifiyarka Ayanah ghaz me girma Sultan LEUL boyem wanda aka daura auren sha ashirin ga watan daya gabata,
A yanzu ba kaine kake da cikakkiyar iko akanta ba nine mijinta,nine mahaifinka,nine Sultan dinka'

Kallansa NUAB ya dago yanayi da dukkanin idanuwansa yana jin maganarsa na sauka kaman baisan meyake fada ba sbd yasan zai iya fadan komai akan ya mallaki Ammin dan haka a natse ya maida idanuwansa akan zinarin gabansa yana kallan sunan Ammin dayake bayyana baro baro akai ya kalla tsawon mintina kafin ya dago da idanuwan ya sake saukewa sultan yana jin zuciyarsa na fara daukan zafin daya manta rabon da zuciyarsa ta dauka,

Bude baki yayi a natse yana kallan sultan din yace

'Ammin tasan da maganar dake gudana nan din maana tasan da aure a kanta??

Sake gyara jinginar zamansa sultan yayi yana sake murmushi me kyau da nutsuwa yana kallan NUAB din yace

'Kaine da baka saniba nake sanar dakai a yanzu sbd ka sani din Sultan dan Amarya'

Numfashi me dumin daya fara zafi NUAB ya sake kalmar na zafafar zuciyarsa ta tafaso sa ya sake kallan sultan da kyau yace

'Aure irin wanda kayi mata a baya na bata matsayin wishmah ka sake bata sbd bansan Ammina zata iya aure batareda sanina ba ko izinin dan kuwa a duniyarta kaf yanxu ni kadai ne waliyin aurenta da bada aurenta'

Ajiyan zuciya me sanyi da nutsuwa sultan ya sauke yana kallan NUAB din yace

'Aure ne mukai wanda kana buqatar nutsuwa ka fahimta hakan,
Ba raayinka ni nake nema ba,ba kuma izininka nake nema sbd mune muka haifeka bawai kaine ka haifemu ba,
Aure ne kaman kowane aure da akeyi me daraja da baa buqatan dogon bayani,
Amminka tana jin shakkar yanda zaka dauki lamarin ne ya saka aka ja lokaci batareda ka saniba ba amma tinda yanzu ka sani ka sani mahaifiyarka tayi tinanin abinda zaka dauka kafin ta amincewa auren dan haka a yanxu daka sani saka albarkanka kawai take buqata ba bacin rai da fushi ba.'

Yana gama fadan hakan miqewa zaiyi NUAB ya kallesa idanuwansa jajir zuciyarsa na wata irin tafasa da bacin rai me tsananin gaske da fushin dayake taso masa yace

'Kanada raayin hakan meyasa bakaiba tin a shekarun baya datake tsananin buqatan hakan?
Meyasa baka yantata ba a lokacinda hakan yakeda amfani?
Meyasa sai ayanzu?
Sbd ka kaine me juya rayuwanta a yanda kaso a lokacin da kaso sbd ita ba kowa bace face baiwar da aka saka kudi aka siya?

Yankar zuciyar sultan maganganun sukai ya dago idanuwansa shima da sukai ja ya kalli NUAB din cikin jin zafin maganar yace

'Eh sbd nine me juyata a yanda naso da kuma bata matsayin da duk nakeso sbd nine na siyota ba kaiba,nine me ita da cikakken iko da ita a kaf rayuwarta ba kowa ba,a yanzu danaga lokacin auren yayi shima gashinan na aure ta auren da ba wanda yakesa ikon sakawa ko hanawa idan ba ni dinba.'

Gama maganarsa yayi daidai da shigowan ayanah din wadda ta kasa nutsuwa da haduwan tasu saida ta iso dan haka kallan NUAB takeyi da idanuwanta da suka sauya sbd fargaban abinda zai iya biyowa baya,

Juyowa NUAB yayi ya kalleta da idanuwansa dake tsananta ja maganganun sultan sun gama buga xuciya da jininsa dan kuwa ko ayanzu ya fada masa uwarsa ba kowa bace face baiwarsa da zaiyi dik yanda yaga dama da rayuwarta,

Wani irin kallo yakewa Ammin yana jin ta gama rusa duk wani karfin zuciya da kuzarinsa ya bude baki yace

'Ammi kina ji da kunnenki ke din ba kowa bace face baiwar da aka saka kudi aka siya,
A hakan kika kuma zabarsa akan duka radadi da baqin cikin dana rayu a cikinsa sbd ke'

Rintse idanuwa Ammin tayi tana isowa gurinsa zata kamasa ya miqe tsaye yana kallan sultan wanda ransa yayi mummunan baci yace

'Ban karbi auren ba sbd nine me bada auren dan haka......

Wata irin tsawar da tinda sultan yake babu wanda ya taba yiwa ita ya sakarwa NUAB din wadda dakin gabaki daya saida ya amsa take Ammi ta shiga tashin hankali tana kallan sultan din kafin ta kalli NUAB wanda jikinsa ke wata irin rawa sosai idanuwansa jajir fuskarsa tayi ja.

Su kadir dasu aleey harma da maa sakinah data taho tareda ayanah a kunnuwansu tsawar me karfin gaske ta sauka wadda ta saka kowannensu qasa da kai jiki na sanyi da wata irin fargaba da damuwa batareda sun motsaba gurin ya sake daukan tsit.

'Zaka dena fadamun duk maganar dataxo bakinka kowane matsayi kake dashi kuwa daga yau sbd duk abinda kakeji kake taqama dashi nine na bakashi sbd nine na haifeka,
Nina na baka sunan dakake amsawa yau,
Nine na na baka jinin iko da mulki da izzar da duk kake ji a kanka da jininka,
Nine na baka kariyar da kake taqamar ka rayu ayau,
Nine na hana kaina duk kwanciyan hankali da farin cikin da duka mulki yake bayarwa nai watsi da girma da iko na na fixgeka daga hadarin dayake tattare da rayuwarka na baka dalilin daka zama jarumin dayake tsaye a gabana yanzu,
Nine na bawa mahaifiyar taka kariyar data rayu a cikin cikakkiyar kwanciyan hankalin da kake ganinta a gabanka a yau,
Nine wanda ya tsaya ya tsayu akanka na baka kariyar da bazaka taba zama abinda ka zama abinda ka zama ba a qasar da ba taka batareda na taba baka dalilin rauni ba,
Ni ba ubanka ne kadai ba daya kawoka duniya ni saviour dinka ne,
Ni sultan dinka ne,ni ubangidan mahaifiyarka ne sannan ni ayanzu mijin mahaifiyarka daga karshe ni masoyinta ne da 'dan da muka haifa bai isa ya saka sharadi a gabanmu dan haka ka aje matsayinka na sulta a komai nine ubanka da you must learn how to talk and respect me to the core...'

Da wani irin zafin gaske ya qarasa maganar wadda take fita da karfin gaske cikin bacin ran da babu wanda ya taba gani wanda ya saka Ayanaah kallan NUAB wanda shima rawa jikinsa yake sosai har lokacin jan idanuwansa kaman zasu kama da wuta sbd ayau ya tabbatarda idan aka haifeka angama shan gabanka duk kuwa abinda kake ji dashi ko kake dashi dan kuwa abinda yake ji yafi wuta ci a jininsa amma baida yanda zaiyi bayan tsayawa yana sauraran gorin da ubansa ke masa shida uwarsa bama tareda ita tasan hakan ba.

Dago idanuwansa yayi ya kalli sultan din wanda ko kallansu ya dena sbd tafasar da zuciyarsa ke yi shima ya gaji da zafi da fushin NUAB dayake tolerating tin yana yaro wanda yana masa uzuri ne sbd yasan zafin son dayake wa Amminsa dashine ya saka ya tashi da jin zafin rashin ganinsu a tare amma sam ya kasa gane cewa son dayake masa ne yake sakasa jin tsananin zafinsa daya kasa zabarsu da Amminsa akan kowa bayan shi kuwa yafisa jin zafin ciresu da yayi daga jikinsa sbd basu kariyar da ayanzu suke tsaye tareda juna.

Magana NUAB din zaiyi shima cikin kololuwan quntata da maganganun Amminsa ta katsesa da tsawa me karfin gaske itama tana riqosa cikin damuwa da rasa abin yi tace

'NUAB mahaifinka ne kome kake ji zaka hadiyesa ayanzu batareda ka bayyanaba sbd tinda ya haifeka ya gama maka komai,
Kome laifinsa a

83 / 100