kaina an yi mini tsawa ya sa Rabi'atu ma ba ta matso kusa ba, balle Baby da ta maƙale a bayanta jikinta na rawa.
Duk wannan bugun da hayaniyar Gimbiya na ji ba ta buɗe ba, har ta window ya je yana kiran sunanta sai da ta ga dama sannan ta buɗe bayan har handle ɗin kofar sai da Yallaɓai ya kar ya shi wajen jan shi, ta fito daga ita sai rigar barci doguwa a cikinta da hula mai raga raga ta fa gan mu duk tsaye ga uban gayya na huci kamar zaki amma duk ba ta sha jinin jikinta ba.
"Topha! Lafiya na ga an taru a ƙofar bangarena?
Ta fada tana mai kallon mu ɗaya bayan ɗaya.
Mamaki ya hana ni magana shi kuma Yallaɓai ban san dalilin ba ina tunanin shima dai mamakin ne sai cije baki yake yi alamun yana ƙoƙarin sarrafa ɓacin ran shi ganin haka yasa na yi saurin tare ta da cewa.
"Ke yanzu duk ba ki ji abin da ke faruwa ba?
"Ban ji ba me ya faru?
Ta faɗa cikin halin ko in kula.
Motar na nuna mata ina faɗin" Motar Rabi'atu ne muka wayi gari an yi mata haka'
Sai ta wani kama baki kamar na mamaki da firgici kafin ta ce" Subhanallah garin ya ya haka ya faru?
"Shi ne ake son sani yanzu"
Na bata amsa sai na ga ta wata dariya ta ce" Ikon Allah! To ko aljanu ne suka yi haka?
"Aljanu ko ke da kanki?
Yallabai ya katse mata mgana a fusace, sai na kalle shi jin abin da yace ita ko sai ta ware ido kafin ta ce" Ni kuma?
"E ke"
Ya faɗa yana takawa kusa da ita ƙokarin kare rabin jikinta take yi da ƙofar ya saka ƙafa ya tokari ƙofar ta buɗe sai ta yi baya da sauri tana faɗin" Ban gane ba daga ganin abu sai kawai ka ce ni ce na yi? Ina ruwana?
Ta faɗa cikin rashin kunyar da ta saba da shi a kwana biyun nan.
"Saboda ke ɗin ce mai muguwar zuciya a gidan na."
Ya faɗa yana mai kallonta kamar ya jawota ya fara dukanta a yanayin shi.
"Oho dai kai ne mai mugun zuciya wallahi. Ban da rashin adalci tun yaushe na ke bin ka da ka saiya mini mota amma kaƙi shi ne ko kunya za ka siyo ma matarka mota ni ba ka siya mini ba! Hakan da ka yi adalci ne? Wallahi kai ne ba ka da zuciya mai kyau kuma duk cutata da ka yi saboda wannan yarinya Allah na sama."
"Bum!!"
Ya saka hannu ya buge mata baki kafin ta karisa magana sai da na ji tsoro ganin abin da ban taɓa gani ba. Yallaɓai na kai hannun shi jikin mace.
"Tun kafin Megadi ya tabbatar mini da ke ce da man naa ji a zuciya ke ce kika yi haka? Ni za ki yi ma asara saboda shegen kishin ki na banza da wofi?
"Wallshi da man na ce sai dai kowa ya rasa"
Ta sake faɗa har tana rantsuwa sai a lokacin na gama fahimtar komai wato dai Gimbiya ce ta yi wannan ta'asan.
"Ba ka yi adalci ba sai ka siyo biyu in kana so a zauna lafiya ko ka fara siya mini bayan an kwana biyu sai ka siya mata amma ko kunya ba ka ji ba ka je ita ka siya mata ni kuma ko oho? Wallahi ba ka isa ba in dai ina gani ba wanda ya isa ya yi mini rashin adalci ban yi magana ba."
"An yi miki rashin adalci ki yi duk abin da za ki yi"
Ya faɗa a fusace kafin ya ce" Kuma wallshi ki sani ba ni kika yi ma asara ma kanki kika yi mawa. Sai kin biya duk abin da kika bannatar kin ji ma na rantse."
"Wallahi ba zan biya ba. Rashin adalcin ka ya jawo maka asara "
.
Ta faɗa har tana rikr kugu ina so na shiga na yi magana amma ina tsoron kar ya haɗa da ni amma hayaniyarsu ta fara yawa ga su Khalipa har sun fito suna tsaye sannan ita bakin ta yaƙi yin shuru shima haka tana fada yana faɗa.
Ganin haka yasa na ce ma Baby ta tattara yaran su koma shashena. Rabiatu ma da na duk ta tsorata na ce su shige ciki sai da na samu sun shige ciki sannan na koma wajen su Gimbiya abin har ta kai ga tana kiran shi Azzalumi kuma sai Allah ya kama shi.
"Alhamdulillah na ji ni azzalumi kuma kin ga ba za ki cigaba da zama da mai zalunci ba. Zo ki fice mini daga gidana Saudatu wallahi nima na gaji da zama dake."
Jin haka yasa na yi zaraf na shige tsakaninsu ina faɗin" Haba Yallaɓai."
"Ta zo ta fice mini dags gida na ce ko!
Ya sake maimaitawa, ita kuma jin haka sai jikinta ya yi sanyi ta fashe da kuka.
"Ni yau kake kora a gidan ka Yusuf?
"Na kore ki gidan ki ne ko gidana? Wallahi na gaji dake da halin ki, da man tun tuni ya da ce na kore ki, kin fara yi mini asaran dukiya wata rana rai za ki kai ma hari."
"Duk abin da ya faru kai ne sila. Domin da ka yi adalci da haka ba ta faru ba maimakon ka yi nadama amma sai ka kore ni? Ni za ka tozarta a kan wancan yarinyar?
"Ba sunanta yarinya ba. Sunan ta Rabi'atu ce matatace kamar yadda kike matata. "
Gimbiya ta sake sakin kuka kafin ta ce" Saboda ita yau kake kora ta?
"E saboda ita ne domin ita ba mahaukaciya ba ce kamar ke"
Sai Gimbiya ta fara kururuwa har tana zama a kasa hannu a saman kai tana faɗin Yallabai ya zageta ya ce mata mahaukaciya.
"E na faɗa in ba mahaukaciya ba wacece za ta yi abin da kike yi? Ita yarinyar da kike kishi a kanta wallahi na tabbata ba za ta yi haukan da kike yi ba. To tun da ni ba ki bani farimciki nima kuma ima zaluntarki gwara ki zo ki tafi garin ku na gaji"
A fusace ta mike tana faɗin" Nima wallahi na gaji "
"Ni na fara gajiya"
Yallabai ya faɗa har yana sakin tsaki, ina so na yi magana sun hanani da wannan ya dire wannan zai ɗauka.
"Sai ka sake ni domin na je ma da iyayema da shaida."
Gimbiya ta faɗa tana tsiyayan hawaye duk sai jikina ya yi sanyi.
"Sakin kike bukata?
Yallaɓai ya faɗa idanuwansa sun yi jajir.
"E ina buƙatar shaida."
"Fine. Zan ba ki shaida."
Ya faɗa yana mai juyawa da gudu na fito na sha gaban shi ina kiran sunan shi amma ya raɓa ni ta gefe ya wuce na riƙe bayan rigan shi ina faɗin.
"Don Girman Allah Yallaɓai kar ka yanke hukumci cikin fushi."
Fizge rigan shi ya yi kawai ya shige bangaren Rabi'atu na taho ya banko mini kofa a fuskata sai na yi sororo, ba. Buga masa ganin mun riga mun bar ma Megadi abin faɗa duk da bai fito ba amma yana cikin ɗakin sa yana jiyo duk hayaniyar dake faruwa.
Shashen Gimbiya na koma tana cikin bedroom ɗin ta, tana haɗa kaya a cikin babban akwatinta tana kuka. Duk ta zubo su daga cikin wardrope ɗin ta. Hankalina ya tashi na fara tare ta ina hanata saka kayan a cikin akwatin da ta ɗauko sai na karɓe ina faɗin" Haba don Allah miye haka kile yi?
"Ba ji ji me ya ce ba ne? Ya ce na zo na bar masa gida tun da ba na bashi farimciki."
.
Ta faɗatana mai ƙara fashewa da kuka. Duk taƙamar cikin mintina har ta fita kamaninta sai na dafa kafaɗanta ina lallashinta.
"Ki yi hakuri kema bacin rai ne shima haka in zuciya ta yi sanyi za a daidai ta."
"A'a Maman Jidda ki bari kawai na tafi. Sakina fa yaje ya rubuto ya kawo mini zaman me zan yi?
"Ba zai sake ki ba. Ba aure ki don ya sake ki ban"
Na faɗa ina mai kara dafata, cikin kuka ta ce" Ya ce fa da kanshi ya gaji Maman Jidda. Ni wai yau Yusuf ke yi ma wulaƙanci saboda wata ƙaramar yarinya?
"Laifin ki ne me ya sa kika fasa motar nan? Duk da shima bai kyauta ba amma da kin yi shuru kin jira ki ga iya gudub ruwan shi. Sannan ai shi mijin ku ne shugaban ki, bai kamata yana faɗa kina faɗa ba. Duka ranku ya baci shi ya sa kuka yayyaba ma juna mganganu."
Cikin hawaye ta kalleni kafin ta ce" Na kasa haƙuri a nan wajen na ke jin ƙuna in na ga Yallaɓai na fifita wannan yarinyar a kaina? Na kasa hakuri ne"
Ta faɗa tana mai nuna mini saitin zuciyarta sai kuma kawai ta yi zaman dirsham a ƙasa tana cigaba da gurzan kuka. Sai na bi ta nima na zauna a gefenta ina ɗan bubbuga kafaɗanta alamun lallashi.
"Shi ya sa na sha ce miki Gimbiya ki yi haƙuri domin duk abin da haƙuri zai ba ka rashin sa ba zai ba ka ba. Da kin yi hakuri don Allah duk wannan abin da ya faru zai zo ya faru?
Sai ta yi shuru ta kasa mgana sai kuka ni kuma sai na cigaba da faɗin" Kana gani za a cuceka ayi maka abu na rashin adalci amma sai ka yi shuru ka yi haƙuri ba wai don an fi karfin ka ba sai domin hakurin shi ya fi alheri. Tashin hankali ba shi da daɗi da a ce kin same shi ta lalaba kin tambaye shi Baban Jidda ni fa tawa motar sai yau she za ta zo? Duk amsar da zai wuce kema na ki na hanya ba ai yana da ilimi ya kuma san abin da yake yi. Ba ina kare masa ba ne amma ina so na faɗa miki gaskiya. Yallaɓai na kamanta adalci, nu ya faɗa mini zai siya ma Rabi'atu mota saboda makarantar ta, duk da bai yi mini bayani ba na san ya fara siya mata ne saboda ita ke ɓukata yanzu. Ke kuwa kina da shi canji kike so nima haka shi ya sa ya fara siya mata kafin ke daga baya."
Sai na ɗan dakata ina kallonta ganin ta natsu tana saurarena amma ba ta shassheƙan kuka ba.
"Da kin yi abin cikin lalaba da duk wannan abubuwan ba su faru ba. Ga shi yanzu zuciya ta ɗebe ki kin aikata abu. Ran ki ya ɓaci shima na shi ya ɓaci fisalillahi ina daɗin shi.?
Cikin jan majina ta ce" na kasa hakurin ne. Wallahi na kasa."
Ta fada hawaye suna mata ambaliya sannan ta sake kecewa da kuka kamar wata ƙaramar yarinya.
Duk surutun da na gama yi a banza domin Gimbiya ta miƙe ta cigaba da haɗa kayanta ta kuma ce sai ta bar masa gidansa tun da ya ce ba ta bashi farinciki.
Ganin ta ƙi saurarana ya sa na fita zuwa shashena na iske su Baby sun yi jugum har da ita kanta Rabi'atu ni saboda tsshin hankali na manta da yau suna da makaranta sai da Baby ta yi mgana.
"Kun makara ki shiga kitchen ki sama muku abin da za ku ci. Rabi'atu yau ba ki da shiga makaranta ne?
A sanyaye ta ce suna da lecture, sai na ce ta koma bangarenta ta shirya mana. Ta amsa mini ni dai na shige ƙurya na dauki wayata na danna ma Nene karon farko domin mi ban taɓa kiran ta da sunan wata matsala ba sai dai gaisuwa. Bayan ta ɗauka mun gaisa ba ɓata lokaci na zayyana mata duk halin da ke faruwa ta ja salati ta dire kafin ta ce" Ya sake ta ne?
"Ban sani ba amma dai ya shiga ɗaki ya rufe kansa."
"Innalillahi Saudatu ba ta jin mgana. Sadiya don Allah ki hana ta tafiya bari na kira Zuwaira."
Sai na amsa mata da to, muna gama wayar na fito sai na ga ba Rabi'atu Baby kuma tana kirchen yaran kuma sun saki suna ta wasan su sai na fita, haraba na ci karo da Rabi'atu tana buga ƙofar shashenta.
"Yana ciki ki yi magana in ya ji muryan ki zai bude."
Ban tsaya ba na shige bangaren Gimbiya na same ta har ta gama haɗa kayanta ta zurma hijabi, na janye akwatin na ce ba ta za ta tafi ba.
"Maman Jidda ki bar ni na tafi, ya ce sakina zai yi"
"Shi bai ce ba ya dai ce ki bar masa gida amma bai ce zai sake ki ba ke ce kika furta haka"
Cikin kuka tace" To ai manufarsa kenan. Miye ma'anar miji ya kore ka daga gidan shi? An ya an taɓa yi ma wata mace tozarci kamar yadda yau Yusuf ya yi mini?
Ina mata mirmishi na ce" Nima mun taɓa faɗa da Yallaɓai na ce zan bar masa gidan sa ya ce na tafi bs zai hana ni ba'
Sai ta kalleni baki buɗe tana mai mamaki.
"Wallahi kuma a kan ki ne. Ban taɓa faɗa ma kowa ba ranar a gidanmu na kwana."
Sai na ga ta koma ta zauna gefen gadonta amma na kasa mgana, ni ma sai na zo na zauna a gefemta amma ina riƙe da akwatinta a hannuna.
"Shi ya sa na faɗa miki haƙuri ake yi ba kyau yanke hukunci cikin fushi."
"Ya ce ki bar masa gida? Ke ma ɗin!
Sai na gyaɗa mata kai ina dariya kafin na ce"Yes na kuma yi tafiyata saboda lokacin raina ya ɓaci komai ma zai iya faruwa."
"Wa ya dawo da ke?
"Alhajinmu ya yi mini faɗa ya nuna mini kuskurena. Sannan shi kuma ya zo ya tafi da ni washegari da Safe."
"Da man kuma samun sabani a kaina?
Na ɗauka ke ba ki da kishi Maman Jidda?
Ta faɗa tana kallo na kuma da gaske take yi abin da ke ranta ne ta faɗa. Ban san na kyalƙyalce da dariya ba sai da na ga ina yi.
"Da gaske ina ta so na tambayeki tuntuni. Miye sirrin ki da ke ba ki damu da mu ba? Lokacin komai matsala za mu samu ni ce zan zama sila ba ke ba. Kuma sai na ga kamar ba ki da kishi a kaina, ga ma Rabi'atu yadda kike mu'amalamta kamar ba kishiyarki ba, da gaskr nake yi na sha tunanin ko dai ba ki da zuciya ne? Ba kya jin irin zafin da muke ji in mun gan shi da ke?
Kai na girgiza ina faɗin" Me ya sa ba zan ji kishi ba ai nima mace ce Gimbiya ina da zuciya a kirjina.'
"Amma me ya sa ba ki nunawa?
"Nunawan ba shi da amfani in har ka bari wasu daga waje suma fahimta. Amma ina nunawa a yanayin da Allah ya hallice ni, mun sha yin faɗa ba adadi ni da Yallaɓai. Amma sirrina shi ne haƙuri gaskiya na saka haƙuri a kan komai ko na ji wani abu ya motsa mini sai na kira sunan Allah na danni zuciyata na yi haƙuri. In abu ya dsme ni Ubangijina na ke zama ina faɗa mawa ina, shi na kuma roƙa ya cire mini mugun kishi a zuciya na ce ya saka mini salama domin na samun zaman lafiya."
Gimbiya ta buɗe baki ta rufe kafin ta ce" Ikon Allah. Ni fa sai nake ganin duk wanda ya ce na yi haƙuri kamar ba ya sona ne."
Ta faɗa har tana yin tagumi.
"Haka za ki ji da farko. Amma in kika yi haƙurin wata rana ke ce da riba. Sai dai riban ya kan ɗau lokaci kafin a cinmma riban amma watan wata rana mai hakuri dai shine ke da riba."
"Haka ne."
Gimbiya ta faɗa cikin sanyin jiki, ni kuma ina ta mata dariya ta ce wai ko ba ni da zuciya ne bana kishin su.
"Kawai na saka ma raina ba don ni kaɗai Ubangiji ya hallici Yallaɓai ba. Kuma ni ban isa na hana shi abin da Allah ya ce ya yi ba. Sannan ina yi ma zamantakewar mu kara saboda nima ya yi mini kara, ya yi mini hallaci kamar yadda na yi masa shi ya sa nake tausan zuciyata ina karɓan duk wani abu da ya fito daga bangaren shi da zuciya ɗaya. "
Kai ta girgiza alamun gamsuwa kafin ta ce" Ga shi kuma kina ta ganin riban haka. Ki yi haƙuri a da ina yi miki kallon kin gama da Daddy domin yadda yake darajs ko sunan ki aka kira abin mamaki ne. Ya taɓa faɗa mini bayan Nene ke ce macen ta farko da yake jin kunyar ki roƙi sa abu ya kasa yi miki. Ya taba ce mini ke ce ragamar gidan shi, wakilyarshi da ba shi da haufi a kan karan da kike yi masa. Ke ya taɓa faɗa mini cewa ke ɗin ta musammance a rayuwar shi da har gobe ba ki samu madadiya ba."
Sai na kalleta ita kuma ta cigaba da faɗin" Ni ban gane ba na yi ta fada da shi a kan ki. Karshe dai ni ce ba na cin riba. Sannan su Anty Bahijja su yi ta nuna mini yana jin tsoron ki. Halima ma har ce mini ta yi in ban dage ba saboda ke Daddy zai iya rabuwa da ni."
Bsn wani ji mamaki ba da man na san ai ba sa sona. Saboda haka ba za su faɗi alheri a kaina ba.
Kamar an matsi bakin ta nan ta shiga faɗa mini mganganun da suke fada a kaina ba daɗin ji, da bakin ta da ke cewa duk in da Halima ta zauna sai ta zage ni, ta ce mini Naja ce ma kr kwaɓanta wani lokacin amma su Anty Bahijja sai dai su yu ta zugi in abu ya kwaɓe su koma gefe. Ko a nan hatsaniyar auren Rabi'atu duk suka kai ta suka baro miji duk ya gaji da ita.
"Kin gani ko? Kuma da abubuwan da kika yi ta yi ne yake tarawa shi ya sa ya ce ya gaji. Na sha faɗa miki ki yi hakuri domin hakiri shine mafitan ki, wata rana akwai wani abun da zai faru da za su nuna miki sun fiki kusa da shi akan ki."
"Gaskiya ne"
"To gwara ki gyara tun kafin lokaci ya ƙure miki "
Sai ta yi shuru amma ta daima kuka sai jan majina. muna zaume muka ji ƙaran buɗe get sai na miƙe lna leƙe ts window ina faɗin" Ga ta man ina jin ta iso"
"Wa kika kira?
"Nene"
Na bata amsa sai ta ware ido ina dariya na ce" Ba