ci abincin rana tareda Ammi cikin wata kulawa dake sake saka Leylah jin duniyarta na kammala.
Acan bangaren na ASIM shima Ayau yafara kokarin bayyanar da kulawansa kan Bahar wadda batajin tsananin tsoro da shakkarsa kaman yanda su Naimah ke yi dan haka koda ya fara kokarin jefa tambayoyinsa Akan sunanta da nahiyar data fito kai tsaye ta basa amsa da sunanta da kuma sunan nahiyar mahaifiyarta sbd batajin zata iya fadar sunan ghaz ne asalinta sbd ayanah ghaz da matsayinta a masarautar.
Koda lokacin tashinsu yayi suka fito suna isa ko zama basu yiba aka sanar da NUAB zai shigo bangaren dan haka duka bayin miqewa suka koma gefe suna rabe wa a Jere kansu a qasa.
Ita kuma kokarin barin gurin tayi Wanda yayi daidai da sako Kansa yana sanye da black qananun Kayan RL gashin Kansa a daure tsakiyar Kansa batareda matsesa ba tin jiya daya dawo bai fito ba sai yanzu din sbd hutawan dayayi dakyau.
Aleey dayake bayansa shine idanuwansa suka sake sauka Akan Bahar wadda take kokarin ficewa cikin girmamawa me tsaftar da ubangidansa kadai yake bawa se iyayensa ya dan sadda kai yana bude baki ya gaidata a girmame.
Bata ji ba dan bata taba kawowa ita tanada matsayi ko darajar da zata samu gaisuwa a gurin wani dan haka wucewarta tayi a natse.
NUAB dinne kadai ya wuce ciki zuwa kai tsaye palon mahaifiyarsa na Kurya Wanda ya taddata Zaune da Leylah a gefenta.
Leylah na ganinsa ta miqe tsaye a hankali cikin nutsuwa ta masa Barka da zuwa muryanta na saka Ammi din sake sanyayyan murmurshi a sanyaye a zuciyarta kuma Wani daci da radadi ne ya yanketa sbd fatar inama ace ‘yar Abaas ce a gabanta take yiwa NUAB wannan kallo da gaisuwan sbd cikar burinsu.
Numfashi ta sauke tareda jin jikinta ya mace
NUAB kuwa da hannu ya iya amsa gaisuwan batareda ya iya bude bakinsa ba dan haka ta fice daga palon dan basu guri.
Bai fitoba sai magrib ya fita ya fice.
Tenya na Zaune palo Bahar ta shigo ta gaidasu itada Maa Sakinah ta shige dakin Maa din kai tsaye Wanda sam tenya bata damuba sbd tinanin Wani aikin zatai a ciki dan haka firarsu suka ci gaba da Leylah wadda take tenya takejin har a zuciyarta tana karban auren Leylah dari bisa dari duk da sakon bai isa ga LEUL din ba Sai a gobe insha Allah sultan zai isar masa sbd jiya da yau din duka daga sultan har NUAB da kowa hutun dawowan sultan din akeyi daga gobe zaman fada zai Dora.
Wankanta tayi tai sallah ta Zaunawanta a dakin har akai ishai tanayi ta kwanta bacci koda Maa a shiga mata da fruits da madara tada ita tasaka tasha tukuna ta koma baccin.
Washe gari haka suka tafi yau kam sosai ASIM ya zauna da ita yana mata tambayoyin da suka ja zance yafara yawaita a tsakaninsu Wanda hakan yake basa dukkanin mutsuwan dayake buqata ita kuma shine mutum na biyu bayan Maa sakinah dinta da matsayinsa ya wuce nata amma yake kokarin sakewa da ita dan haka a natsenta ba hayaniya take amsawa kowane zancensa.
Yau da farin ciki sosai yake sbd firar daya samu yayi da ita yana sake gamsuwa da kowace irin rayuwar da zaiyi da ita.
Ayau dinma a tare suka fito da yammar dan tafiya zuciyar ASIM fes Akan tunanin daya yanke na isar wa da sultan sakon ya shirya karban imebetin farko kafin aurensa dan kuwa yanason Bahar ta zama tasa har abada ya shirya tsaf Akan fuskantar komai dazai hanasa mallakarta Bare babu tinda baiwa ce batada ikon kanta hakama bame ikon Hana hakan koda kuwa shi sultan dinne sbd halascin Masarauta ne.
Acan fadar sultan ma kai tsaye sako ne da yammar ya isa bangaren LEUL me boyem na takarda basa auren LEYLAH YUNAR BOYEM a matsayin tukuicin Barka da dawowansa gida Bayan shekaru.
Aleey ne ya karbi sakon kuma shine ya bude ya fara ganin abinda yake ciki dan haka sunkuyar da Kansa yafara yi a natse yana kasa fadawa NUAB din sbd sanin aure daya ma dayake Kansa bai karbasa ba yama manta dashi kila bare aure na biyu Wanda yake na sarauta ne har abada NUAB din bazai karbesa ba.
Jin shirun aleey din ya saka NUAB din dayake Zaune sanye da fararen kayan sanyi a jikinsa dagowa ya zuba masa fararen idanuwansa baice komaiba ya miqa masa hannu sbd yasan koma menene aleey shakkar isar masa dashi yakeyi bare kuma daga sultan sakon yake.
Da sanyin jiki tareda girmamawa Aleey ya miqa masa takardar me dauke da stamp ma masarautar Wanda shine sakon auren da zai fita a matsayin sanarwar hadin auren.
Karantar sakon yayi har karshe yana ganawa ya dunqule takardar ya jefar yana jin ransa da zuciyarta na mummunan baci da wata irin tafasa baisan waye ma yarinyar da ubanta da ake magana akai ba.
Acan ma sakon ya isa ga mahaifiyarsa wadd akai tsaye ta kirasa a waya tana nemansa sbd sanin zai iya samun sultan Akan hakan dan haka ta buqaci ganinsa da gaggawa dan kuwa ita hadin auren yayi mata dan kuwa bazata qi yar Zuhrah ba tinda Allah bai bata ikon cika burinta ba Akan ‘danta.
Koda kiran Ammin ya shigo wayarsa zuciyarsa takai qololuwan fusata dan haka miqewa yayi kai tsaye ya fito su Aleey na bayansa a kame sbd ganin bacin ransa a saman qoli yake.
Tinkaro gefen sukai daidai ASIM ma ya iso tareda sakaman dasu Bahar ja bayansa amma ita tana daga gefensa.
Aleey a karo na biyu idanuwansa a Yauma sun sake tabbatar masa da abinda ya kasa yadda dashi a Karan farko ganin Bahar a tareda ASIM dan haka satar kallan NUAB yayi daidai Wanda yake gaban ya dan tsaya tareda kallan ASIM Wanda ya dakata sbd tinanin gaidasa aleey zeyi kaman daga sama aleey din yace
‘Barka da yamma Ms Ayanah Bahar’
ASIM da maganar ta kashesa cikin iko da isa yace
‘Baiwa tace ta musamman bakin Ka ya San yanda zai fada sunanta…..
NUAB dayake gap da saka kai bangaren Amminsa dakatawa yayi cak tareda dan dago idanuwansa da suke jajir sbd fushin dayake tafe dashi sbd yaji lokacinda aleey a Ambaci sunan sedai bai tsammaci amsar data fito daga bakin ASIM ALMAZZ ba….
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali*_HAYATEEM_*
Mamuhgee
76
A cikin nutsuwa da wata irin izza ya juyo a hankali idanuwansa dake jajir suna dagowa tamkar Wanda suke a buge sbd wani zazzafan yanayin dayake cikinsu na abinda ya gama kunno wutar jininsa da kuma abinda kunnuwansa suka ji masa yarinyar da igiyoyin aurensa uku suke kanta da sai ayanzu ne ma da aka ambaceta yake tina hakan Wani yake kira da baiwarsa.
Akan fuskar Aleey ya fara sauke idanuwansa sbd ya samu direction kai tsaye na wacece Bahar din a cikin bayin dake tsaye cikeda Wani irin tsoron ganin maza biyu masu BOYEM da kanta tsaye a gurin daya niimarsa ta dauki Zafi take,
Aleey da NUAB din yana dakatawa shima ya dakata da maganar da zaiyi yana qasa da Kansa dan kuwa yasan duk abinda ya Dakatar da tafiyar NUAB mai zafi ne dan haka gabaki dayansu Yaransa qasa sukai da kai kowannesu shirye da raba ASIM da rayuwarsa batareda shakkar komai da abinda zai iya biyowa idan NUAB yace Ayi to yi din zasuyi.
Kallan bayin yayi da idanuwansa masu girgiza Wanda aka kalla dasu a Karan farko ya bi bayi da kallan tsaf yagansu gabaki daya da uniform da komai iri daya,
Gabaki dayansu kasa riqe kallansa daya sauka akansu sukai duk da kansu na qasa cikeda fargaba da tsananin girmamawa zubewa qasa sukai gabaki daya bayin kaf.
BAHAR saida kowa ya zubewa tukuna ta motsa zata zube qasa din itama zuciyarta na Wani irin nauyi da radadin baqin cikin kasancewanta anan a Karan farko,
Sauka gwiwowinta zasuyi qasa ASIM da zuciyarsa bazata taba daukan ganin macen dayake tsananin so kuma macen da zata zama imebētinsa zuwa wishmarsa ta durqusawa NUAB dan haka kai tsaye hannu ya miqa zai riqota dan hanata kafafunta kaiwa qasa.
Hannunsa na isa gareta aleey yayiwa hannunsa Wani irin riqo da hannunsa daya tareda dagowa da sauri da Wani irin mamakin dayake hade da bacin ran da bai bayyana duka ba sbd babu kuma Wanda yake da ikon kai hannunsa jikin Bahar da aurensu yake kanta ko waye kuwa.
NUAB kuwa da zuciyarsa ta gama qara fusata hakan daya faru ya tabbatar masa waye Bahar din dan haka idanuwansa ya rintse da karfi tareda budesu akanta ya miqa hannu cikin wani irin fushin daya saka su aleey sake yin qasa da idanuwansu ya damqi hannunta ya jata yana Juyawa daga inda ya fito tareda fasa shiga gurin Ammin nasa.
ASIM da zuciyarsa ta gama quluwa tana wata irin tafarfasa fizge hannunsa yayi cikin tsantsan tiriri da kishin dayaji na Neman kashe zuciyarsa da dukkanin gangar jikinsa ya daga hannu zai shararawa Aleey lafiyayyan Marin rashin da’ar da yayi masa daya daga cikin securities dinne ya sake riqe hannunsa Wanda bai tsaya wata wata ba ya sakarwa security din wata mummunan Marin daya saka fuskarsa jajir.
Sauran securities din cikin girmamawan da batada amfani garesa suka dan saukar masa da kai bisa umarnin aleey daya kallesa ya bude baki yace
‘Allah ya Huci zuciyar Li’ul ASIM’
Yana gama fadan hakan ya juya yabar gurin yana ban Bayan ubangidansa da gabaki daya rahamarsa ta dauke sbd Zafin dayake tafasa a jininsa na fushin dayake hawan gobara a yanayinsa,
Sauran suma gabaki dayansu bayansu suka bi Ana barin ASIM a gurin cikeda Wani irin tafasa da jininsa ke yi a gurin sbd NUAB ya gama wulaqantasa da bayyanarda shirin yaqi a tsakaninsu dan kuwa hakan da yayi masa zai iya bayyanar da tasa zazzafar qiyayyar sbd abinda yayi a gurin yafi yaqi da gabar dake tsakaninsu na gadar mulki,
Zai iya hakura Bayan yaqi da dukkanin kokari idan yayi ya rasa mulkin BOYEM amma kuma Akan Bahar bayajin a bayyane ma zai iya barin ko uwar NUAB din a raye bare NUAB din dan kuwa sedai ya rasa ransa gurin yaqar hakan dan kuwa Bahar tasa ce akanta zai iya fuskantar kowa,
Zai iya tsayawa gaban kowa ya bugi kirjin ita tasa ce dan haka NUAB koma me yake nufi da hakan da yayi a yanzu dan kawai tana baiwar mahaifiyarsa to tabbas zai nuna masa baiwa ce ita daga shi har ita sunada iko da ita cikakke dan haka zai shayar dashi mamakin da zai girgiza dan kuwa a ganin idonsa zata zama macensa imebētinsa.
Barin gurin yayi Salman na biye dashi shima tasa zuciyar kaman zata fashe suka isa bangaren queen haile ASIM din ya shige idanuwansa jajir baya ganin komai daidai tsabar baqin cikin dayake Neman kashesa.
HAILE dake Zaune tareda su Aslam suna hutawa a palon hutawanta Kayan marmari da abubuwan hutawan cike Jere a gabansu duk da ba Wani dadin rai suke cikinsa ba dan kuwa suna Zaune a gurin labarin auren ‘yar mai girma YUNAR daya bawa NUAB Yazo kunnuwansu ya lalata gabaki daya Sauran dan farin cikin rayuwar daya rage musu zuwa sabon baqin ciki me girman gaske dayake Neman makantar da HAILE wadda ta dago jajayen idanuwanta ta kalli Aslam wadda tafara zantika cikin tsananin tashin hankali da baqin ciki me girman gaske hannuwanta har suna rawa idanuwanta jajir take cewa
‘Auren yar YUNAR ga NUAB yana nufin zai tsaya masa a gurin karban mulkin BOYEM,
YUNAR zai zabi tsayawa duk Wanda ya zama Siriknsa a cikin magadan biyu,
Tayaya zai zabi NUAB ‘dan mistress Akan ASIM Wanda a bayyane da duniya shine dan dayafi da’a da kwantarwa manya kai,
ASIM shine Wanda ya cancanta ya bawa aurar yarsa,
ASIM ne ya kamata ya zabi tsayawa Akan karban mulkin BOYEM me zaisa ya zabi dan ta’adda?
Baisan halinsa da rayuwar da yakeyi ba Wanda yana buqatar sani dan kuwa Mamee muna tsananin buqatar ‘yar YUNAR ta kasance Matar ASIM ba NUAB ba,
Mame kota halin yaya kada ki bari dan Allah NUAB ya samu Leylah YUNAR a matsayin mata idan ba ASIM ba sbd aurensa da ‘yar nada kashi casain na alaman nasara Akan ASIM mame dan Allah kada ki bar hakan ta faru…..’
Yanda take maganar cikin tashin hankali da mummunan baqin cikin daya danne zuciyarta kaman zatai bindiga ta buga ya saka meryam ma hankalinta tsananta tashi da Wani irin zallar tsoro da zullumin daya saka idanuwanta jajir dan kuwa faduwar ASIM yana nufin tasu faduwar a abinda suke tsananin so tamkar mutuwa.
HAILE da zuciya ta gama cinyeta Wani zazzafan radadi zuciyarta ke yi dan kuwa idan ma adalci zaayi ASIM dinne ya fara zuwa duniya dan haka shine ya kamata a fara bawa macen a daura masa aure kafin daga baya Ayi maganar NUAB Wanda batajin ma yanada niyar auren a rayuwarsa dan kuwa ta’addancinsa kadai ya sakawa gaba,
Tayaya sultan zai mata wannnan mummunan cin fuskar a Idon duniya ya zabi fara yiwa dan mistress dinsa aure Akan ‘dan sunnarsa,
Tayaya zata iya barin YUNAR ya tsayawa NUAB ba danta ba?
Tayaya zasu iya barin NUAB ya samu wannnan saar ta auren ‘yar YUNAR Bayan ga ASIM dinta….
Jajir idanuwanta sukai Wanda tsananin ja da baqin cikin dayake cike dasu da jini da zuciyarta idanuwanta har wasu ruwan da ba hawaye ba suka tara,
Shigowan ASIM din Wanda tamkar jininsa zai Kama da wuta hannuwansa har wani rawa sukeyi ya sakasu kallansa su dukan kowa idanuwansa na tsananta ja sbd suna ganin tsantsan fushinsa da bacin ransa tareda baqin cikinsa a bayyane kenan shima ya samu labarin,
Zaunawa yayi a kujera yana kasa bude baki sbd fushinsa yayi yawan da bazai iya magana kai tsaye ba,
Shiru sukai dukkaninsu kowa da baqin cikin dayake cinsa,
Sai Bayan mintina masu tsayin gaske ya bude Baki cikin radadi me bayyana yace
‘Ko zan rasa rayuwata bazan Bari NUAB ya shiga tsakanina da abinda nakeso ba,
Akanta na shirya bayyanannan yaqi dashi da mahaifinsa sbd shine yake tsayawa haukar NUAB din kowace iri dan haka wannan Karan mutuwa ce kadai zata rabani da ita’
HAILE da kalaman sukai mata Wani irin dadi da Jin sassauci tace
‘Ko ni bazan taba barin ya sameta ba koda hakan na nufin aikata kowane irin aiki saina tabbatarda sun rabu rabuwa da har abada’
Aslam ma Jin tayi sanyi na samun sassauci na dan ratsata ta kalli ASIM din tanajin nutsuwar daya kasance yana son Leylah din dan sun dauka bazai sota ba bazai kishin kasa samunta ba dan haka dukkaninsu suka Ji sun dan samu relief na zasu Hana auren da dalili me karfin gaske.
********kai tsaye bangarensa ya nufa da ita bata ma ganin gabanta sbd yanda yake riqe da hannunta datake Jin azabar riqon da yayi mata amma idanuwanta da zuciyarta sun rufe da ‘dacin da harma bata Jin komai dan haka bata bude idanuwanta sai lokacin da taji ya saki hannunta da karfi tayi baya idanuwanta na budewa jajir itama sbd har cikin ranta bata kaunar ganinsa dan ganinsa ba mummunan auren dayake tsakaninsu tinawa ba hadda rasuwar mahaifinta dan haka kokarin sake rintse idanuwanta takeyi cikeda baqin cikin kasancewa tareda shi…….
Saukar hannunsa Akan rigar dake jikinta ya fizgo da karfin gaske yana rabata biyu daga jikinta ya sakata bude idanuwanta masu girman gaske da kyau sunyi ja ta sauke akansa tana riqe hannunsa da karfin gaske tareda bude baki a Karan farko muryanta ya sauka kunnunesa da tsananin fushi tana kallan cikin tsakiyar idanuwansa da kowa baya iya kalla tace
‘Ābidehali?¿
Jajayen idanuwansa ya dago da Wani irin tsananin Zafi da fushi tareda bacin ran gaske ya kalli bakinta daya furta kalmar da duk duniya babu Wanda ya taba furta masa hatta uwa da ubansa kuwa kaf duniyarsa babu Wanda ya taba kallan fuskarsa ya furta masa wannan kalman da zata iya ajalin dik Wanda ya furtata,
Yana da hankali take tambayarsa????
Shi LEUL take tambayar yanada hankali???
Menene hankali?
Batasan koda Yazo duniya baida hankali ba?
Batasan baisan menene hankalin ba?
Ina ta samu zarrar yi masa wannan kalmar?
Qarasa fizge rigar yayi cikin wani irin sabon rashin hankalin dayaji yana shigarsa data ambata sbd Allah ne kadai yasan yanda ya danni mahaukaciyar zuciyar tasa bai yaga Kayan jikin nata tin acan ba.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali*_HAYATEEM_*
Mamuhgee
77
Dago idanuwanta tayi da suka tsananta Wani irin Jan da hawaye masu tsananin radadi suna cikowa a cikinsu ta kallesa hannuwanta na kare jikinta duk da akwai wata qaramar halfvest din a cikinsu,
Ayau ta fuskanci tozarci da baqin cikin da bazata taba mantawa ba daga Wanda batajin har abada zata manta,
Wani mummunan baqin ciki ta Hadiye ta bude baki zatai magana ya juya ya bar gurin har lokacin hannuwansa har wani rawa sukeyi yana isa kofa ya fice tareda rufe kofar da karfin gaske daya sakata rintse idanuwanta tana silalewa qasa ahankali wasu hawaye masu tsananin zafi suna gangarowa daga idanuwanta.
Su aleey dake palo a tsatsaye babu Wanda ya dago kai a cikinsu kowa Kansa sake yin qasa yayi daya fito din tamkar guguwan wuta zata tashi haka fuskarsa tayi Wani ja ya fice daga palon suka biyo bayansa,
Suna fitowa kallan securities din aleey yayi yace su tsaya su tsare bangaren tinda princess din GHAZ tana ciki.
Komawa sukai bakin kofar shiga ta farko data shiga palon suka tsare shi kuma aleey yabi Bayan NUAB din zuwa gurin kiran Amminsa da shine ya fiddosa tin farko.
Tin kafin su isa aleey a fidda wayar sa ya Turawa Maa sakina sakon taje bangaren NUAB Princess din GHAZ tana can.
Maa sakinah dake Zaune tana kallan time a agogon wayarta na rashin dawowan Bahar har lokacin zuciyarta cikin wani zullumi da rashin sukuni take dan haka miqewa tayi tana nufar dakin bayin bangaren dake Bayan kitchen dinsu dan dubowa.
Tana shiga kitchen zata bi ta kofar kitchen din zuwa dakin nasu sakon aleey ya shigo wayarta tana dubawa kirjinta yayi Wani dummm Wani sabon zullumin da fargaban idan ba Wani abin ne ya samu Bahar din ba dan haka dawowa tayi tana fitowa daga kitchen shi kuma NUAB a lokacin ya shigo harya saka kai a palon farko ya shige dan haka basu hadu ba ita kuma kofa ta nufa kai tsaye ta fice,
Aleey dayake kofar gurin ta hadu dashi baice mata komaiba sbd baya magana ko wace iri idan baisan Meye a zuciyar LEUL dinsa ba dan haka kai tsaye bata