Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   51 / 100

150K to 153K   out of 299.8K words

yawa ta kudin dollars bayan tarin dukiyar dake bankunansa ya fito da shirin guduwa da Bahar a cikin daren bayan ya saka salman ya masa ready da komai na fita masarautar.

Kadir ayau yanayin da NUAB din yake ya sakasa kasa shiga sbd yau akwai babban almarin da zai iya zama me kyau ko mara kyau a tsakanin uba da 'da.

Da wata irin aura dake cike da zafaffan fushinsa da tafarfasan jininsa ya iso a cikin takun isa da Iko ya zauna a kujeran dake kallan mahaifinsa.

Kallansa sultan ya dago yayi a natse zaiyi magana NUAB ya dago nasa idanuwan da Babu rahama a cikinsu ko daya ya miqo hannunsa dayake dauke da zanen numbern mahaifiyarsa ta bauta ya Tarawa sultan din tareda kafe idanuwansa akansa ya Bude Baki da muryan data saka gashin jikin sultan gabaki daya miqewa yace

'zan tabbatarda baka Manta wannan ranar da burinka zai cika na shekaru,
Zan tabbatarda sai kayi Dana sanin sauka akan mulkin da nine zan hau'

Cikeda samun cikar tsofaffen burin da nauyinsa yake danne a kirjinsa na shekaru sultan ya ce

'ina maraba da hakan SULTAN NUAB ALMAZZ Mai boyem da GHAZ'

*****A daidai wannan lokacin ne su aleey sukai nasarar gane inda su Bahar din suke Dan haka Kai tsaye suka nufi bangaren da tarin securities da full loaded guns da suke a shirye da harbi tareda umarni me Karfi na kawar da duk wanda ya shiga gabansu,

Asim ma a wannan lokacin ya biyo duhun daren ya nufi inda su Bahar din suke da wata irin mummunar wuqar da zai kashe duka wainda suke bangaren Dan tafiya da ita ciki kuwa hadda Leylah baida niyar barin kowa Salman na tareda shi shima da wata muguwar takobi me muni a hannunsa.

Haile ma a wannan lokacin bangaren ta dosa tareda masu kakkarfan bayi biyu da zasu daukan mata ran Bahar kafin Asim yayi tinanin isa ta gama ta koma Dan hakan kadai zai saka ya dangana ya kama abinda yake gabansa.

A lokaci daya kusan dukansu suke kokarin isa bangaren wanda tin daga nesa securities din da sultan ya saka suka fara fitowa Dan bawa bangaren kariya da rayuwarsu su kuwa su aleey Kai tsaye suka Bude wuta kawai wanda ta saka gabaki daya masarautar daukan dirar fitar bullet din daya saka duniyar boyem daukan tsit ga haile da Asim duka suna cikin bangaren a gurare daban daban take kowannensu ya tsaya cak cikin mummunan tashin hankalin da baa saka masa rana ba kafafun haile na jiqewa da wani irin zufa kaman yanda kunnuwan asim ke tsiyayo wani zufan da bai san daga Ina yake fito masa ba sbd mummunan tashin hankalin da baida kama.

Wata irin kakkarfan sautin karar data karade gabaki daya ciki da wajen masarautar boyem tana ratsa cikin gari da qasar ne ya dakatar da komai da kowa dake boyem da zagayenta  cikeda firgicin da baa taba shiga ba sbd sauti ne na bayyanar da sabon sultan a karagar mulkin boyem me tarihin da duniya tasan dashi.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

90
Coming kunnuwan aleey sautin yake ratsawa yana tayar da kowace tsigar jikinsa yana sbd sanin LEUL dinsu ne kadai Wanda ya isa ya amshi mulkin sarautar boyem kaf duniya a lokacin,

Sauran yaran gabaki daya dauke wutar dasuke sakice sukai wadda take jijjiga har qasar masaurautar sbd duk inda kake a masarautar kana jin yanda qasa take amsa irin wutar da aka bude ana sakewa wanda ya saka duniyar boyem daukan tsit.

Duk inda kake a ciki da zagayen masarautar harma da garin gabaki daya sautin yakai maka na hawan sabon sultan a tsakar daren abinda baa taba yi ba a tarihi dan haka komai ya sake daukan tsit din da babu motsi,

Aleey ne ya fara kai gwiwowinsa a qasa daga inda yake tsaye cikin tsananin
Girmawansa ga sultan LEUL NUAB da matarsa dake cikin gaban inda suke tsaye,

Gabaki daya kowa zubewa yayi qasa ba iya su kadai ba kaf duk wanda yake masarautar zubewa kowa ya fara yi akan gwiwowinsa suna sadda kai qasa hatta manyan fada dake zaune cikin tsaka me wuyar gaske da zullumi me girma shigar sautin kunnuwansu ya saka kowannensu dagowa a cikin matsanancin tashin hankali da mummunan fargaban dayafi wanda suke ciki dan kuwa hawan sabon sultan da tsakiyar daren da babu wanda ya sani hakama ba sanin waye ya sakasu shiga zullumi me karfin gaske daya saka tashin hankalinsu komawa akan sultan din koma waye amma a haka suka zame qasa suna zubewa akan gwiwowinsu dan bada girmamawa me karfin gaske tsigar jikinsu na tashi da shigar sautin da babu karya a cikinsa zuwa cikin kunnuwansu.

Su kansu securities din da suke tsare dasu zubewan sukai tin daga fada har wajenta har securities dake gate na farko dana biyu dana uku dake wani irin kokari da gaggawan isowa ciki da nasu mahaukatan makaman sbd kukan bindigogi masu karfin gaske dake tashi a cikin masarautar saukar sautin ya saka kowannensu dakatawa daga inda yake yana zubewa qasa kawunansu a suna tabbatarda akwai abinda yake faruwa a cikin masaurautar dan haka sautin da mintinan da ake dakata komai dan bada cikakkiyar girmamawa suke jiran ya cika su fada inda ake bude wutar su bawa masarautar tsaro da kariya daga dukkanin abinda yake kolarin biyowa baya.

A daidai lokacinda sautin ya ratsa kunnuwan Haile wadda take cikin mummunan tashin hankalin harbin bindigogin daya fara tashi kawai tako ina ba tsammani dakatawa tayi cak daga bude kofar bangaren datai harta saka kafafunta a ciki manyan samudawan data zo dasu suna bayan,

Wani irin dummmm taji kunnuwanta na daukewa daga jin komai na duniya bayan sautin dayake cigaba da ratsa kunnuwanta yana wucewa kai tsaye zuwa ga kwakwalwanta wadda itama tin kafin sautin ya gama isar mata ta dena aiki ta dakata da kowane aiki cak idanuwanta ma fara dauke gani sukai a cikin seconds din da basu kai uku,

Wani irin mummunan zufan dayake hade da maiqon kitsen jikinta dayake narkewa take ne yafara gangarowa daga cikin rigarta zuwa kafafunta da sukai mummunan nauyin dayafi na buhun siminti,

Girgiza kanta tayi cikin wani irin slow sbd dawo da jinta dayake barinta da ganinta amma sam babu alaman gangar jikinta zata sake moruwa ko dawowa daidai daga wannan mummunan shock din na karshen rayuwarta....

Zubewa tayi gabaki daya jikinta na wata irin fizga da jijjiga tareda mummunan zafin jikin daya gauraye jikin nata a take sbd yanda jininta yake wata irin konewa bama tafarfasa ba,

Da sauri baiwarta daya data taho da ita tayi kanta tareda tareta tana kokarin ambatar sunanta amma ba damar hakan dan haka riqeta kawai tayi da sauri tana hanata qarasa zubewa jikinta yana rawa sosai sbd tsoro da fargaban halinda suka ga tana shiga dan kuwa da gasken gaske mummunan balain da masifar da kunnuwanta suka ji mata dauke jinta da ganinta yayi tareda dakatar da kwakwalwanta daga aiki dan haka jikinta ke wani irin rawa yana qarawa tana kokarin bude baki tayi magana amma bakin nata juyewa yake kokarin yi sbd wannan shine shock na karshe da rayuwarta ta samu wanda yake tabata tana ji gefenta daya na kokarin kasawa dan haka ta fara kokarin yunqurawa da karfi ko zata mutu ko rabin jikinta ze dena aiki saita tabbatarda ta kawar da bahar kaman yanda ta kudurta idan ta aikata lahira zata san waye ya hau wannan mulkin da shine abinda take ganin tazo duniya nema,
Koma waye a wannan daren ya karbi mulki matiqar ba Asim bane wlh bazata taba shaqar numfashi me karfi ba saita fara kawar da sultan daga duniya kafin ta tarwatsa mulki da masaurautar boyem gabaki daya.

Wani irin mummunan jan da baida kyan gani idanuwanta sukai hannuwanta da kafafunta na wata irin rawa da zufan gaske wanda yake tsiyayo mata ba kakkautawa ta ta miqe tsaye tareda miqa hannu aka saka mata wata mummunan karamar wuqar da batada kyan gani ta riqeta da kyau a hannunta datake jin yana kasawa sbd paralysed din gaske take neman kamuwa da shi dan yanda jininta yake hauhawan gaske yana kokarin harbawa cikin kwakwanta da zuciyarta dake bugawa da mummunan karfin gaske.

Jan da idanuwanta sukai har wasu hawayen dake bayyane da tsanani tsananin baqin ciki tsagwaronsa da tashin hankalin daya fiddata hayyacinta ta bude baki kai tsaye muryanta na rawar tsananin baqin ciki me girma dayake sake kumbura zuciyarta tace

'Duk me rai dayake bangaren nan kada abar kowa da rai,inason kowane bango na bangaren nan ya qawatu ya koshi da jini,kada rai ko daya ta fita.'

Tana fadar hakan ta daga kafafunta dake rawa basaji koina jefawa sukeyi tayi gaba tana saka kai a palon wanda baiwar dake bakin kofar daga ciki kai tsaye kafin tayi motsin komai ta ratsa wuqar hannunta me kaifin gaske maqogoronta wanda take wani irin jini ya feso da karfi har yana bata fuskarta gabaki daya amma bata tsaya ba ta zare wuqar da karfi yana wucewa ciki idanuwanta a tsananin rufe hakama zuciyarta a rife kaman yanda kwakwalwanta ta gama rufewa ruf.

Wainda suke bayanta suma ba imani suka hau cika umarnin data basu suna kashe duk baiwar da suka hadu da ita a bangaren babu imani ko tausayi ko daya a fuska da idanuwansu.


Asim dayayi mutuwar tsaye tin lokacinda sautin ya sauka a cikin kunnuwansa yana ratsa zuciya da kwakwalwansa shima haka ya ringa jin ganinsa na kokarin daukewa da jinsa kafafunsa kaman wanda aka saka kafa aka kwashe haka ya zube a gurin mummunan jiri na dibansa daga zuben a qasa kawai komai yake ganin yana juyawa dashi numfashinsa na kokarin daukewa zufa na gangarowa ta kunnuwansa ciki da waje,

Salman dayake cikin mummunan shock din abinda yaji din shima da tashin hankali me tsananin gaske na harbin da daman shine ya fara Girgiza duniyarsu da rikitar da ita zubewa qasa yayi tareda kokarin Asim dayake wani irin layi daga qasan dayake a zube kan gwiwowinsa,

Jini ne ya fara gangarowa daga hancin asim din me kaurin gaske da yawa wanda ya saka Salman sake shiga wani irin mummunan tashin hankali jikinsa na sake daukan wata irin rawa,

Kokarin sake kamosa yakeyi yana kasa goge masa jinin a daidai lokacin soldiers din masarautar suka iso gurin da makamansu suka bude tasu wutar data saka su aleey sake bude tasu wutar aleey ya bude baki da karfi yana bawa yaransu umarnin kada su saurara matiqar ba Queen din su ce ta dawo hannunsu ba.

Hakan daya fada tamkar ya zubawa wutar dake cikin zuciyoyin nasu soldiers din fetur ne dan kuwa su abinda suka iya kenan hakama matiqar wani abin ya samu tasu princess din da seconds da suka wuce ta koma queen ta shiga hannunsu ba a shirye suke da cigaba da bude wutar da zata qawata masaurautar boyem da fresh jini me dumi.

Irin wutar da ake budewa ta saka salman sake shiga mummunan tashin hankali yaci gaba da kokarin tada asim din ko jansa su bar gurin dan kuwa matiqar yaran LEUL din suka shigo suka samesu bazasu bata second daya ba batareda sun fasa kawunasu da bullet ba a banza dan haka yake gaggawar jan Asim din shima yana wani irin zufan mafi girman tsautsayin daya kawosu.

Jan Asim din yafara yi zufansa da rawar jikinsa na qaruwa gashi sun riga sun shigo baisan ta inda zasu fita ba dan wutar gaske ake budewa wadda qararta ya saka komai na duniyar baka ji bayan wata irin jijjiga.

Maa sakinah dake dakin da ayanah take a sume ana kokarin ganin ta farfado kai da kawo takeyi cikin wani irin zullumi da fargaba tareda rashin nutsuwan zuciya me tsananin gaske datake ji dan har wani rawa hannuwanta ke yi,

Kallan ayanah ta juyo tayi taga likitoci biyu ne a kanta ga tenya itama data dawo da ita sai kaida kawon takeyi sun kasa cewa juna komai sbd babu wanda yake cikin hankalinsa,

A daidai wannan lokacin ne sautin qarar sanarwar sabon sultan ya ratsa kunnuwansu wanda ya saka kowacensu dakatawa tareda tsayawa cak,

Tsawon mintina kowacensu ta kasa motsawa sbd shock da tsananin tsoron da yasa maa sakinah jin idanuwanta sun ciko da wasu irin hawayen da kafin su sauka kuka me tsananin karfi ya kwace mata sbd tabbatarda 'dan Ayanah ne ya hau milkin qasa me girma kamar boyem ayau.

Tenya ma rawa jikinta ya dauka hawaye masu tsananin zafin gaske suna gangaro mata ta zube qasa tayiwa Allah sujjada sbd ayau burinta dayake qume a zuciyarta ya cika NUAB dinsu ya zama mai mulkin boyem,
Duk akan takurawar sultan ne sun tabbata amma ayau din ranar da dukkaninsu bazasu taba mantawa bace harma da duniyar boyem gabaki daya bazasu taba manta wannan daren ba.

Maa sakinah kasa iya hakura tayi sbd a yanzu bahar tafi zamowa a cikin mummunan hadari dan haka kai tsaye tambayar tenya tayi inda suke ko gama fada tenya batai ba ta nufi kofa da sauri ta fice kafafunta na wata irin rawa.

Bangaren haile ta fara nufa da wani irin sauri sedai ko isa bataiba aka dakatar da ita tareda cewa bata ciki,

Hakan dataji shine ya kusan jefo zuciyarta waje dan daman son tabbatarda haile na bangarenta takeyi dan shine zai bata yar nutsuwar bahar dake can tenya dake basu dan tsaro bata nan,

Kai tsaye bangaren sultan datasan NUAB na can bai isa barowaba ta nufa da saurin gaske dan sanar masa akwai yiyuwan bahar na cikin mummunan hadari.
#MAMUH
#SULTAN LEUL NUAB YASAR ALMAZZ
#BEST LOVE
#ROMANCE
#ROYALTY
#BAHAR GHAZ BOYEM
#CRAZYLOVE

HAYATEEM novel
700
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

91
Tana isa ba damar shiga sbd tsaro dan haka ta saka aka kira mata kadir shima sbd ansan daga bangaren wishmah mahaifiyar Sultan LEUL take ne dan haka take aka tafi kiransa da sauri.

Tin kafin ya iso NUAB dinne ya fara sako kai yana gaba kadir din na bayansa wanda take securities da bayin dake tsoron bangaren suka zube qasa akan Gwiwowinsu dan bada asalin girmamawa ga sultan LEUL NUAB.

Bai ko kallesu ba akan maa sakina ya sauke idanuwansa da sukai jan da sai da gabanta yayi mummunan faduwa jijiyiyin fuskarsa da wuyansa duka sun fito sbd asalin Bacin rai da tsabagen fushin dayake yawo a kowace jijiyan dake gudanar da yawon jini a jikinsa.

Dan sassauta kallanta maa sakinah tayi sbd ko yana matsayin 'danta shi a yanzu sarki ne na qasa guda,
Sarki ne da dubban miliyoyan mutane,
Sarki ne da manyan kasashe da dama suke qarqashinsa,
Shi sarki ne a yanzu da zai mulki duk wani me rai dayake qasar boyem da zagayenta
Shi sarki ne da zai mulki har iyayensa tinda suna qasar,

Bayani tayi masa wanda baice komaiba kai tsaye ya wuce idanuwansa na tsanantuwa da halinda suke ciki yanajin dukkanin abinda yake ji a xuciya da gangar jikinsa yana qaruwa sbd zata tabbata ne a safiyar goben dole akwai wainda zasu tafi a maimakon tasa matar.

Maa sakinah bin bayansa tayi zuciyarta na sake tsananta rawa sbd qarar harbin datake jiyowa wanda har kayan cikinta rawa sukeyi sbd jin abinda bata taba ji ba.

Yana doso gurin aleey ne ya fara ganinsa take suka riqe tasu wutar wadda ta saka sauran suma dakatawa tin daman kowa kariya yake kokarin bawa nasa bangaren.

Gabaki daya gurin dauke wuta yayi bayyanar sultan NUAB da kansa a gurin dan haka take kowa ya bude sun ja da baya tareda sauke kawunansu a qasa.

Baice komaiba bai kuma tsayaba hanyar isa bangaren ya nufa kai tsaye aleey da mutum uku suna bayansa a shirye da bindigoginsu sbd ihun da suke jiyowa daga ciki yana tashi.

Salman jin harbe harben ya tsaya ya sakasa shiga sabon mummunan tashin hankalin daya qarasa rikitasa gabaki daya yana cigaba da jan Asim dan su samu gurin boyewa dan tsira sbd gabaki daya Asim din ya zama kaman gawa baya motsin komai idanuwansa a bude sai jini dayake fita hancinsa har lokacin,

Qara ce take sake tashi sosai a bangaren ta mata cikin tsananin neman ceto wadda tana ratsa kunnuwan Asim ya dago a hankali yana kallan hanyar qarasawa can qurya inda matan suke ya bude baki da sautin daya fito daqyar yace

'Bahar,Bahar,Bahar na cikin hadari.'

Miqewa yafara kokarin yi a rikice jikinsa na rawa tamkar mara hankali yabi hanyar da wani irin gudu kafafunsa na neman kifewa yayi ciki.

Salman da yake neman zarewa sbd masifar dayake hango musu babba kiri kiri bin Asim din yayi da sauri shima kafafunsa na rawa da wani irin tsallen tashin hankalin qamshin mutuwa daya fara jiyowa.

Suna shigewa NUAB shima yana sako kai aleey na kallan jini daya fara gani a gurin cikin tsananin mamaki yana fidda dayar bindigar dake jikinsa ya hada biyu a hannunsa.

Haile ma da idanuwansu suka gama rufewa kai tsaye dakuna suka fara bi suna banka kokafin da karfin gaske suna kashe duk ran da suka hadu da ita wanda ya rikita bangaren gabaki daya da wani irin ihun tarin bayin dake bangaren masu dan yawa suna gudun neman tsiran da babu hanyar fita ganin kisar da ake musu ta rashin hankali da imani.

Leylah da Bahar da gabaki daya bayin ma dake bangaren daman a cikin matsanancin tsoro da tashin hankali suke na irin harbe harben dayake daga wajen bangaren tin farko shiyasa su sam basu ma samu hankalin jin sautin karar daya tashi ba,

Bahar da bata taba jin karar bindiga ba a rayuwarta wani irin matsanancin tsoron da bata taba shigaba ta samu kanta tana shigewa bayan gadon dakinta ta boye tareda rufe kunnuwanta da duka hannuwanta biyo koina jikinta yana wata irin muguwar rawa zuciyarta ta gama tsinkewa da bugawa idanuwanta sunyi jajir harma bata iya gani dakyau dasu zufa ne me tsananin gaske take fitarwa tareda ficewa hayyacinta.

Leylah ma cikin tashin hankali jikinta na rawar da bata taba shigaba tayi karfin halin fitowa jikinta na tsima,

Jinin datake gani kusan koina ne da ihun dayake tashi me tayar da tsikar jiki na bayi da masu kulawa dasu dake gurin ya sakata ja baya da karfi cikeda matsanancin tsoro da tashin hankalin da bata taba sanin akwai ba ta juya da gudu jin ihun yana sake gauraye koina.

Baya ta koka inda ta fito da gudu kafafunta na neman kifewa a rikice ta wuce dakinta bata sani ba tana isa dakin dayake na karshe gabaki daya ta fada,

Tana fadawa ciki taga babu kowa hankalinta ya ninka tashi gashi bazata iya sake fita ba sbd yanda komai na jikinta ne tsananta rawa tsoronta na tsananta sosai shima.

Kuka ta fasa me

51 / 100