da wata irin kewan dake bayyana a idanuwansa da gangar jikinsa.
Baiwar hailen ce dake gabanta tana mata iso ta bude kofar palon na kurya inda suke a zazzaune tana janyewa daga kofar dan bata damar shigowa.
Kafarta ta fara sakowa a natse cikin palon ita kadai bayinta na palon farko dan basa shigowa nan din.
Gabaki dayansu kofar suka juyo suna zubawa ido sbd shigowanta ya shigo musu da wata irin kamshi me tsananin sanyi daya kama jikinta sosai kaman wacce akewa shirin sabon aure sbd duka basirar tenya ta gyaran Amare da shiryasu ta fiddota akansu wannan karan wainda duka kayan qamshinta dasuka gama kama jiki da suturar su bahar din hatta wayoyinsu sun kama qamshin kai me karatu zaka iya samunsu tsaf a gurin SHUWA INCENSE AND MORE 07042293387,
Qamshin da zaka samu a jikinsu Leylah da Bahar din tsaf zaka samu komai da komai da duka abubuwan gyaran jiki da tabbataciyar qamshi da hatta gashin kanki da panties naki zasu ringa fidda qamshi me sanyin da ko zama kadai a kusa dake zai bawa ruhin mijinki nutsuwa ki tintibi SHUWA INCENSE AND MORE 07042293387.
Kallan mamaki dukansu suke wa Leylah wadda kwata kwata ta dena zuwa bangaren sedai a waya take kiran mamin ta gaidata sai kuma can baa rasaba take zuwa ta gaida mamin sai kuma yau gata kuma da wannan lokacin na dare.
Akan Asim daya nutsu yana ginginar da bayansa jikin kujera tareda tattara nutsuwansa guri daya ya kafeta da fararen idanuwansa suka maida kallansu sukaga yanda imaninsa gabaki daya yake kanta yana kallanta.
Takowa leylah tayi a natse tana jin gabanta itama yana dan faduwa sbd ganin wanda bata taba tinanin ganiba a lokacin dan haka ta kasa dagowa tai qasa da kanta tana jin idanuwansa tsaye cak akanta yana mata kallan dayake kashe duka jikinta.
Haile kafe Asim da ido tayi cikin tsananin mamakin yanda ya mace mata a zaune ya tsayar da nutsuwansa akan mace.
Mutuwa ta sake jin jikinta yayi sbd wata sabuwar balai da masifar ce take bayyanar mata dan kuwa a yanda take gani a yanzu Asim ya gama susucewa akan leylah dake jinin Ayanaah shikenan shima rasata zatai wa ayanah kenan,
Leylah na isowa cikin girmamawa ta zauna gefen kafafun mamin tana bude baki ta gaidata a natse.
Daqyar Haile ta iya bude baki tana shiga wani sabon yanayi ta amsa tana kasa dauke idanuwanta daga leylah da gabaki daya ta sauya tayi wani irin hasken daukan ido da cikowa tayi mulmul kamar amaryar dake cin amarci da sabon ciki.
Su Aslam ta juya tana gaidawa suma cikin girmamawa da tambayan kwana biyu tana kokarin nuna sakewanta da girmamawa garesu.
Suma amsawa sukai suna kallan Asim wanda fuskansa tafara sakewa da sanyi suna mamakinsa da gane abinda ya tsayar dashi kenan.
Kaman bazata kallesa ba sbd yanda take jin tsananin nauyi amma kuma sbd nuna girmamawanta garesa gaban mahaifiyarsa saita dago a natse ta kallesa da idanuwanta dasuka qara haske sosai idanuwansu suka hadu take ya sarqe da yawun bakinsa yafara tari a hankali yana dan kamewa sbd ganin idon kowa na kansa mamaki na neman kashesu.
Gaidasa tayi tana dauke idonta batareda jiran amsa ba.
Amsawa yayi yana dan gyara murya kafin ya juya ya kalli haile data koma kaman me zaman takaba sbd yanda fuskanta tayi kalar tausayi ya bude baki yace
'Mami sallama Leylah tazo miki gobe zasu wuce Anjom gabaki dayansu asalin garinsu Ammi sbd hidimar bikin da zasuyi kuma ita Ammin ba dawowa zataiba acan zata zauna tukuna so ba tafiyan dawowa ce yanzu ba idan suka tafi shine taxo miki bankwana..'
Ba haile ba hatta su Aslam juyowa sukai gabaki daya suna tsayar da idanuwansu a kansa cikin rikitaccen yanayin kasa fahimtar me yake fada sbd barin ayanah boyem gabaki daya kaman yana nufin barin Sultan yasar barin boyem din gaba daya ya koma can da zama.
Meryam mahaifiyarsu ta maida idanuwanta akai tana kallan yanayinta sbd jan da fuskarta da idanuwanta sukai a take hannuwanta na dan rawa ta dunqule su tana hana leylah dake gefenta ganinsu tanajin kaman numfashinta na toshewa a kirjinta,
Sultan barinta zaiyi ya koma garin imebēti dinsa da zama shikenan kaddararsu ta zama tarihi ko me?
Da bataji hakan ba da sedai idan zai tafi taji kokuma idanma ya tafi ko me?
A karo na biyu na karshe zai sake nunawa da bayyanawa duniya Imebēti dinsa ya zama akan kowa da komai yabarta anan ba miji,ba 'da ba mulki ba daraja ba farin ciki ba walwala.
Wannan itace kaddarar da bazata taba dauka da yadda ba dan kuwa a yanxu anxo karshe komai ya qare ya wuce limit din daukanta,
Asim ma barinta zaiyi yabi leylah shima acan zai rayu sbd a yanda take gani yanzu gabanta Asim akan leylah tsaf zai koma can yayi rayuwan dayake buqata ita shikenan ayanah ta kwace komai ambatarta da zallan tsoffin 'yaya a gabanta da tulin baqin ciki tana rayuwa a karkashin iko da mulkin 'dan Ayanaah wanda batada darajar da ko kallan arziki daga garesa,wallahi tallahi bazai yiyuba bazata yadda ba.
Rawa jikinta ya fara idanuwanta na rinewa wanda ya saka meryam ma datake cikin tinani kala kala akan ita dai kada sultan ya tafi batareda anzo neman auren nata ba duk da wlh ko can ita anjom din tsaf zata saka a samesa a nema auren acan hadda daurawa ma idan ta kama kawai dai ita burinta kafa Mamin ta shiga tashin hankalin da zaayi wata babbar tashin hankalin dazai saka ya sake ciresu daga rayuwarsa yace haryanzu bin hudubar mamin sukeyi.
Tasowa tayi ta dan daure tana kallan leylah tayi mata fatan Allah ya kiyaye tareda fatan ayi bikin lafiya a watse lafiya ya kuma bada zaman lafiya.
Asim ta kalla wanda duka halinda suke ciki baisaniba dan baima lura ba tace masa leylah din ta tafi ta kwanta tinda akwai tafiya gabanta ga dare yayi.
Miqewa yayi a natse batareda jin komaiba ya miqawa Leylah din hannu wadda ke kokarin tashi daga qasan tana jin ba dadi sbd zaman datai a qasan da qaramin ciki.
Satar kallan Haile data fice hayyacinta tayi tana qin kama hannun nasa sai dayaga zata sake komawa dabas ya saka hannuwansa biyu ya kamata yana tadata gabaki daya cikeda kulawa ta bude baki tayi musu da safe ba wanda ya isa amsawa se meryam tana binsu da ido har suka fice Asim din na riqe da hannunta.
Suna fitowa time ya fara kalla yaga duka duka mintinanta shida da baro bangaren Ammi bayan yasan a qalla anbata kusan mintina talatin xuwa arbain dan haka daukanta yayi cak sbd kafarta ma kada tayi tafiya a gane
Kai tsaye bangarensa ya nufa da ita yana kallan kyakkyawar fuskanta da ita shi take kalla tana shiga tsoro tana ce masa Maa zata bata ransu su duka idan tasan ta qara gaba daga bangaren Mami.
Murmushi me hade da tsantsar farin ciki ne ya taho masa yana kallan bakinta dayake maganar yakai bakinsa akai yayi mata wani kiss me tsantsan sanyin daya kashe bakinta yace
'Ta kwantar da hankalinta ina zuwa daurin auren Kadir bazan dawoba saita san yanda zatai dani matiqar ba tareda ke zan dawo ba'
Kaman a mafarki taji maganarsa dan haka ta kafesa da ido tana kasa motsawa sbd jin yanayi me sanyi yana ratsata dan kuwa daman damuwanta idan acan anjom ko anan zata zauna bayan bikin batasan makomarma inda zata zauna ba.
Tambayarsa maanar abinda ya fada tayi a natse shima cikin nutsuwan ya kalli cikin idanuwanta ya fada mata duk inda zaiyi rayuwa ta tabbata da ita zaiyi a duk inda take so bayan boyem.
Ajiyan zuciya ta sauke tana jin farin ciki na ratsata da batasan lokacinda ta saka hannuwanta biyu ta zagayo wuyansa ba ta rungume tana lumshe idanuwanta farin cikinta na bayyanuwa.
Suna isa bangarensa a palonsa suka zuba ya zaunar da ita a cinyarsa yana kama fuskanta kai tsaye ya hade da tasa yana hade bakinsu yafara mata wani lafiyayyan kiss me tsananin shauqi da nutsuwan da basu taba samuba a tsakaninsu yana mannota jikinsa.
Acan dakin maa tenya kuwa wayar mai girma Sultan NUAB ce ta shigo wayarta inda kai tsaye ba kowace irin kwana a zancensa ya sanar da ita ba kowa ya bawa matarsa ya tafi da ita Anjom ba bayan ita kuma duk abinda sukeyi ayisa a gama kafin isowansa daurin auren wanda matiqar kafarsa ta sauka qasar babu abinda zai sakasa barin Queen dinsa.
Mamakinsa zuwa yanzu ya dena bata shock ko bugawan zuciya dan haka da angama kawai ta bisa dan haka ta tabbatarda suna isa akan bahar zatafi maida hankalin aikinta dan kuwa zatai mata gyaran da idan ta dawo zata jima a gyaren sbd a yanzu zasu dade batareda suna ganin juna ba.
#MAMUH
09033181070: HAYATEEM
Mamuhgee
166
Duk yanda suka shagala basu bari sun wuce lokacinda zaa gane bata bangaren Maminsa ba dan haka babu abinda ma yayi mata kawai yar soyayyarsu sukai ya dawo da ita har kofar bangaren ya sake rungumeta yana kissing gefen fuskanta tareda jin kaman bazai iya jiran ranar daurin aurenba zai wuce gaba yabi bayansu idan suka wuce.
Daqyar sukai sallama ta shige ya juya yana jin qamshinta da nasa na tashi duka a jikinsa ya sauke ajiyan zuciya yana jin farin ciki mara iyaka cikasa wanda ya manta rabansa ma dashi.
Itama tana shiga ba kowa dan haka a kofar dakin maa tenya ta tsaya ta sanar da ita dawowanta sbd batason ta shiga jikinta duka qamshinsa yakeyi ta silale ta wuce dakinsu.
Ko data je Bahar na kan waya da NUAB yana fada mata yanda zata kula da kanta ita kuma tana kwance kaman mara lafiya a dunqule cikeda kasala da mutuwan jiki muryanta na fita a kasalance tana neman hanasa zaman lafiyar zuciya da gangar jiki.
Leylah zare hijab dinta kawai tayi tana nufar toilet harta fito suna wayar itama zuwa tayi ta kwanta xuciyarta fes tana jin yau damuwanta da duka baqin cikinta yakau.
Washe gari da shirin tafiya da farin ciki suka tashi musamman ayanah da sakinah da sukejin finally zasu koma qasarsu suyi rayuwa,
Qasar da suka cire rai daga saka zuwanta a rayuwarsu sai gashi sun tafi yanzuma zasu koma gida da farin cikin da yariga yayi gibin da bazai taba cika ba sbd wainda aka bar gida taredasu aka fara tafiyar dasu,
Anfara dasu baa gama dasu ba wanda kaman koyaushe gibin da Abaas da Nurat suka bar musu bazai taba cikewaba duk kuwa farin cikin da zasu samu a rayuwa.
Sultan NUAB ya shigo bangaren da karfe goma na safiyar ya shiga ya gaisa da iyayen nasa kafin yayi magana da Ammi tsawon lokaci kafin ya fito ya fice.
Harya shigo ya fice Queen din boyem tana bacci bata farka ba har lokacin shima kuma daman baima saka ran ganinta ba sbd yasan bata farkaba dan sunyi magana da asuba yasan zata jima bata farkaba sbd yanda suka jima suna maganar a waya da asuban.
Karfe sha daya na rana ta farka tayi wanka dasu brush da sauransu ta fito tana jin jikinta ya samu karfi.
Shiryawa tayi ta fito ta nufi dakin Ammi ta gaidata Ammin na binta da ido ta fito tayi dakin Maa tenya ta tadda maa sakinah acan suna magana dan haka anan tayi zamanta salmah ta kawo mata abincinta anan taci tana shiga firarsu a natse ba hayaniya.
Tana gamawa mum zuhrah nashigowa sbd lokacin tafiyansu ya kusa.
Karfe daya da rabi jirginsu zai tashi dan haka karfe goma sha biyu da arbain harma da mintina akai Bayi suka fara fidda kayansu inda motocin dake jere suna jiran fitowansu ana sakawa.
Gama fidda kayansu akai kaf kafin suka fito kowannensu a shirye cikin nutsuwa da mulki da wayewan da duka ta ratsesu tareda daula.
Tin daga iyayen har yayan designers ne a kafafuwa da hannuwansu maana shoes and bags dinsu dan kuwa su chanel ne da Lv dasu Dior ke hannuwansu daban daban wainda kudin kowace zai baka mamaki idan kaji,
Bahar kai tsaye ita da maa tenya da sakinah wucewa gaba sukai sedai zuhrah da Ammi da leylah ne suka tafi har bangaren haile dan yi mata bankwana amma bata iya ganinsu ba sedai meryam tace musu bacci takeyi bata jin dadi,
Haka suka fito batareda sun gantaba suka wucewansu zuwa mota,
Motoci ne a jere na alfarma da suke daukan ido saina securities acan gaba suma a jere suna jira dan kuwa ba qananun securities aka hadasu dasu ba dan kuwa kusan zuciyoyin masu boyem ne dika aka hada guri daya da babu wanda bai bada nasa securities dinba akan matarsa musamman NUAB da wasu manyan murdaddun securities aleey ya bayar,
Sultan ma ya bada securities ga ayanah duk da yasan na NUAB ya ishesu,
Shi kansa Asim bai nutsuba saida ya bada securities biyu wa tasa matar hakama Zuhrah kusan bayi biyar zata dasu daga bangarenta bayan wainda suke acan anjom da aka tanada masu yawa da tsari da sanin komai na aikinsu.
Motocin suka shiga dan zuwa airport,
Aleey ne ya iso da motar da NUAB kadai ne yake shigarta tasa ce ta hawansa ya kara a gaban bahar da kansa ya tuqota ba kowane driver ba,
Ko ubangidansa baya tuqawa sbd akwai drivern NUAB din da dashi suka taho tun daga Moscow amma ayau NUAB shi ya bawa umarnin ya tabbatarda isar dasu Airport da kansa dan hakane ma ya zabi daukanta da kan nasa dan tabbatuwar hakan ya faru.
Ammi motar tata mijin da aka bude mata ta shiga batareda ta shiga ta Aleey ba daya fito ya bude musu kofar.
Bahar ce ta saka kafarta a natse ta shiga motar ya rufe yana komawa ya shiga ya tada sukabi bayan sauran motocin a natse suka fice daga masarautar boyem.
Ko da suka isa airport ba sautan time sozai dan haka kai tsaye wucewa sukai ciki suna duba time wanda Allah yasa basu wani bata lokaci ba jirginsu ya daga qasar.
***Tafiyan wuni guda sukai me kafin duka sauka a inda duk gajiyansu basu tsaya sun kwana ba haka suka dauki hanya da wata sabuwar private bus data da komai da suke buqata a ciki suka wuce Anjom nanma motocin securities dinsu na biye dasu da wani irin tsaro.
Tinda suka kama hanyar da dukansu sukaga bata ruwa bace mamaki da shakku masu karfi suka rufesu musamman ganin hanyar titi ce suke bi wanda yake sabo a bayyane bawai tsohon aiki ba da alama kenan an bude hanyar zuwa garinsu ba dole saita hanyar ruwa ba.
Ga mamakinsu hadda motocin kasuwa dake tafiya wasu kuma fitowa daga hanyar garin tareda mashin mashin harma da masu tafiya a qafa jefi jefi wanda yeke nuni da hanyar zuwa garin jamaa sosai ne suke kokuma garin kasuwanci.
Kasa mahana kowacensu tayi suka zuba idanuwansu suna bi da kallan ikon Allah da mamaki da farin ciki duka a zuciyoyinsu lokaci daya.
Symbol suka gani shima babba dayake dauke da sunan garinsu baro baro hade da sunan masarautar garin ta ahalinsu wato ANJOM GHAZ.
Bahar kanta farin cikine takeyi sosai ganin garinta da mahaifinta ya dawo cikakken gari a yanzu abinda Abaa dinta yaso Allah bai basa damar cika wannan burinba gashi bayan ransa an samu cika hakan.
Basu sake shiga mamaki ba saida suka iso cikin garin wanda yake garin gaske ayanzu hakama manyan shaguna da malls malls da manyan gurare daban daban hakama ga wutan lantarki.
Baban ginin dayafi kowane gini a garin suka tsaya mai hawa biyu da wani irin girman gaske gate har mataki biyu da securities da fadawan da aka dauka aiki aka qara da securities da tarin bayin hidima suka tsaya ginin na dauke da sunan GHAZ Empire acan sama da manyan baqaqe na kalan zinari yana daukan ido da haskawa.
Bude musu gate din farko akai suka shige aka rufe suka isa gate na biyu aka budesa shima motar ta shige sauran motar securities kuwa a harabar gate din farko ta tsaya tareda bayin da suka taho dasu sedai su suka isa da kafa zuwa ciki bayin.
Su kuwa ana parking a babban harabar gurin da girmansa yayi yawan da zai dauki motoci fiye da takwas a bakin babbar kofar shiga main entrance ta farko wadda kana shigarta bangarora ke kashi kashi da suke a tsare cikin wani irin kyakkawan gini da tsarin zamani na turawa da daula aka tsaya dasu aka bude motar suka fito.
Suna fitowa bayin dake jere suna jiran isowansu kansu a qasa suka fara musu barka da sauka cikeda girmamawa kafin suka fara daukan kayansu a natse suna wucewa ciki dasu.
Shigowa sukai wanda tin daga nan babbar jakadiyar gidan datake bada umarni ga bayi itace tayiwa kowa iso bangarensa da babu bangaren da babu duniyar jin dadi a cikinta.
Bangaren Ayanaah shine bangaren mafi girman gaske wanda yake dauke da dakuna kusan guda biyar da palo uku sai toilet a kowane daki da kitchen da dining room me girma da babu luxury dun da baa zuba ba.
Bayan bangaren Ayanah sai bangaren da Sakinah zata zauna wanda yake komai iri daya dana ayanah sedai ita 3 bedrooms ne da palos guda biyu da babban master bedroom mai hade da palo,
Bangaren Zuhrah ma irin hakan ne saina Bahar wanda yake shima iri daya sak sai babban bangaren da aka ware can gate din farko akai hadaddiya wadatacciyar fada me tsari datake dauke da offices kusan guda biyar masu tsari da kuma babban dakin taro maana meeting da sauransu.
Acan baya kuma bangaren bayi ne da maaikatan gidan da kuma bangare daya daban dakin securities dinsu ne a jere da suma daidai gwargwado ba abinda babu.
A jikin bangaren Ammi wani lafiyayyan bangaren da Sultan zai zauna yake wanda yake tamkar shine bangaren da daace Abaas yana raye zai zauna sbd shine na namijin gidan,
Akwai palon daya hada bangaren dana Ammi wanda ta cikinsa kawai zata fada bangarensa hankali kwance.
A bisa tsarin ginin asalin iya jinin GHAZ din akai ginin aka warewa kowa bangarensa kaman rabon gado,
Ayanah,zuhrah da bahar wadda ita kadaice a cikin yaya take asalin jinin ghaz sbd mahaifinta ne ita bawai mahaifiyarta ba kaman yanda su su NUAB da leylah sedai ace jinin boyem ne su.
Sakinah ta zama jinin ghaz kaman yanda suke fada dan hakanne akai gunin da ita wanda koda aure ko ba aure tanada bangaren data mallaka a cikin masarautar ghaz da itace asalinta yanxu.
#MAMUH
09033181070 HAYATEEM
Mamuhgee
167
A bangaren Ammi dukansu suka sauka banda zuhrah data sauka nata bangaren da bayinta da tini suka fara aikin jera