Hayateem 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Adventure

Chapter   63 / 100

186K to 189K   out of 299.8K words

kenan har abada daga rayuwar sultan din,

Yayi hakan ne dan hanasa fita koina kuma shima shiyasa tsawon wannan lokacin bai taba tafiya koina ba yana cikin boyem da kusan fiyeda rabin bataliyarsa da ayanzu suka tare a boyem dan bude sabuwar ghaz da boyem a qasa daya,

Ko ayau ma sultan din tinaninsa daya ne akan wannan particular dokar ta NUAB akan imebētis dan haka baji komai sbd batareda sanin NUAB dinba ya basa wata babbar damar da itace burinsa daya jima dashi akan Ayanah ghaz dan haka kai tsaye a cikin daren shima ya fidda takardar da kadir ya isar a fada wadda washe gari zaa gabatar da ita a fadar wadda itama sabon sultan yana cikin abinda ya soke matiqar ba zaman taro me mahimmanci akeda shi a qasa ba da ake buqatan zama da duka masu matsayin fada to ya sake zaman banza na fadar an sauya tsari zuwa manyan offices sabbi masu tsari da aka gina a cikin masarautar kusan hawa hudu tamkar wata babbar sabuwar palace kowane shugaban fada yanada office dinsa me zaman kansa da securities dinsa da mataimakansa tareda p.a,

Shi kansa Mai boyem din office sabo da babu kamarsa a boyem aka gina masa a floor din karshe da babu kowane office bayan nasa hade da lafiyayyan palo da bedroom me girman gaske dayake hade da bathroom harma da yar closet din hutawansa a ciki idan yaso harma da gurin cin abinci duka a guri daya sai office din Aleey dayake farkon shigowa floor din daga ka fito lifter wanda shima nasa yake babba da toilet lafiyayye kadai a cikinsa dan haka tsaro da security din da floor din yakeda shi yafi na koina,

Bayan sabuwar ginin offices din ba palace officials wata sabuwar ginin bangaren sultan LEUL NUAB me boyem akai acan Asalin bangarensa da aka sauyawa maana ana hade kusan bangare uku aka maidasa daya tareda yi mata tsarin da babu kamarta kaf a masarautar hakama tsarin ginin yanda akasan yana rayuwa da buqata,

Chambers din Sultan NUAB itace bangaren datafi kowane bangare kyau da tsari tareda daula a cikin boyem,

Komai na bangaren nasa akan tsarin mulkin bature yake,
Hakama bangaren mahaifiyarsa anyi masa gyara na musamman tareda sauya musu komai hakama sauran gurare da dama an sauya musu tsari wanda ya saka masarautar zamowa tamkar sabuwar masarauta ga sabbin tsare tsare da security cameras nako ina da aka sauya.

Bangaren Asim bai taba hakura ba da Bahar sbd bai taba jin soyayyarta ta rage bare fitaba daga zuciyarsa dan haka tinda ya samu cikakken bayanin barinsu masarautar zuwa uk da zama take boyem da masarautar boyem din harma da mulkin boyem din ya fice daga ransa yaji yana son barin qasar zuwa duk qasar da bahar take da zama,

Haile na ji tana gani Asim ya koma mata mummunan kaddarar da bata taba zata ba akan soyayyar da babu alkhairi a cikinta,

Bata taba tsammanin akwai macen da kaf duniya Asim zai so fiyeda burinsa da dashi ya girma ba,

Asim ya mutu rayuwarsa ta mutu batada Sauran amfanin da suke buqatarsa dashi hakama yana nan yana macewa da zama marar amfanin NUAB yana can yana gudanar da mulkinsa na gina sabuwar duniya ga boyem hankalinsa kwance hankalin uwarsa a kwance a wata qasar hakama hankalin sultan a kwance yana hutawa tamkar babu su a duniyar sbd kwata kwata tinda ta dawo taqi zuwa tirakarsa sbd tsanarsa datake ji me tsananin gaske da batada burin daya wuce barinsa duniya kuma bai taba nemanta ba tinda taqi zuwar masa maraki ce kadai take zuwa tirakarsa wadda itama a yanzu batada burin a wayi gari ace sultan din baya duniya ta huta tasan kowa a cikin su ukun ya rasa an huta dan kuwa a duk zuwan datake shimfidar sultan din bata taba ganin soyayyarta ba a tattare dashi ko so daya wanda take da tabbacin ba kuka haile bace Ayanah ghaz ce a zuciyarsa.

Su aslam zuwa yanzu sun saddaqar da rayuwa ga qarewa a gagare ba aure sbd a yanda Asim ya koma babu sauran amfani ga tsayuwa akan burin da nacewa nemar masa sarautar boyem dan haka suka zubawa sarautar allah ido da jiran damar dawowansa daidai.

A bangaren Leylah kuwa duk yanda zatai ta isar da kanta ga NUAB babu kowace hanya ta toshe sbd a yanzu ko ganinsa sai me babban rabo da matsayi dan kuwa kwata kwata sun dena ganinsa har ita har mum dinta wadda duka baifi so biyu yazo har bangarenta ya gaidata ba sedai yana aiko mata gaisuwa duk jumaa akai akai sbd bata matsayinta na uwa a garesa.

Duk lokacinda zai taho gaida mahaifiyarta saita sake mutuwa me zurfi akansa sbd gabaki daya ya sauya daga LEUL NUAB a yanzu ya koma cikakken SULTAN LEUL NUAB dinsa me tsantsar kwarjinin dayafi na baya.

Haukacewa take neman yi akan rashin samuwarsa dan haka ta cire kunyarta ta sanar da mahaifinta aure kawai takeso ayi mata ta gaji da jiran maganar aurenta data kwanta da NUAB din ita dai a tada maganar ayi mata auren koda shi bayaso ita tana so.

Maganarta tayi tasiri sosai a zuciyar mai girma yunar wanda shima zuwa lokacin yana ganin ya bada duka lokacin daya kamata ya bayar na barin NUAB yagama shiryawa akan mulkinsa duk da yayi farin ciki sosai da hatta Shuraim ya samu matsayi me girma a cikin tafiyar sarautar ta NUAB wadda Aleey kai tsaye ya saka sunansa a ciki dan hanasa tafiyar daya samu cikakken bayanin tafiyar zaiyi zuwa uk a bakin Mum zuhrah lokacinda sukaje gaidata dan haka kai tsaye ya saka alaman tambaya akan tafiyar da bai samu cikakken dalilin yinta ba a binciken dayayi bayan jinta dan hakanne ya gabatar da sunansa da wasu boyayyun hujjojin daya saka NUAB amincewa batareda yasan asalin dalilinba.

Bawa Shuraim matsayin ministern hukunce hukunce ya saka zuciyar iyayensa farin ciki sosai dan kuwa ya shiga cikin royal politics kenan zai fara kutsawa a sarautar qasar,

Su Ammi ma da suke can sunyi farin ciki sosai da hakan sbd ganin NUAB yafara jan dan uwan nasa a jikinsa,

Haile data samu labarin maganar auren da yunar yake kokarin sake tadawa akan yarsa wadda bazata iya barin NUAB ya aureta ta rasa damarta ta karshe ba akan cire bahar daga rayuwa da zuciyar Asim ba shiryawa tayi a cikin daren takaiwa sultan yasar ziyarar da bai taba tsammani ba dan haka babu kowace irin sauyi a yanayinsa ya karba zuwanta tareda bata damar kasancewa dashi.

A bangaren nasa ta kwana wanda da safe kafin ta wuce ta isar masa da buqatarta da rokonta na nemawa Asim auren leylah a gurin mai girma yunar.

Kallanta sultan yayi a karo na farko bayan lokaci kafin ya juya buqatar tata a zuciyarsa ya sauke numfashi a natse kafin ya bude baki yace ya amsa buqatarta a yau zai aika sakon takardar neman auren leylah wa Asim.

Farin ciki taji ya sauka a xuciyarta bayan watannin data share a cikin quncin baqin ciki tayi godiya tareda ficewa dan kuwa a gaggauce zata tabbatarda an daura auren dan matiqar aka karba auren a kwana uku kafin a samu matsala take son a daurasa.

Tana ficewa shi kansa sultan bai tsaya komaiba ya aikawa yunar sakon wanda yana isar masa shima bai ga illar hakan ba tinda ga dukkan alama NUAB baida raayi kuma shi bazai zabi kwadayin mulki ya aurawa leylah Sultan din da baya buqatanta ba dan haka kai tsaye ya maida saukon bada auren nata ga Asim wanda shima sultan sakon na dawo masa ya buqaci auren da gaggawa sbd yasan zaa iya samun matsala gwara ayi sa su daidaita kansu daga baya.

Koda sakon auren ya isa kunnen zuhrah har yunar ya karbi sadakin auren wanda take aka fidda sanarwar daurawa ranar jumaar da saura kwana hudu dan haka batai wani baqin ciki ko damuwa ba sbd tafi kaunar leylah din tayi aure ta cire NUAB a ranta sbd Bahar daya riga ya aura batason duk abinda zai lalata ko kawo matsala ga kaunarsu da yar uwarta ayanah dan haka da hannu bibbiyu ta amsa auren kafin ta kira leylah dan sanar da ita babban lamarin dake shirin faruwa.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

114
Leylah na shigowa lafiyayyan bedroom din mahaifiyarta ta nufota a natse yanayinta a dan sanyaye sbd bacci ta tashi dan tin kafin baccin nata sakon kiran mum din ya isa gareta amma sbd tayi shirin baccin hutawa na rana shiyasa bata taho ba saida yammar bayan ta tashi taci abinci tayi wanka ta nutsu amma jikinta hakanan yake mace har lokacin da sauran yanayin baccin datai,

Zuba mata ido Zuhrah tana kallanta a lokacinda take tahowar tanajin tausayinta sbd gabaki daya ta sauya harda yar ramewa tayi sbd kwallafa rai akan wanda takeda tabbacin ba lallai ya taba yi mata so na soyayya ba tinda gashinan bahar din ma da already aurensa yake kanta ba sonta yakeyiba yama mance da ita bare ita da baima aura ba,
Hakama bayan hakan tayaya zata iya barin son zuciya yakaita iya barin leylah ta auri NUAB bayan yana auren bahar wadda tin kafin asan ma zasu zo duniyar akai alkawarin aurensu a tsakanin iyayensu wato abaas da ayanah,
Gwara dai suji da dayan ciwon rai da damuwan Bahar daya tattara ya watsar akan su qara sa wata damuwar dan haka ta sake jin qwarin gwiwan gwara leylah din tayi aurenta da Asim din tinda shima baida matsalar komai a gurinta bataga kowace illar ba a bayyane dashi.

Zaunawa leylah tayi tana kallan Mum din ta sauke ajiyan zuciya tareda bude baki tace

'Mummy Lafiya kika kafeni da kallo haka kaman na tausayi?'

Numfashi Zuhrah ta sauke a karo na biyu tana sake tausayawa Leylah din dan haka take zuciyarta taji gwara ma kada ta fada mata a yanzu sai ankwana biyu zuwa gap da auren ta yanda kafin tafara damuwa da shiga tashin hankali anriga an daura auren dan haka dan sakewa tayi tana murmushi me kyau tace

'Ba komai tukuna amma maganar aurenki ce ta taso wadda insha Allah zuwa friday muke saka ran komai ze iya kammala dan haka saiki fara shiri hakama kada ki fita koina daga bangaren nan dan kaucewa matsala tinda kinsan dai amarya kike'

Wani irin yanayi taji yana ratsa zuciyarta wanda yake na tsantsan farin ciki da kuma ta bangare daya mutuwar jiki sbd bata taba tsammanin jin hakan ba dan kuwa ko a yanzu idan akai magana kila zaa iya saka date na daura auren nesa amma dai koma yayane taji tana tsananin kaunar zuwan ranar jumaar sbd jin matsayar da ake akai.

Da farin ciki ta rungume Mum din tana godia sosai tareda miqewa da sauri tabar dakin dan zuwa dakinta ta fara lalaban wayarta dan kiran qawayenta ta sanar dasu cikin izza da alfahari,

Ajiyan zuciya Zuhrah ta sake bayan fitar leylan tareda bude baki batareda jin tana karaya ba akan auren tace

'Allah ya sakawa auren albarka ya saka ya zamar miki mafi alkhairi akan na NUAB din tareda farin ciki da dawwamamman kwanciyan hankali dan yafi muna gabaki daya kwamciyan hankali da kawar da damuwan da zata iya shigowa zumunci.'

Leylah na isa dakinta tinda ta fara wayoyi bata sake fitowa ba har washe gari wanda yake sauran kwana uku kenan,

Daga mai girma yunar har sultan gayyatar daurin auren a tsare suka fitar akayi shi bayan sultan ya isar da sakon auren ga sultan LEUL NUAB shima baiji komaiba ya aminta tareda bada approve na auren duka a cikin qanqanin lokacinda kowa yake mamaki banda wainda zaa daurawa auren da basada cikakken sani sbd haile datasan Asim bazai taba yadda da aurenba tare duk wani motsinsa na yanda sakon auren zai isa garesa tayi ta hanasa fitowa bangarensa cikin kwanakin tamai alkawarin basa mamakin da zai sauya rayuwarsa zuwa ta farin ciki a kwanakin idan har ya zauna bai fita koina ba bai kuma kunna wayoyinsa ba ya fake da cewan baida lafiya kawai takeso.

Idanuwansa da zuciyarsa a rufe suke da son samun yancinsa na barin boyem da mahaifiyarsa ta saka masa takunkumi dan haka jin zata iya barinsa yabar qasar daga ranar jumaa din ya sakasa amince kawai tareda kashe wayoyinsa sbd daman baya fita koina yanzu hakama koyaushe cikin damuwa da rashin amfani yake shiyasa rayuwar tasa take a mace mutus yanzu.

Su Aslam kuwa da tashin hankalinsu baifi kada Asim ya taba barin boyem ba sbd dukansu sunsan gurin wa zai tafi kuma zuwansa ga bahar zuwa ne ga mutuwarsa duk da a ransu da zuciyoyinsu tare ma da masarautar boyem din sun gama tabbatarda ba aure a tsakanin Sultan NUAB din da bahar dan kuwa basu ga alamarsa ba tayaya sultan yana nan yana mulki matarsa na wata qasar daban tana rayuwar da ba ranar dawowa.

Haile samun abinda takeso da zatai ya saka karfinta dawowa dan tabbatarda auren Asim da leylah zai fara dawo da abubuwanta a hanya dan kuwa dole asim din zai fito daga mutuwan dayake yiwa kansa da rayuwarsa daganan komai zai sauya musu,

Shirye shiryen gaske sukeyi sosai na bikin wanda babu wata doguwan shagalin da zaayi daman su bikinsu a rana daya ake yinsa ayi duk gagarumin shagalin da zaayi a lokaci daya a gama shikenan,

Dukiyar Uwar Ango da ake kaiwa amayar komai da komai masu bayyanarda tsantsar gata da daular arziki haile ta hada tareda iyayenta da suka qaraso qasar duk da sun manyanta sosai amma hakanan sun taho auren asim din haka aka hada aka aika bangaren me girma yunar zuwa ga Mahaifiyar Amarya kuma sun karba tareda tukuici me girman gaske daga iyayen leylah din tin daga nan al'adun biki suka barke tako ina aka dauki harama ba sauki wanda dole ya saka Leylah shiga wata muguwan fargaba da shakka ta samu mahaifiyarta tin kafin tayi maganar data kawo ta akan kunnuwanta taji maganar aurenta da sunan da batajin kunnuwanta sunji daidai daga bakin mahaifinta take kafafunta suka kasa daukanta ta zube qasa batareda shiri ba ta rarrafawa idanuwanta na sauyawa ta isa gaban mahaifinta dake zaune a tareda mahaifiyarta a palon tareda shuraim wanda yayi mugun busy din da yau kusan sati guda basu gansa ba sedai a waya yana can bangarensa ayyuka sun mugun yi masa yawa yana jin shima hankalinsa na rabuwa biyu a tsakanin matsayin daya samu na sarautar da tattarawa ya koma uk yayi aikinsa acan da rayuwarsa.

Leylah rawa jikinta yakeyi sosai tana wani irin bari tareda kokarin danne abinda yake kokarin tasowa ya danne numfashinta daga cikin kirjinta ta kalli Abbinta tace

'Abbi hidimar me akeyi ne?
Kuma ta auren waye abbi?

Juyawa mai girma yunar din yayi ya kalli Zuhrah sbd mamakin bata sanar da ita ba bayan tintini ya fada mata ta sanar da ita tin farkon ma maganar auren.

Kallansa Zuhrah itama tayi cikin dan rasa abin cewa yanayinta na nuna sanyi da tausawa.

Maida kallansa yayi akan leylah din wadda har lokacin hannuwanta rawa sukeyi tana kallan Abbin bugawan zuciyarta na mugun tsananta amsar zancen take jira a matse.

Take Abbin ya karance halin da take ciki wanda ya tabbatarda taji maganar kenan tabbatarwa take son yi kuma da cikakkiyar alaman bata shirya karban hakan ba dan haka numfashi ya fitar shima a natse sbd bayajin wannan karan shima ya shirya sake barin maganar aurenta ta gantale a karo na biyu dan haka kai tsaye ya bude baki yana dan kama fuskarsa zuwa tabbatar mata sa abinda zai fada yace

'Aurenki Sultan ya nemawa 'dansa Asim kuma ba bayar dan haka gobe ne kadai bazaa daura auren naku ba insha Allah'

Dif kunnuwan Leylah suka dauke tareda bugun zuciyarta ta kasa motsawa ta qame idanuwanta na sauyawa zuwa mummunan ja na shock din dayafi kowane zama balain rayuwarta ta fara wata irin rawar jiki tana son bude baki tayi magana amma ta kasa dan haka sai kawai ta zube a gurin.

Kallanta Abbin yayi cikeda mamaki sbd yasan dai wannan karan aurenta ba fashi dan haka ya kalli mum din tata data tashi da sauri tayi kanta tareda shuraim wanda ya sauketa gavaki daya yana barin palon da ita zuwa dakinta.

Binsu Zuhrah tayi da sauri tana ji itama a ranta ba maganar fasa auren nan sedai leylah din tayi hakuri,

Shuraim ne ya taimaka mata kasancewansa likita kuma dan uwanta dan haka bata wani jima ba ta farfado cikin mummunan tashin hankalin da bata shigaba rayuwarta ta fara kallansu daya bayan daya su biyun sai kawai ta fashe da wani irin kuka me karfin gaske tana kama hannuwansu ta qanqame da hannuwanta dake rawa sosai cikin mummunan baqin ciki da rikicewa tace

'Dan Allah da girmansa Mum kada kumun haka,
Mum wlh banma riqe kamanninsa ba,bana sonshi ban taba son kowaba mum bayan NUAB,
Wlh mum zan iya mutuwa idan na auri wanda ba NUAB ba,ni wlh mum shi wannan din bana kaunarsa,bana sonsa bana son jin ma maganar auren dan Allah ku ceci rayuwana ku hana wannan auren,,,,

Qanqame hannun shuraim tayi da karfi shima tana dawo da kallanta akansa da jajayen idanuwanta da sukai jajir tace

'Shuraim mutuwa zanyi idan akai auren na wlh tallahi banaso ban kauna ka taimaki rayuwata dan Allah a hana wannan auren'

Dukkaninsu ba wanda ya iya ce mata komai sbd anriga angama komai baqin bikin auren tini suka fara cika masarautar hakama sultan NUAB ya riga ya fidda sanarwar auren harma anyi komai na daurin auren an gama babu ta yanda zasu iya hanasa sedai tayi hakuri kawai gashi shi kansa Shuraim din a yanzu yafi mata shaawan auran wanda ba NUAB ba sbd a yanxu dayake tareda shi ya qara sanin asalin waye shi sam babu alaman akwai tsarin mace a rayuwarsa koda akwai to tabbas kila bazatai darajar da mace ke yi ba a gurinsa sbd babu wani me daraja a gurinsa da yaransa bayan shi kadai kansa hakama duk macen da zata shiga rayuwarsa batareda yana sonta ba tabbas zata sha wahala me tsananin da rayuwarta zata iya mutuwa a banza sbd tsaurin raayinsa da zafinsa da kaf duniya ta sheda yanada shi dan haka ba amfanin taje gurinsa tinda bai taba sonsa ba bahar ma dayake aure insha Allah zai tabbatarda ta fito ta rabu dashi ya mallaketa dan shi ne kadai zai bata rayuwar datake buqata ta kauna da tattali.
#MAMUH
09033181070HAYATEEM
Mamuhgee

115
Ganin babu wanda ya nuna alaman tausayawa da yadda ga buqatartaba ya

63 / 100