Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   53 / 100

156K to 159K   out of 299.8K words

tana jin hannuwansa sun kasa saketa wanda ta kasa doguwar motsi itama tana rufe idanuwanta sbd nauyin idanuwan dana hannuwansa dake rungume da qugunta tana jikinsa sosai,

Dago idanuwanta tayi a hankali batareda ta motsaba tana san kallan fuskarsa amma zuciyarta na hana hakan,

Maida kanta tayi qasa tana son sake rabuwa daga jikinsa,

Sake kallanta yayi yana jin dukkanin motsinta a jikinsa,
A natse ya saketa tareda tayar da ita zaune daidai a kan kafafunsa yana qin kallanta sbd zuciyarsa dake wani irin zafi da radadin abinda ya kusan faruwa da ita a daren wanda zuciyarsa ta kasa sakewa ta kasa iya cirewa daga idanuwa,zuciya,kwakwalwan da tinaninsa shiyasa babu sauyi ko daya daga yanayinsa na fushi da tsantsar baqin ciki da bacin rai a daren wanda tabbas bazai mancesa ba sbd abubuwa da yawan da suka faru a cikinsa,

Yanda ya zaunar da ita akan kafafun nasa ya sakata dagowa a hankali jiki a mace ta kallesa sbd jin shiru har lokacin bai iya furta kowace kalma ba hakama hannuwansa tabi da kallo taga jijiyiyin jikinsa duk sun fito alaman jininsa tafasa yakeyi,

Tasan yanada yawan fushi da zafi ga duk abinda aka tabasa akansa amma bata taba ganinsa a irin wannan yanayin ba wanda ya sakata jin jikinta ya sake mutuwa ta dago idanuwanta dasukai mummunan nauyi sbd kuka ta kalli fuskarsa wadda tayi jajir tana kasa dauke idanuwanta sbd shima dagowa yayi a wani yanayin daya saka tsikar jikinta gabaki daya miqewa ya bar idanuwan nasa akanta har lokacin babu wanda ya iya cewa komai a tsakaninsu bare motsawa.

Ahankali ya sauko da idanuwansa zuwa ga wuyanta da jini yake kwance a jikinsa zuwa cikin rigarta daga gefen kafadarta,
Fuskarta ya dawo da idanuwansa kafin ya sake maida kallansa akan jinin wanda da alama rauni ne taji wanda itama bata san dashi ba.

Idanuwanta ta dauke akansa a sanyaye tana dorasu akan inda yake kalla da dukkanin jajayen idanuwansa dake qaruwa a lokacin,

Ganin jini a jikinta ya sakata jin kanta ya sara da karfi hannuwanta na dan daukan rawa tsananin tsoro da wata irin firgita na shigarta ta daga hannunta dayake rawa sosai a rikice zata dora a gurin ya kama hannunta da nasa yana hanata tabawa tareda zuba mata idanuwansa cikin wani slow dayake tafasa jininsa,

Wasu sabbin hawayene suka ciko idanuwanta wainda ya kalli cikinsu baya iya cewa komai sbd idan yakai karshen qonuwa a bacin rai da fushi baya magana sam sam.

Hannunsa yakai gurin kai tsaye a cikin wata nutsuwa ya kama rigarta ba tsammani taji ya saukar daga kafarta wanda ya sakata saurin kama hannunsa da tafin hannunta tana dagowa ta kallesa hawaye dake cikin idanuwanta suna gangarowa a hankali.

Bai kalleta ba idanuwansa na kan raunin ya saka hannunsa dayake bayanta ya mannota sbd bayan datai kadan ta manno da kirjinsa sosai ya zagaye qugunta da hannunsa daya tareda qarasa saukar da rigarta daga kafadarta wadda ta sakata rintse idanuwanta da karfi bugun zuciyarta na fita da karfin dayake iya gani a saman fatar kirjinta fara tas datake wani daukan ido.

Jinin ya zubawa ido tin daga inda ya fara zuwa inda ya sauka wanda ya tsananta wani nauyin karjinsa sbd ba raunin dataji jinin wani ne ya dauka a jikinta wanda ya sakasa jin hannuwansa na dan rawar data sakata bude idanuwanta ahankali tana fara saukewa a fuskarsa wadda ya dago jajayen idanuwansa ya zuba gabaki daya akanta yana mata wani irin kallan daya ringa saka bugun zuciyarta qaruwa ta maida kallanta akan gurin wanda itama taga tamkar jinin ne kawai ta daga hannunta dayake rawa ta nufi gurin zata taba ya sake riqe hannunta da karfi yana hanata taba jinin dayake jin yana neman yanke numfashinsa sbd nauyin da kirjinsa yayi sbd tabbatarda jinin a cikin mazan biyu ne da suka tarar a dakin.

Miqewa tsaye yayi batareda yace komaiba ya dauketa kai tsaye toilet dinsa da baya taba iya sharing da kowa a rayuwarsa baya iya sharing toilet da bakwancinsa da kowa tin yana yaro bai taba iya hada gurin kwanciya da kowa ba bare hada toilet,

Ciki ya nufa da ita kai tsaye sbd shi kansa bazai iya saka hannunsa a jinin wanda iya ganinsa tafasa nasa jinin yakeyi ba bare barin ta saka hannunta,

Girman da toilet din nasa yake dashi ya saka suna shiga wani sanyin gaske ya ratsa har zuwa cikin naman jikinta ta rufe ido tana jin wani iri.

A tsakiyar shower ya ajiyeta idanuwansa a rufe ya sakar mata ruwan dumin data ji saukansu a bazata ta ja wani irin numfashi me karfin gaske tana qamqame hannunsa a rude ba tareda tasan tayi hakan ba,

Tin daga tsakiyar kanta da abin rufarta ya fadi tin a farkon shigowansu palonsa na farko ruwan ke zuba suna bin fuskarta suna sauka a wuyanta zuwa kirjinta da gangar jikinta.

Tsaye yake a gabanta ruwan na sauka har a kusan rabin jikinsa shima idanuwansa na kafe a wuyanta zuwa kirjinta da ruwan suke wanke jinin yana sauka,

Akan idonsa jinin ya kama wankewa tas batareda ya saketa ba duk da ruwan sun isheta hakama ya hanata saka hannunta ta wanke sbd zai iya zama makashin gaske idan hannunta ya taba jinin wani.

Ruwa sosai suke sauka a jikinta bayan komai ya wanke tas amma ya kasa saketa cikin wani irin yanayin tinawa da kaman baida cikakken hankali a yanzu ya sakata qwacewa tana fitowa daga ruwan tareda qin kallansa ta nufi inda taga towels dinsa a jere ta ja daya ta fice daga toilet din tana rufe jikinta da towel sbd wani irin sanyin ac daya ratsa har qashinta.

Bata tsaya a dakinba kai tsaye dakin data saba zama ta nufa tana isa dakin cire kayan jikinta tayi sbd wani irin kakkarwan sanyi da jikinta keyi me karfin gaske take tanajin zazzabi na shigarta me karfi shima komai daya hade mata a daren guda ga wani irin tsananin ciwon kai.

Daqyar jikinta na wata irin rawa ta iya zare komai ta saka kayansa da kusan sune a dakin take sakawa.

Bata iya tsayawa busar da gashinta me tsayin gaske dayake a jiqe ba hakanan ta dunqule guri daya a jikinta na rawa sosai.

Acan bathroom din kuwa bayan fitowanta bai iya motsawa ba sbd zuciya ta gama cinyesa ayau tin farkon safiyar babu abinda jininsa yakeyi bayan quna da tafasa har zuwa daren da tsakiyar daren ma da ayanzu yake jin idan bai iya controlling na zuciyarsa ba zai iya zama makashin mutune da dama a daren sbd an wuce dukkanin iyakarsa da baa wucewa a rayuwa.

Tsakiyar ruwan data fita ya tsaya yana samun ruwan na sauka a jikinsa suna dan sassauta zafin dayake jininsa da gangar jikinsa.

Mintina ya dauka sosai abubuwa da dama suna yawo a cikin kwakwalwan kansa gameda rayuwar daya samu kansa a ciki a lokaci daya,
Da kuma rayuwar da zaiyi daga daren yau dan zuwa safiyar gobe shine Sultan din da zai mulki qasar daya tsana da dukkanin zuciyarsa,

Zan zauna a qasar daya tsana
Zai rayu akan mulkin da shine ya hana mahaifiyarsa 'yancinta na shekaru,
Daga gobe zai rayu a matsayin SULTAN LEUL NUAB ALMAZZ batareda ta taba kauna ko raayin hakan ba dan kuwa hakan shine abun da yakewa dukkanin tsanarsa da bai taba sanin kaddara zata kawo sa akan matsayin ba.

Fitowa yayi daga shi sai towel mai haske sosai a qugunsa gashinsa dayake sake har a kafadarsa tsiyayar ruwa yakeyi shima.

Tsayuwa yayi a gaban mirror wani irin sanyi me tsananin gaske yana ratsa shi amma bai motsaba ko kadan sbd hakan yana rage zafin dayake ji a cikin gangar jikinsa sosai wanda yake kaman zai kama da wuta.

A haka ya bude tas kafin ya busar da gashinsa da dryer yayi shirin kwanciya ya fice daga dakin jikinsa a matiqar sanyaye ya nufi dakin datake sbd ayau Rauninsa a kusan bayyane yake.
#MAMUH
#HOTLOVE
#BESTSTORY
#2SULTANs
#2AYANAHs


HAYATEEM novel
700
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

94
Wata nutsuwa ce ta saukar masa wadda take tattareda sanyi da kawar da dukkanin fushi da hayaniyar kansa tareda sakarwa jikinsa sanyi da kamewa dan haka a natsen ya isa kofar dakin ya bude a natse tareda saka kai a ciki sbd bai hangota akan gadon ba.

Da wata irin kwantacciyar nutsuwa ya qaraso cikin tsakiyar dakin yana sauke kyawawan idanuwansa akanta tana dunqule a kan sofa idanuwanta a rufe tayi baccin wahala zazzabi me karfi yana cin jikinta.

Tsayuwa yayi a kanta tareda zuba mata idanuwansa da suka dan sauya kadan yana kallan gashinta dayake a jiqe a jiqe har lokacin bai bushe wanda ya tabbatarda zai sakar mata ciwo.

Durkusawa yayi a hankali daidai kanta ya saka hannunsa ya taba gashin wani sanyi ya ratsa tafin hannuwansa ya dauke hannunsa ya miqe ya nufi inda dryers na dakin suke bama daya ba ya dauko ya janyo har inda take yafara busar mata da gashin a yanda take kwance batareda ya bari zafi ko iskar yayi mata yawa ba,

Duk abinda yakeyi bai kalli fuskarta ba harya gama ya maida ya dawo ya yaye rufar dake jikinta a hankali ya wanda ya sakata bude idanuwanta a hankali cikin zafin zazzabi ta kallesa batareda ta ce komaiba se motsawa datai zata tashi zaune sbd bata buqatan komai da kowa a lokacin ita kadai tasan abinda take ji a gangar jiki da zuciyarta,

Yunqurawa tayi a matiqar galabaice zata tashi ya dakatar da ita da ta hanyar dora hannunsa a cikin sanyi kan kafadarta ya hanata yunqurawan.

Daukanta ya sake yi batareda hayaniya ba ya nufi gadon dakin ya kwantar da ita ya rufe mata jikinta dayake dan rawa ya zauna bakin gadon tareda rintse idanuwansa sbd a yanzu wata irin damuwa ce me tsananin nauyi ta danne kirjinsa a rayuwar daya samu kansa na matsayin daya hau kan kansa duka a cikin dare daya,
Nauyin daya rataya a kansa jin yake tin ayanzu ya danne kirjinsa yana raba gangar jikinsa da wani sashensa dashi aka haifesa.

Mahaifinsa ya yanka rayuwarsa ya datsata a gabansa ya lalata masa buri da dukkanin abinda yayi shekaru yana ginawa a zuciya da rayuwarsa,
Mahaifinsa ya wargaza tsarinsa da akidarsa ta rayuwa
Mahaifinsa ya tilasta karban rayuwar da babu ita a kundin rayuwar daya tsarawa kansa da mahaifiyarsa.

Numfashi ya sauke me zafi daya fito a natse tareda bude idanuwansa da suka sake sauyawa zuwa ja ya waiwayo ya kalleta ta sake komawa baccin wahala itama.

Zubawa fuskarta datake bayyanar da halin ciwon datake ciki ya dauke idanuwan yana miqewa ya koma kan sofan datake dakin tana facing gadon ya zaune a natse tareda jinginar da bayansa ya dora kafarsa kan daya a natse tareda folding hannuwansa yana sake kwantar da kansa jikin kujeran yana rufe idanuwansa sbd kansa dayake sarawa.

********
Sultan me murabus kuwa a daidai wannan lokacin da shima ya isa har asalin bedroom din ayanah ghaz wadda qamshinsa ne ya fara ratso mata cikin dakin duk da tana cikin mummunan halin tinanin bayyanar halittar data kasance jinin abaas a gabanta batared bayyanarsa ba da shine mahadin karshe na rayuwarta shigowan qamshin namji na uku a rayuwarta wanda sune suke da rayuwa da ruhinta ya sakata rufe jajayen idanuwanta da suke cikin matsanancin halin da zuciyarta take ciki sbd Abaas shine namijin da yafi kowane namiji a rayuwarta kafin 'dan ta NUAB da mahaifinsa Sultan yasar.

Rufe idanuwanta yayi daidai da sako kansa dakin a cikin wata irin nutsuwan da bai taba samu ba a tsawon shekarun mulkinsa ba,

Idanuwansa masu kyau da haske saukesu yayi akan ayanah ghaz wadda nata idanuwan suke rufe tana jin zuciyarta na kokarin bugawa ya tako a natse har gabanta daidai nan ta miqa hannu zata dafe kirjinta dayake wani irin radadi.....riqe hannun nata yayi da nasa a cikin wata irin nutsuwa da samun cikar burin dayafi kowane burinsa a duniya yana kafawa hannun nata daya riqe da nasa idanuwansa batareda ya kyafta ba tasa zuciyar na wani irin ciwon daya debi shekaru yana hadiyewa shi kadai.

Hannunta daya ta dago zata dafe kirjin dashi sbd jin takeyi zuciyarta na kasa daukan abinda take ji ya sake riqe hannun da dayan hannunsa tareda dago idanuwansa ya kalli fuskarta cikin cikakkiyar asalin nutsuwansa daya jima da rasawa akanta yaba kafesu tareda tsayar dasu akan fuskar da yayi shekaru bai yiwa kallan daya bawa zuciyarsa sanyi da hasken data rasa,

Bude nata idanuwan tayi a cikin wani irin mutuwar jiki hawayen abinda take ji na radadin zuci da gangar suna gangarowa daga idanuwanta ta sauke su akan fuskarsa da tinda take bata taba masa kallan ido cikin ido ba sai ayau din ta zuba masa su hawayenta na tsananta gangarowa ta kasa riqe abinda take ji zuciyarta na neman bugawa sbd bazata iya rayuwaba idan aka fada mata wani labarin daban akan abaas ta bude bakinta ahankali muryanta na cikeda wani irin raunin datake shirye da barin duniyar da babu abaas tace

'Abaass gha.....

Tafin hannunsa me sanyin dayake keto a cikin daren ya saka yana rufe bakinta a cikin wata irin sanyi da tsantsar kaunar datake bayyanuwa a idanuwansa babu burki yana tsayar da kallansa dakyau akan fuskarta baya buqatan jin dacin dayake tattare da zuciyarta wanda yana jiyosa a tasa zuciyar sbd yasan wani tsantsar baqin ciki da mafi dacin rayuwarta ne zata ratsa a duk abinda zaa sanar da ita gameda 'dan uwan nata wanda ya gama sanin komai akanta amma koma wane halin zata shiga na rashin dan uwan da shine rayuwarta ya shirya tayata shigarsa da tsayuwa akanta batareda ta rasa kanta ba har sai ta samu nutsuwa da saukin komai daga abinda zata dandana rashin da jajjiga rayuwa da duniyarta,

Babu abinda yakeson ji daga gareta ya yafe wannan damar da matsayin ga 'danta sbd shine wanda zai iya bata sassaucin datake buqata a lokacin da zataji komai daga bakinsa,

Tin daga lokacin da ta shigo rayuwarsa mulki da matsayin da dukkanin mulkin yake bayarwa ya fita a kansa,
Rayuwa yakeso wadda ita kadai ce zata kasance dashi a cikinta,
Rayuwa yake so wadda shine kadai zai kasance mata a cikinta ya bata dukkanin farin ciki da walwalan da qasarsa ta bata dan kuwa kaddarar haifa masa 'da ce ta rabota da komai nata da farin cikin da har abada kila ta rasa,

Wasu hawayen nata ne masu zafi suka gangaro a sanyaye suka sauka akan fatar hannunsa datake rufe da bakinta ya gangara da idanuwansa akan hawayen dake kan fatar tasa suna gangarawa zasu sauka kafin ya dawo da kallansa akan fuskarta da itama shi din ta dago ta sake tsayar da idanuwanta kafin wani irin kuka me tsananin tsima zuciya ya taho mata ta fasa a hankali tana rintse idanuwanta da karfi babu abinda ruhi da zuciyarta da idanuwanta da gangar jikinta suke tsananin nema da muradi a lokacin bayan bayyanar abaas a gabanta.

Qamqame hannuwanta Sultan yasar yayi yana sauraran kukanta da sautinsa suna ratsa sa idanuwansa na sauyawa kafin ya saketa a hankali tareda zaunawa a gefenta a wata irin nutsuwa ya bude hannuwansa ya zagayota a natse ya shigar da ita jikinsa ya rungume da sanyayyar nutsuwan data isa gareta ta rintse idanuwanta tana sake fasa wani kukan dayake jinsa har tsakiyar kirjinsa data toshe.

Kuka takeyi sosai wanda yake na tsantsar tsananin tsoron dayake shigarta wanda bata shirya ji ba koma menene ya kawo bahar gareta batareda abaas ba  dan haka zuciyarta ke wata irin karyewan da bazata taba gyaruwaba.

Dukkanin kukanta da radadin dayake tafe dashi ratsasa yakeyi yana karbansa hannu bibbiyu da radadin da quncin da komai duk karba yakeyi a zuciyarsa idanuwansa jajir yana sake rungumeta da karfi a jikinsa.

A haka ya qarar da kutsawa a cikin kowane quncinta daya shirya rayuwa a cikinsa har qarshensa tareda ita.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

95
Acan bangaren ma SULTAN NUAB a zaunen ya kwana batareda rintsawa ko ta second dayaba idanuwansa a kafe guri daya zuciyarsa a nauyaye da abinda baisan ya shigesa ba har akai asuba tukuna ya iya miqewa dan sallah.

Kai tsaye masallacin masarautar dayake duk wani sultan acan yake sallah tareda manya ayau shima da yaransa can suka nufa dan gabatar da sallarsu acan sabanin tasu da suke hada jam'i suyi a nasu masallacin da suka tadarwa kansu a bangarensa.

Ba dukkaninsu suka tafi ba wasu anan bangaren sukai sallarsu shi kuwa da aleey da keelah tareda wasu daga securities dinsa masallacin suka nufa a karan farko sbd a yanzu shine me masarautar gabaki dayanta.

A lokaci daya ya iso masallacin tareda mahaifinsa wanda ya kallesa da idanuwansa da basu gama dawowa daidai ba shi kuwa bai dagoba sbd baya buqatan kallan kowa a yanzu bare wata hayaniyar da zata qarawa kansa nauyin dayake ji,

Ganin securities dinsa suna kokarin cike rabin masallacin yasa kusan kowa iya kansa yana bin sahun sallah a natse dan tada sallan da zaayi batareda tsayawa kallan kwaf ba zuciyarsu na shiga rudanin ganinsa a masallacin tareda tsananin tsoro da fargaba da zullumin abinda suke ganin kaman yana shirin tabbata cewan shine Sultan din boyem a a yanzu.

A guri daya ya tsaya sahu kafada da kafada da mahaifinsa wanda shima yake cikin yanayi na rashin son hayaniya,

Sallah akai aka kammala kowa yayi tsit da adduar da kowa yake sanarwa ubangiji har gari ya fara haske wanda kowa ya fara silalewa daya bayan daya suna barin masallacin dan tafiya fara shiri sbd da safiya ake nadin sarautar qasar wadda a cikin tsakiyar daren dukkanin labarin nadin sarautar goben ya fita yana isa ga duniya da duk inda ya kamata ya isa sbd akan dole manyan fada basu rintsa ba suka kwana aikin nadin mulkin sbd dolensu ne.

Koda ya koma bangarensa babu wanda ya sake zuwa fara shirye shirye kawai akeyi tako ina wanda ya saka koina ya dauki wata irin harama da hayaniya amma banda bangarensa wanda yake tsit babu kowace hayaniya duk da su aleey wani irin zazzafan shirin sukeyi tareda tsananta wani irin tsananin tsaro da securities tako ina,

A bangaren ayanah tinda sultan ya fice su tenya suka sanar da ita NUAB ne sultan na yanzu wanda zaayi nadinsa ayau.

Wani irin sabon nauyi taji ya danne kirjinta amma tin da kansa ne ya karba ba dole aka dorasa ba tasan an cika mata alkawarinta,

Tausar zuciyarta tayi daga dukkanin abinda takeji zata jira ayi nadin sarautar ayau din a gama kafin ya fuskance ta shi da Sakinah su sanar da ita menene yake faruwa wanda bata saniba dan haka ta saka dukkanin karfin hali da taurin zuciyar da batada ta

53 / 100