Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   17 / 100

48K to 51K   out of 299.8K words

macen da zata fi HAILE komai da samun gurbi a zuciya da ahalin sultan,

A tarihi da doka tareda qaida mai girma a Masarautar BOYEM baa taba auren wadda ba jinin BOYEM ba,
Babu macen data taba Matar Sarkin Boyem matiqar ba jinin sarautar BOYEM bace,

Duk yanda mace ta shiga ta mamaye zuciyar Sarkin Boyem komai tsananin so da kaunar dayake mata fiye da matansa matsayinta yana tsayawa ne a iya WISHMAH wato lady mistress ita ta wuce matsayin imebēti hakama bata zama matarsa ta aure ba amma kuma matsayinta daya da matansa a duniya a zuciyarsa kuma tama fi matan matsayi,

Dan haka a koyaushe burin da tenya take kwana dashi take tashi tayi rayuwa dashi shine ta tabbatarda ta samar da wishmah a BOYEM din yanzu wadda zata ruguza power din HAILE koba duka kwata kwata ba to ta tabata sosai dan babu macen datai darajar HAILE a qasar BOYEM yanzu sbd itace mata kuma uwargidan sultan YASAR haka kuma macen datafi kowace macen kyau da iko a qasar.

Duk da Ayanah baiwa ce wadda bauta ta sauya mata abubuwa da dama ita ta hango asalin sirrin kyanta Wanda zai fito fiyeda na HAILE idan ta samu gyara da hutun da fata da gangar jikinta suke buqata ga wata irin sanyi da nutsuwa a tattare da ita wanda zai iya sanyaya zuciya mai Zafin gaske irin ta sultan jinin masu BOYEM da kansu dan haka Ayanah tayi mata tako Ina kuma taci burin fiddo da dukkanin kyanta da kwarjininta da bauta ta boye zata fiddota a matsayin sabuwar wishmah ta BOYEM da aka shide qarnika baa samu ba sbd yawancin sarakunan BOYEM basa soyayya dan bata tsarinsu Sarkin uku ne kadai suka taba wishmah Sai a yanzu datake fatan hakan ga sultan YASAR.

Umarni ta bada aka tada Ayanah Zaune wadda take kwance kaman babu inda baya aiki a jikinta,

Sakinah ce ta saka mata pillows biyu a bayanta suka tareta aka fara bata maganin masu dumi da wani qamshin nutsuwan dayake ratsa hancinta zuwa cikinta,

Gabaki dayansa aka sakata shanyewa kafin suka ajiye cup din akan tray din da aka jero cup da bowl din Dayan maganin masu kyau.

Dayan maganin aka Dora mata a baki yafara shiga maqoshinta ta rufe idanuwanta ahankali tana Jin taste din maganin na ratsa bakinta aka buga kofar dakin da nutsuwa Wanda ya saka dukansu kallan kofar Banda Ayanah din dake Jin zuciyarta na Wani irin nauyi ta sake rintse ido.

Da ido tenya ta basu umarnin su bude dakin dan haka daya daga cikin bayinta ta juya ta nufi kofar dakin a natse ta bude Kai tsaye tana kallan wadda ta bude dakin kanta a qasa ta bude baki da taushin murya tace

‘Daya daga cikin sabbin imebētin da zaayi ta illata kanta harma tana gap da rasa ranta amma…….

Wani irin fesowa abinda yake cikin bakin Ayanaah yayi da karfin gaske idanuwanta na budewa jajir sbd abinda taji Wanda zuciyarta ta tabbatar mata da Zuhrah ce,

Wata irin rawa hannuwanta da kafafunta suka fara ta yunqura da karfin gaske tana Miqewa tsaye harshenta karyewa sbd mummunan tashin hankali ko magana ta kasa sai idanuwanta dake rikidewa jajir b Kyan gani………

Sakinah ma da jikinta ya dauki wata irin rawar tashin hankali saurin dafe Ayanah itama tana Jin tabbacin Zuhrah ce dan haka hawaye suka fara ciko idanuwanta sbd Zuhrah tayi hakan ne sbd yar uwarta Ayanaah…

Ayanah fizge wa tayi daga riqon Sakinah tana Miqewa jiri mai karfi na dibarta tabi bayan su tenya da suka fice dakin batareda sunsan halinda Ayanah din ta shiga ba.

Ko ganin gabanta Ayanaah batayi jiri na dibarta na maganin da aka bata Wanda karfinsa yake dan bugarwa sbd na gyaran mace ne,

Wani dishi dishi take gani a idanuwanta da duhu duhu amma a hakan take jefa kafarta duk inda ta samu ta nufi hanyar da Batama San Ina zata samu Zuhrah dinba,

Sakinah d gudu taje biye da ita tanason ambatar sunanta amma ta kasa sbd kada wani ya jisu asan sun fito komai y qarasa lalacewa dan haka biye take da ita tana wasu irin hawayen tausayi da tashin hankali tareda baqin ciki tana kokarin kamata amma Ayanaah dinba taqi Bari fizge wa takeyi sbd ko zata rasa ranta Ayau sai taje ga yar uwarta.

Ragaita Ayanaah din ta ringa yi tana zagayen Neman inda Zuhrah taje amma koina tsit babu Zuhrah ta zube a tsakiyar gurin qasa tareda dafe kirjinta dake mata Wani irin azababben radadi ta fasa wani irin kuka mai karfi da taba zuciyata tareda ambatar sunan Zuhrah da karfi tana sake dafe kirjinta dake Neman bugawa da sauri sakinah ta zube qasa din itama tana rufe mata baki da hannuwanta biyu tana kukan itama mara sauti jikinsu na rawa su dukan,

Kuka sosai Ayanaah keyi mai tsananin karfin sautin gaske amma Sakinta ta riqeta jikinta da karfi ta toshe mata baki sautin kukan baya fita sbd idan batai hakanba koina zai amsa karar kukan nata Wanda takeyi d karfin gaske tana ambatar sunan Zuhrah.

Motsin tahowa suka Ji Wanda ya saka sakina janta da karfi cikin tausayawa ta boye bayan wani dakin da ita har lokacin riqe take da ita bakinta a toshe.

Zuhrah ce aka dauko tamkar gawa a kan wani qaramin gadon marasa lafiya koina jikinta ba Kyan gani jininta ne yake fita sosai Wanda ya sauya kamanninta dana Kayan dake jikinta,

Babu alaman rai a jikinta idanuwanta a rufe hannuwanta a sake Mutum hudu ne maza dauke da ita jini na bin hannuwanta zuwa yatsar hannunta yana diga qasa,

Tenya ce ta bude baki Kai tsaye cikin iko da bada umarni mai Zafin gaske tace

‘A kaita kurkukun bauta da ukubar da bayi acan zatai jinya t warke tayi rayuwa har qarshen rayuwarta bazata taba fitowa ko wuya ta dauki ranta ko kadaici da ukuba wannan shine hukuncinta……

Wani irin Juyawa duniya tayi da Ayanaah wadda ta bude baki da karfin gaske ta fasa Ihun kiran Zuhrah cikin rikitaccen kukan daya saka sakinah sake saka karfinta duka tana danneta tareda rufe bakinta d karfin gaske itama tana hana nata Ihun gunjin kukan fidda sauti.

Fizge fizge Ayanah keyi tana dukan hannuwan sakinah son qwacewa ta tafi ga Zuhrah kome zaayi musu Ayi tare amma Sam sakinah ta saka karfi sosai ta danneta da gaske sbd tana fita dukansu su ukun rasa rayuwarsu zasuyi dan haka dole ta hana Ayanah dan yanzu ita da zata zama imebēti itace hope dinsu harma dana fiddo Zuhrah cikin wannan mummunan hukuncin na qarshen rayuwa.

Gap da su aka kawo Ana wucewa fuskan Zuhrah dake jina jina da jini tana fuskantar saitinsu idanunwata a rufe Wanda ya saka zuciyar Ayanah kasa dauka ta daga hannu tana miqawa zuciyarta na rage bugawa tana sake kokarin fizgewa tana ihu sosai a zare amma Sam babu sauki a riqon da akai mata tana kallo har aka bace da Zuhrah zuwa inda bazata sake ganinta ba har karshen rayuwarsu kila.

Wata irin jijjiga takeyi tana Ihun Wanda har jikinta ya fara sakewa ahankali ta some a jikin sakinah din gaba daya numfashinta na tsayawa.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali*_HAYATEEM_*
Mamuhgee

29
*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Bononza bononza
Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka
Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah
-Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani,
-Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba,
wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online
Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare
Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah
Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma,
Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take
Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k
Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k.
Zuzeam ventures
08144015291

*******
Cikin tsananin sabon tashin hankali da tsananin tausayin Ayanah dake kashe duka jiki da zuciyarta ta fara girgiza Ayanah din da dan karfi tana ambatar sunanta da sauti qasa qasa amma ba alaman Ayanah din zata motsa ko alamar akwai Sauran rai a jikinta dan haka da sauri ta saka qarfinta ta daukota a bayanta tana waiwayen hanya dan gudun a Gansu ta ringa bin bango a tsorace da firgici ta koma har dakinsu ta fada gado da ita tana sauke wani wahalallen numfashin gajiya da tsoro da firgici,

jikinta na rawa ta miqe tazo kofa ta rufe da sauri hadda saka keyi kafin ta dawo inda Ayanaah din tana sake girgiza ta tana ambatar sunanta da sauti mai bayyanar da tsoronta na rasa Ayanah din ga kuma tausayin Zuhrah dake sake sako mata kukan daya kasa ma fitowa zuwa lokacin sedai jan ido da rawar jiki,

Ruwa ta dauko hannuwanta na rawa ta zubawa Ayanaah din wadda bata motsa ba saida ta zuba mata ruwa sosai tukuna ta motsa kadan idanuwanta da sukai mummunan ja suna budewa ahankali ta saukewa sakinah su batareda ta kyafta ba ko motsawa tamkar gawar da baa shafe wa idanuwa ba,

Hawaye ne masu tsananin zafi suka gangarowa sakinah ta sunkuyar da kanta qasa tana dauke kallanta daga kan fuskan Ayanah da ko kyaftawa idanuwanta basu yi ba tana mata kallan da batasan na menene ba amma dai koma na menene tasan akwai kallan yanke kauna a cikinsa dan haka jikinta yayi sanyi hawayenta na tsananta gudu ta bude baki koina na jikinta na qara sanyi tace

‘Allah ne ya kaddaro muku hakan da gani har ke har Zuhrah babu Wanda zai iya sauya hakan,
Allah ya fini sanin dalilinsa na yin haka hakama yafi ki sani yafi Zuhrah sani harma da duka masarautar BOYEM din,
Ga dukan alama kaddararki ce ta sako mu halinda muke ciki sbd Allah ya riga kila ya kaddara tarayyarki da sultan YASAR Wanda matiqar akwai rabo a tsakaninku to shine yayi sanadin komai daya faru dan zuwanmu nan,
Komai daya faru ya samu yan uwa da iyayenki ki yadda da rabo mai karfin dayake tsakaninku ke kila ya haddaso hakan dan haka ko a yanzu rabon ke dince ya saka yar uwarki sadaukar da rayuwarta sbd bazata iya qazantar dake shirin shiga tsakaninku ba ta hada shimfida daya da Mutum daya ku haifa masa yaya ku hada yayanku uba daya Kina raye tana raye,

Kinyi kokarin daukan taki rayuwan Amma Allah ya Hana hakan sbd kece wadda kila ya kaddarowa hakan,

A yanzu Zuhrah ta Riga takai karshen tata kaddarar kila dan kuwa har abada mutuwarta ce kadai zata fiddo da ita inda aka kaita waton gawarta ce kadai zata fito idan zaa rufeta kenan,

Tsananin so da kaunar da kike mata da saka rayuwarki a halakar da zaku rasa Ranku gabaki daya bazai taba sauya kaddar datake boye a cikin wannan lamarin ba,

Lokaci yayi da zaki rungumi kaddarar da gaske AYANAH GHAZ,
Zamtowanki imebēti ki haifi jinin BOYEM ko mace ko namiji shine zai baki hope na koba yanzu ba zaki fitar da yar uwarki daga wannan ukubar data Riga ta shiga sai mutuwa,
Zamtowanki cikakkiyar imebētin sultan YASAR BOYEM shine gatan da zakiyi wa yar uwarki da komai dade wa bazata cire rai daga samun ceto daga gareki ba dan kuwa tayi abinda tayi dinne dan ke ki samu zama imebētin ke kadai bada ita ba dan tasan zaki taimaka mata daga lokacinda kika samu daman tashi daga baiwa hakama matiqar kika zama imebētin kika tashi daga baiwa ko ba yanzu ba Kinada Sauran saka ran samun yancin Neman dan uwanki Abaas da shima matiqar yana raye yasan indai Kina raye wata ran Zaki iya nemansa,

Ke kadai kika raye a GHAZ wadda yan uwanki suka Dogara dake dan Allah Nima Ayau Ina rokonki ki jure ki daure ki rayu ko dan yan uwanki Dani kaina…….

Wani irin kuka mai tsananin ratsa zuciya ne sakinar ta sake tana sake sunkuyar da Kai tace

‘Matiqar kika jure kikai sadaukarwa tabbas ranar da zaki fiddo yar uwarki zata zo harma Kuyi rayuwa a tare idan bazaki iyaba ki daure ki iya kiyi sadaukarwar da yar uwarki tayi ki jure kiyi yaqi da komai ki ceto yar uwarki….’

Rufe idanuwa ahankali Ayanah tayi wasu hawaye masu dumin gaske suna gangarowa daga cikinsu batareda ta motsa ba har lokacin,

Shiru sakinah itama tayi hawayen na gangarowa daga cikin idonta babu Wanda ya sake motsawa a cikinsu hawayen Ayanah takeyi sosai hatta gashin jikinta sun kwanta gabaki daya tamkar sun mace,

Babu Sauran rayuwar data rage mata a yanzu da batada kowa a rayuwarta bayan sakinah,

Dukkanin kuzari,farin ciki,ruhi da bugun zuciya da hasken idanuwanta an rabata dasu babu ko daya a tattare da ita dan haka babu Sauran abinda ya raye komai na rayuwa bayan gangar jikinta da yanzu itama zata zama ba nata ba saina biyan buqatan wani Wanda zai watsar da ita ya manta ita da duk abinda ya rabata dashi ta zama fanko sauransa har qarshen rayuwarta,

Batada Sauran zabin daya wuce wannan din matiqar ranar da zata fiddo yar uwarta zatazo tabbas zata zama fankon ragi da Sauran wani din har karshen rayuwarta sbd daman babu abinda ya rage a rayuwan Bayan gangar jikin.

Hawayen ne suka cigaba da gangarowa gefen idanuwanta dake rufe batareda ta motsa ba har lokacin sedai sakinah ce ta saka farin qaramin handkerchief mai tsafta tana share mata hawayen ahankali suna saika Akan kyallen batareda ta sake cewa Ayanah din komaiba sbd ba abinda ya rage ma fada.

Shiru dakin yayi ko numfashinsu Baka Ji har tsawon Daren haka suka shafe sa cikin toshewan zuciya babu motsi,

Sallan asuba ce ta saka Ayanah din motsawa bata iya tsayuwa daidai ta miqe sakinah na riqe da ita har toilet.

Dukkaninsu sallah sukai suka ringa kuka mai tsima zuciya suna fadawa Allah damuwa da quncinsu har gari ya fara haske lokacin sakinah ta fice zuwa dakinsu tayo wanka ta sauyo uniform ta taho tafara aikinta ita kuwa Ayanaah na Zaune zuru ta kwantar da kanta a gwiwan kafafunta seti da window ta zubawa waje ido bata ko kyaftawa.

*********Ayau din aka taho aka kawo masu fara mata gyara ma Musamman Wanda zai qarasa dawo sa asalin kalar fatarta fara sol da gyaran fata da qamshi na musamman Wanda tinda masu gyaran suka iso bata iya cewa komai ba ko kuzarin komai duk yanda akai da ita tana Zaune babu gardama ko hayaniya ta zama tamkar Mutum mutumi dan haka suma suka zags sosai sukai aikinsu hankali kwance a natse,

Har kusan dare Ana abu daya da jikinta kafin suka tafi sai kuma gobe,

Washe gari ma haka suka taho sukai aikinsu suka tafi,

Tsimata akeyi cikinta da fatarta da asalin zallan madarar raqumi da lalle da zuma tareda wasu Hadi masu tsananin qamshin da hatta gashinta dayake Shan gyara qamshi yake fiddawa me sanyaya zuciya da kwantar da hankalin mai shaqa tareda basa nutsuwa da mutuwar jiki,

Sati guda akai Ana mata gyaran daya sauya kalarta da kamanninta asalin Ayanah dinta ta dawo sedai duk tsawon lokacin nan babu Wanda ya taba Jin koda muryanta sbd gabaki daya ko magana ta dena ido ne kadai se Numfashi ya rage mata sai kuma yanda akai da gangar jikinta ta sauya gabaki daya ko sakinah bata samun maganarta se dai ido kawai.

A cikin sati biyu tenya ta gama samun duka abinda takeson samu a gurin Ayanah na zama imebēti kafin zuwa wishmah dan kuwa hatta yatsun kafafun Ayanah dama hannunta abin kallo da daukan hankali ne sbd ta fito asalin balarabar ANJOM GHAZ dinta,

Haskenta da kyanta wani daukan ido yake yana fizgar hankali,
Qamshinta kuwa daya gama Kama kowane saqo na jikinta da gashinta tana tinkaroka zakaji qamshin asalin Larabawan BOYEM yana tashi a jikinta musamman idan tai motsi haka zakaji sa yana ratsa zuciya da gangar jikinka dan haka kwata kwata aka hana kowa ganinta bare Jin qamshinta bayan sakinah da ita kadai ce baiwar da tenya ta yadda ta Barwa hidimart sbd labarin Kyan Ayanah GHAZ na isa gurin HAILE zata iya yanke mata hukuncin Kisa Kai tsaye tin kafin sultan ya mallaketa a shimfidarsa dan haka tenya ta saka ido sosai da tsaro akan AYANAH GHAZ kaman yanda take kiranta kafin ta hau shimfidar sarki sunanta ya tashi daga hakan.

Tsaro sosai Ayanah GHAZ take samu daga tenya wadda daga qarshe dauketa tayi daga bangaren gabaki daya ta dawo da ita gurinta sbd barazanar datake ji a jikinta na kusanto Ayanah din sbd kyanta da yayi Wani irin yawan da itama idan ta kalleta Jin takeyi gabanta ma faduwa.

Dawowan Ayanah gurin tenya ya sakata sake shiga ran tenya sbd shirunta daya zamo tamkar nutsuwar datafi ta kowa data sani a rayuwarta hakama hakanan takejin a ranta Ayanah zata iya sauya musu kaddara dan yanda take Jin nacin son kasancewanta imebēti kota halin yaya dan haka ta matsu safiyar Washe garin ranar ta wanye dan sultan YASAR na kan jirgin sauka BOYEM Wanda a Daren goben ne zata isar da Ayanah shimfidarsa da insha Allah take masa fatar samun rabon haihuwa da ita.
#MAMUH

HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070

Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali*_HAYATEEM_*
Mamuhgee

30
*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Bononza bononza
Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka
Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah
-Da 5k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani,
-Da 10k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba,
wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online
Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare
Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah
Idan kinada 3k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma,
Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take
Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan

17 / 100