Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   91 / 100

270K to 273K   out of 299.8K words

kayanta a wardrobe suna sake gyara komai daidai da yanda tsarinta yakeso.

Suma a bangaren Ammin Dakin Ammin shine a kurya me hade da palo me tsari sai sauran bedrooms din a jere a hallway saina maa tenya a main babban palo wanda hake hade da qaramin palo a cikinsa shima sbd itace zata zauna din din shiyasa nata yake hade da palonta dan haka nasu dakunan basuda palo.

Akwai gajiya me tsananin gaske a tattare dasu dan haka kowa daki ya shige dan rage gajiya da ibada.

Wanka da ruwan zafi tayi masu cire gajiya,
Tara ruwan ma tasaka Naimah tayi mata a bathtub kafin taxo ta shiga tana rufe idanuwa sbd ratsata da ruwan sukai suna fara rage gajiyan datake ji musamman kafafunta da suka dan kumbura kadan sbd zama.

Wanka tayi sosai a natse bayan ta gasa jikinta tukuna tai brush da sabbin komai da aka jere musu na buqata a toilet dinsu komai a kwai.

Tana fitowa sama sama tayi shirin ta saka riga da wando masu kauri da hula ta saka doguwar riga akai tayi sallar asuba da akai suna hanyar anjom din.

Tana idarwa tea me zafi ta saka aka kawo mata har daki sika hado da cake me laushin gaske sabo da akai tinda uwar asubar,
Tas ta shanye tea din kafin taci cake din daya tasha ruwa kafan ta kwanta tana shigewa barko tareda kashe wutar dakin ta qarawa ac din karfi kadan take bacci me karfin gaske ya rufeta sbd ko gani batayi sosai sbd baccin.

Kusan kowama hakan yayi ya kwanta dan suna cikin gajiya matiqa.

Kasancewan masu anjom suna gidan ya saka kowace motsi me hayaniya ya dauke a gidan sbd a basu daman hutawa dakyau.

Babu wanda ya farko ko fito a cikinsu sai bayan karfe daya kusan ma biyu,

Sallah da wanka ta sake yi sai a lokacin ta janyo wayarta tana kunnawa tareda kunna wifi na gidan sbd basuda layikan qasar dole iya wifi zasuyi amfani dashi suyi amfani dasu WhatsApp da sauransu.

Password din aka kawo mata daki ta saka take sakonsa kuwa ya shigo wanda tana gama karantawa murmushi me sanyi ta sake tana lumshe idanuwanta sbd tafar jin kewansa me tsanani a yanzu da basama qasa daya.

Kiransa ta saka ta WhatsApp yana dauka a natse cikin wani irin sanyi suka sauke ajiyan zuciya tare tana qarawa da murmushi me sautin daya shiga kunnuwansa ya sakasa sake lumshe fararen idanuwansa yana ambatar cikakken sunanta cikin nutsuwan da itama saida tsigar jikinta ta tashi ta bude baki daqyar ta amsa tana gaidasa cikin basa girmansa na miji kuma sultan.

Yanda tayi gaisuwan ya sakasa fidda wani murmushi me nutsuwa yana amsawa tareda fara binta da tambayan hanya da gajiya da baqunta da kuma missing nasa.

Amsa masa tai duka a kasalance tana fada masa missing kuwa tanajin kaman idan ta dade batama gansa ba Amminta bazata sake gane lafiyanta ba.

Murmushi me sautin nutsuwa ya sake sakewa yana jin kalman tata har cikin kwakwalwansa yace

'GHAZs princess kada ki janyo aikin da bazaki iyaba fa sbd Anjom bata da nisa gareni matiqar kina can'

Itama murmushin ta sake tana cewa

'Hmmn anan dai ai ko kazo ko masaukinka bamada'

Murmushi kawai ya sake bai bata amsar maganar ba sbd shida yakeda mata da uwa a gari a masarauta ai zancenta neman magana ne kawai.

Fira suka cigaba dayi a natse a kasalance har tsawon lokaci ba hayaniya ba daga murya har suka gama tukuna ta ajiye wayarta tana fitowa tabar leylah na shiga wanka dan ko anan a daki daya suke yanxu da suka saba.

A palo ta tadda su Ammi duka sun fito kusan kowa waya yakeyi banda maa sakinah datake dining tana sake gyara yanda tsarin abincin da ake jere musu a dining tana bada umarnin abubuwan da zasu kawo.

Gurin maa sakinah din ta nufa tana tayata aikin tana dan lafewa gefenta sbd sam tafara jin ta rasa me ke mata daidai.

Suna gamawa daidai su Ammi sun gama waya dan haka taje ta zauna gefen Ammi tana musu sannu da gajiyan hanya tana dan sake neman kokarin kwanciya.

Dining suka suka nufa dukansu suna zaunawa leylah nafitowa itama dan hakaa tare sukaci lafiyayyan abincin da aka cike dining dasu kusan kala uku.

Suna gamawa a palo suka zauna kowa da abimda yakeyi itada dai tana kwance lafe gefen Ammi jikinta yayi dumi kaman me shigar zazzabi Ammin na jinta tayi shiru tana shiga nazarinta sbd gabaki daya ta sauya da qananun ciwo da kasala.

Batai mata tinanin komaiba musamman ciki sbd batajin tayi haduwa sosai da NUAB da zatai saurin samun ciki hakama yaushe rabon su ma da juna dan haka ta ringa mata fadan ta rage san jiki da yawan kwanciya.

Maa sakinah ce kadai tafara zargin akwai wani abu a jikin Bahar din sbd yanda ko cin abincinta ya sauya sam batason abinci sosai yanxu sai tea da abincin ruwa ruwa,

Maa tenya ma bata kawo tinanin komaiba sbd ta dauka abubuwan datake basu ne yake saka kasalan da yawan sauye sauyen appetite tinda yanawa wasu matan hakan.

Leylah ma maa sakinah na ankare da ita duk da ita kwata kwata laulayinta ya bace gabaki daya kawai cika take sake yi tana kiba.

*****kwanaki sikai suna hutawa dakyau sunje ziyarar bangaren kabarin iyaye da dan uwansu sunyo musu addua tareda fidda sadaka me yawa aka rabawa yan gari hakama sun fita sun zagayo gari sun dubo gari kuma gari ya dauki dawowan asalin masu garin dan haka ake jin tamkar haske da rahamar garin ta qarasa dawowa mutane sunyi farin ciki da murna sosai wasuma hadda kuka.

Su kuwa tinda suka dawo basu sake fita koina ba sbd yawo baya cikin dabiun jinin kowane dan sarauta kuma basu saba daman dan haka maa tenya bude aikinta tayi tafara cigaba dan ma bikin na sake matsowa.

Hidimarsu suka maida hankali suka fara sosai ta biki hankali kwance anata kashe dukiya me yawa da zama busy dan kuwa sosai aka fara gayyato mutane,

Ita kanta yayanta dukansu sun taho suna anjom sun iso da wuri kuma zasu kwana biyu suga mahaifiyarsu da kyau ko bayan bikin kafin su koma kuma kowa da hannu bibbiyu da kauna da sakewa aka tarbesu ba babbanci a tsakaninsu dasu Bahar dasu da yayansu yan mata da suka taho dasu duka dan haka gidan ya sake cika sosai da samun hayaniya.

Daga sultan har NUAB har Asim babu wanda a cikinsu baya cikin tsananin matsuwa da zuwan ranar daurin auren musamman Asim da baya komai bayan shirin barin boyem daya gama daga anjom bayajin zai dawo daga can zasu wuce da matarsa gaba dan haka ya zama busy sosai da kuma dagewa gurin cusawa mahaifiyarsa sabawa da rashinsa dan kuwa zamansa din baida amfani gwara tafiyar ya fara aiki ko wasu businesses din tinda nan a zaune yake zaman banza sbd babu jinin boyem dazai taba aiki a wani guri cikin qasar boyem hakama a cikin masarautar ma bazai taba samun aikin ba sbd NUAB ne me mulki hakama a yanzu da Kowa rayuwan aure zaiyi ya zabi yinta a wani gurin daban kawai da iyayensa daban dana NUAB da BAHAR.

Haile da har lokacin ta kasa yadda da 'danta barinta zaiyi hakama sultan barinta zaiyi zarewa tayi gabaki daya kwana takeyi kuka wuni takeyi baqin ciki da qunci,

Umarni da duk wani tashin hankalinta bai saka Asim ya janye barin boyem ba wanda dan haka ta koma roko da magiya amma ya kasa fasawa sbd wasu manyan dalilinsa da bai bude mata ba amma hakan shine mafi daidai kuma yana shirye da tafiya da ita dan itama ta samu sauyin guri ta samu salamar zuciya idan zata yadda da hakan amma sam taqi yadda haukacewa kawai take neman yi takai har cikin baccinta take ambatar sunan Ayanah ghaz tana maimaitawa tana hawaye.

Sultan ma ya zaunar da ita ya sake sanar da ita tafiyarsa wadda ta sakata rasa dukkanin sauran hankalinta musamman dayake fada mata zai jima kafin ya dawo hakama idan ya dawo nan din itama zai jima mata kafin ya sake komawa anjom.

Kaman daga sama yana gama fada mata maganar ta bude baki tana kallansa da idanuwanta da suka bushe jajir tace

'Sultan dan Allah ka saki ayanah ghaz ka barta tinda ta riga ta koma qasarta,
Zaka iya mun hakan ni mahaifiyar 'yayanka??
Kaman zan mutu nakeji,zuciyata zata buga,baqin ciki da qunci zai kasheni'

Kallanta ya tsayar da idanuwansa yanayi a natse cikin nazarin yanayinta daya fara kamata ya karanta dakyau kafin komai sbd tabbatarda lafiyarta kalau.

Ganin alamu sun nuna kalau take ya dauke idanuwansa daga kanta yana ajiye wayarsa gefensa ya bude bakinsa yace ta tafi kawai.

Sake maimaita abinda ta fada masa tayi tana kallansa idanuwanta na sake ja

Bude baki yayi yace

'Kije kiyi hakuri bazaki samu abinda kike fadan ba,
Bana auren mace na saketa a rayuwata musamman macen dana jarabtu kafin samu,babu abinda zai sameki ki cire damuwa ki danga duka quncinki zai yaye'

Yana gama fada mata hakan ya nuna mata kofar ficewa da hannunsa daya dan yana buqatan tafiyar tata dan yanda kalamanta suka sosa zuciyarsa dan bai taba tsammanin kai tsaye magana irin wannan daga gareta ba.

Bata iya cewa komaiba ta fice tana hadiye wani qullutu me nauyi da daci daga maqoshinta tana komawa bangarenta.

Wuni tayi a daki babu wanda ya sake ganinta hatta yayanta duk yawonsu sun kasa ganinta tana daki ta rufe taqi fitowa.

Kasa nutsuwa hankalinsu yayi suka ringa jin damuwa dan haka suka zauna jigum jigum gashi Asim ma bayanan ya fita tin safe yana wajen masarautar ma.

Sai dare ta bude kofar dakin ta fito
Ga mamakinsu tayi wanka tayi shirinta tsaf ta kira babbar baiwarta ta sakata ta dafa mata shayin sultan zataje tiraka yau din.

Aslam na jin hakan ta miqe taje ta karba aikin ta dafa masa da kanta ta shirya komai tana farin cikin dawowan mamin tasu daidai dik da ba doguwan walwala a fuskanta kaman ma ta gama saddakar da rayuwa meryam ke gani a tareda ita din.
##MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

168
Aslam na gama hadawa ta kawo ta ajiyesa yana shirye a cikin wasu lafiyayyun tea set masu kyan gaske sabbi harma da dabino da zuma masu kyau duka ta jere ta ajiyewa Mamin wadda tace su tafi kawai idan ta gama abinda take zata kai masa.

Karfe goma sha daya ta baro bangarenta ta isa bangaren sultan din ita kadai sai baiwarta daya data dauko mata kayan suna isowa ta karba ta shige kadir ma dayaga zuwanta tini yabar bangaren ya tafiyarsa bangarensa saida safe kuma.

Ko data shiga sultan din ya gama komai na shirin bacci yana zaune dakin ba haske sosai yana waya a natse cikin kamala da kwanciyan hankali da Ayanah ghaz wadda take jin nutsuwan wayan dashi itama.

Haile daga fahimci da waye yake wayar wani abun ya sake zuwa ya danne maqoshinta amma kuma tinawa da daga yau baqin cikinta ya qare ya sakata ajiye kayan hannunta a kan table din gabansa tana bude baki tayi magana wadda ta sauka kai tsaye a cikin kunnuwan Ayanah.

Wani iri Ayanaah din taji musamman data kalli lokaci sai kawai taji kirjinta yayi nauyi itama da wani kishinsa me sanyi amma kuma tasan basu kyautaba sbd daga yanzu tasan matiqar yana boyem daidai irin wannan lokacin to na matansa dan haka cikin nutsuwa tai nasa saida safe bata jira amsarsa ba ta kashe wayar tana ajiyewa a gefenta tareda sauke numfashi me sanyi tana hana kanta jin komai.

Shima acan bangaren baiji komaiba sbd hailen dan haka ajiye wayar yayi gefensa yana kallanta a natse.

Zaunawa tayi gefensa gap dashi sosai tana dagowa ta bude baki cikin bayyanarda nadama ta basa hakurin abinda ta fada a dazun.

Sai a lokacin yaji tausayinta me yawa ya shigesa da ratsasa musamman da ramarta da figewanta duka suka bayyanar masa ya kafeta da ido yana jin inama zai iya fada mata nasiha taji ta dauka akan bazai taba wulaqantata ba ko tozartata akan aurensa kodan darajar shekarun da sukai tare da manyan yayansu dake tsakaninsu amma yasan babu abinda zai fada mata taji bare yadda wanda dazatai hakan data samu nutsuwa da kwanciyan hankali tareda zaman lafiya.

Numfashi ya sauke yana karban banhakurinta tareda miqa hannu ya karbi tea din datake miqo masa yana mata godia kadan a natse yakai bakinsa ya bude yafara sha duk da baya buqatansa dan bai jima da gama sha ba amma sbd ya bata nutsuwa da kwanciyan hankali sai yasha din.

Idanuwanta cikowa suka fara yi da hawaye masu tsananin radadi da quna tareda dacin shedar da wannan rana wanda shine ya janyo musu wannan kaddarar.

Tana kallo ya ringa sha ahankali harya shanye rabi ya ajiye a natse tareda dawowa da bayansa yana jingina ya kalleta hawaye na gangarowa daga idanuwanta mamaki ya kamasa bude baki zaiyi magana ta taresa dukkanin imaninta na barin kirjinta ta share hawayenta tana kallansa itama dakyau ta bude baki tace

'Meyasa ka zabi ayanah ghaz akan kowace mace Sultan??
Meyasa ka lalata rayuwan mata da yawa da basada adadi ka qare akan ayanah ghaz?
Meyasa se ayanah ghaz?
Baiwa ce qanqantacciya,imebēti ce macen da ake kwanciya da ita dan biyan buqata,wishmah ma data zama batai darajar mu da muke da aurenka akanmu,
Meye ne jinin ghaz suke dashi da kowa yake sonsu yake mutuwa akansu?
Menene a jininsu bayan mummunan kaddara da baqar rayuwa,
Meyasa zuciyarka bata iya bani soyayyarta ba bayan shekarun da mukai a tare muka tara yaya sai akan baiwar datake ragin kusrawa.....

Rufe idanuwansa yayi a natse kalmarta ta qarshe tana yiwa zuciyarsa yanka me karfin da idanuwansa suka sauya hadda fuskansa sbd radadin yankan,

Bude idanuwansa yayi batareda ya kalleta ba sbd gabaki daya jin yayi babu abinda ya tsana a daidai wannan lokacin bayan iya kallanta dan haka baice komaiba wayarsa ya daga ya saka kiran Asim sbd yace yaxo ya tafi da mahaifiyarsa dan da alama akwai matsala me girma a cikin kwakwalwanta,
Bazai tankawa kowace irin haukanta ba kaman yanda bazai iya cigaba da saurara ba dan haka gwara danta yaxo ya tafi da ita salin alin.

Koda kiran ya fara shiga wayar Asim a lokacin Asim din ya dawo yana tsaye kofar office din NUAB zai shiga a karan farko da zasu fuskanci juna sbd tafiyarsa tagama kammaluwa stamp na sultan din boyem na yaddar barin boyem a matsayinsa na jinin boyem yake nema kadai a takardarsa ta li'uli Asim ya sakasa zuwa dan haka tin safe ya sanar da Aleey a waya cewan ya sanar da Sultan LEUL din yana son ganinsa ba bata lokaci kuwa cikin girmamawa Aleey din ya amsa da yes ya kuma isar da sakon ga NUAB wanda yace koyaushe Asim din ya tashi free yake da zuwa ganinsa ba shamaki.

Bayan aleey ya sanar dashi godia kawai yayi bai samu zuwa ba sbd bai zauna ba sai daren ya kira yaji har lokacin NUAB yana office shiyasa ya fito yazo sbd gobe tinda safe zai bar boyem ya fara wucewa amma ba anjom ba sai antashi daurin auren zai tafi anjom daga can ya wuce da iyalinsa dan ita ma komai na tafiyanta ya mata.

Shigowan kiran sultan yayi daidai da zai shiga office din Aleey na tareda shi cikin sakewa da girmamawa dan haka daga wayar yake kokarin yi a natse da mamakin ganin kiran Sultan a lokacinda baa taba kiran kowa dan idan dare yayi irin hakan baa kiransa baya kira shima.

Yankewan kiran ya sakasa dakatawa yana sake shiga mamaki kafin ya saka kiran wanda tafara ringing amma ba alaman zai dauka.

Acan kuwa haile na lura da kira ya saka ta saka hannuwanta biyu ta fizge wayar tana ja da baya wanda zuwa lokacin ransa da zuciyarsa sun gama zuwa sama gabaki daya da bacin rai idanuwansa ya dago jajir da zallan bacin rai me tsananin gaske ya kalleta ya bude baki zaiyi magana jini yafara fitowa daga hancinsa a hankali wanda ya sakasa kallan gaban rigarsa daya fara diga ahankali.

Dagowa yayi a hankali ya kalleta itama shi take kalla tana ji wayarsa na ringing a hannunta ta daga wayar ta buga da qasa da karfi take wayar ta watse.

Miqewa yayi tsaye tareda daga hannu zai kamota cikin tsananin bacin rai da zafin zuciya amma ko taku biyu baiyiba kafafunsa sukai wata irin majirya me karfi suna sanqarewa tareda sarewa suka daki qasa da karfi hannunsa daya daga ya sanqame shima yana wata irin rawa da qamewa jinin dake fitowa hancinsa ya qaru da karfi yana fitowa sosai bakinsa kuwa kumfa mara kyan gani dake hade da jini yake fitarwa.

Zubewa yayi a gurin duk yanda yaso karfin halin dayake jininsa gangar jikinsa kasawa tayi sbd tsananin karfi da kaifin poison din take kalar jikinsa ma tafara sauyawa tana duhu jinin na tsananta fitar masa.

Tsaye take tana kallansa zuciyarta da idanuwanta a rufe buri da fatarta kawai ransa ya fita yabar jikinsa Ayanah ghaz ta rasashi kaman yanda suma suka rasashi hakama shima ya rasa ayanah ghaz ta hanyar barin duniya kaman yanda ya zabeta akan komai da kowa.

Jajir idanuwanta sukai hannuwanta na rawa ta qanqamesu sosai tana kafe dashi da ido batareda fargaba ko shakkar a kamata ba indai ya mutu ta yadda a kamata dan koda baa kamata ba indai yana raye mutuwan baqin ciki da wulaqanta zatai a banza gwara tasan ta cika burinta na ganin mutuwansa kafin ta mutun.

Asim dayake kiran wayar tana dena shiga jin yayi hankalinsa ya fara kasuwa kashi biyu yana shiga shakka.

Aleey daya fahimci hakan shima suna shiga office din fitowa yayi ya saka kiran kadir ya sanar dashi Sultan ya kira Asim amma kiran ya dena tafiya kuma hankalin Asim din ya rabu biyu ta yanda bazai iya nutsuwa yayi magana da ubangidansa ba dan haka a dubo ko da akwai yiyuwan sultan na neman Asim dinne saiya je ya fara ganin sultan din kafin NUAB sbd sam bai hada duk wanda zai tsayu a gaban Nasa sultan dinba da komai.

Yana gama wayar ciki ya shigo a natse yana kallan Asim da duk yanda yaso tsaida hankalinsa guri daya a gaban NUAB kasawa yayi musamman gashi ba sabo ko kusanci ko qanqani a tsakaninsu hasalima sai ayau suke tsayuwa a gaban juna face to face haka iya su kadai zasuyi magana,magana wadda bata komaiba saita fahimta da nutsuwa da bawa jinin dayake tsakaninsu mahimmanci.

Qarasowa Aleey yayi ya tsaya gefen Asim din cikin nutsuwa yace

'Kadir zai dubo Sultan idan nemanka

91 / 100