Turken Gida Book 3 Complete Hausa Novel

Author :  Janafty Category :  Love

Chapter   36 / 55

105K to 108K   out of 163.1K words

na so na yi sai na fasa kar ya ce na raina shi yana magana ina yi masa tsaki.

"Kina yayeta in sha Allahu sai ki koma. In kuma lokacin na sake yin ajiya shike nan sai ki jira ki sake haihu ki yaye sai ki koma."

Ai ban san na kai ma kafaɗan Yallabai duka ba ya kauce yana dariya.
"Me na faɗa? Ba ki son haihuwan ne yanzu?
"Ban sani ba."
Na faɗa ina tsumewa,
Rumgumoni ya yi yana faɗin"Sorry tsokanarki fa nake yi, ke ba ki san wasa ba?
"Ni ka ƙyale ni, ni ai na gama haihuwa da kai, ni da ka ce ina da mugun nufi a raina game da kai da matarka."

Na faɗa ina kallon shi, da sauri ya sake ni, ni na faɗa ne a wasa amma sai na ga ya wani daure fuska.

"Yi haƙ.."

"Sadiya."

Ya katse ni da kiran sunana a fusace kafin na amsa ya nuna mini yatsa yana faɗin" Ba na ce ki bar tado da wannan mganar ba? Me ya sa ba kya jin magana ne, ko so kike yi ki ɓata mini rai hankalin ki ya kwanta ko? To shike nan kin ɓata mini rai kin ji daɗi."

Ya faɗa yana ture hannuna da na ɗora a kan cinyarsa. Ya mike na yi saurin kama hannun shi guda ɗaya.

"Sorry"

Na faɗa ina leƙen fuskarsa, tun da ya kauda kai ne ya ki dariya sai na jawo shi ya faɗo gefena na sumbaci ƙuncinsa ina ƙara faɗin" Am sorry Yallaɓai na."

Lumshe ido ya yi ya buɗe kafin ya kalleni har muryan shi ta sauya."
"Me ya sa kike haka ne Sadiya?
"Ba zan ƙara ba"
"Shike nan ni ba zan yi kuskure kuma na zo na gyara daga baya ba? Na ba ki hakuri kin ce kin hakura to dawo da maganar kuma duk na mene ne? Ni fa mijinki ne, ke matata ce da soyayya ce ta kawo mu a wannan karnin, kina yi mini laufuka, kafin ma ki roƙe ni nake yafe miki saboda ba na son mala'iku su yi fushi da ke. Amma ke me ya sa in saɓani ya shiga tsakaninmu magana kaɗan bisa kuskure sai ki ma yar da shi makami a kaina? Ko don kin ga ina lalacewa a kanki da ban baki shi ya sa kike yi mini yanga?

Sai na kasa mgana saboda maganganun shi sun sanyaya mini jiki.

"Ka yi haƙuri wasa nake yi."

"Wannan maganar ba abar wasa ba ce. Ki bari kar ki ƙara ta yar da ita raina ba ya so. In kika ƙara zan kai karan ki wajen Alhajinmu."

Da sauri na kalle shi gira ya ɗaga mini kafin ya ce" Da gaske na ke yi. Kin fara kular da ni da mganganun ki."
"Yi haƙuri ni dai. So kake yi ka sa Alhajinmu ya daina misali da mu.?
"Tun yaushe? Ai kin gama karya mini wannan record ɗin a gaban Alhaji. Fisabillahi abin da kika yi  ba ki kyauta mini ba."

Na tura baki kafin na ce" To ba kai ka ja ba. Cewa ka yi na fita ba za ka hana ni ba."

"Kuma kika juya kika tafin ko kunya?

Ya faɗa yana kallona ni kuma sai na juya masa baki, caraf ya kama bakin nawa ya ja, na yi ɗan ƙara ina buge hannun shi.
"To kar na tafin? Na nuna maka muna da gidan uba muma"
"To ai kin makara. Domin Alhajinmu ya fi sona a kan ki."
"Na ga alama."
Na faɗa ina rike baki shi kuma yana yi mini dariya.

"Haka fa Alhajinmu ya zaunar da ni ina faɗa masa abin da ka yi mini ina kuka amma shi yana koro mini jawabin laifina ne a fakaice yana yabon ka."

Na karishe faɗa cikin mamaki, Yallabai ya kwashe da dariya yana mai rumgumoni cikin nishaɗi, muka yi baya shi ya jinginar da kansa a jikin kujera mai zaman mutun huɗun da muke zaune ni kuma ya yi ma kaina da jikina masauƙi a saman kirjinsa.

"Wallahi na yarda Yallaɓai Alhajinmu ya daɗe yana yin ka."

"Tun a ranar farko da na fara ganin shi nima na ji kamar mahaifina. Ba ƙarya ba ne yana ƙaunata nima ina ƙaunarsa sosai na ke ganin girmansa saboda shi ɗin adalin Uba ne sannan dattijo ne."

Ina ta mirmishi jin yana ta yaɓon mahaifina.

"Na je gabansa ina mai neman afuwa na yi miki laifi. Amma ni yake sake ba ma haƙuri da Amana. Ya ce Yusufa ka yi hakuri da Duhu ka cigaba da hakuri da ita akan wanda kake yi a baya. In ta yi maka laifi ka yi mata hukunci cikin natsuwa bayan ka yi bincike. Saboda shi yanke hukunci cikin fushi yana kawo dana sani. Kin ga dai afakaice ya yi mini nasihan na daina saurin yanke hukunci cikin fushi ba tare da bincike ba."

Ya faɗa yana wasa da gashin kaina da na yi tsifa ban yi ri ga na yi kitso ba.

"Kawu ya yi ta kambama dattakon Alhaji. Na ce ai bai ga komai ba ni ne zan bashi labarin Dattakon sa."
Sai na ɗago ina kallon shi, sumbatar lebensa na yi kafin na ce.

" Na gode."

"See your mouth kin gode mene! Nima Alhaji mahaifina ne so ki daina yi mini godiya kuma duk abin da na faɗa akan shi kyakyawan hallayan shi ne."

Na gyaɗa kaina ina faɗin" Gaskiya ne. Allah ya ƙara masa lafiya da tsawon kwana."
"Amin ya yi tsawon ran da zai ga takwaran shi in sha Allahu."
Sai na kalle shi kafin na yi magana ya rigani da cewa.
"Ina so na yi ma Alhajinmu Takwara Sadiya."
"Uhm me ya sa ba ka yi masa a wannan haihuwan na Gimbiya ba?

Mirmushi ya yi har ina jin sautin mirmushin.
Kafin ya ce" Zan iya yi masa ba wanda ya isa ya ce don me. Amma na fi so takwaran Alhajinmu ya kasance Dubu da Yusufa ne iyayen sa. Sai ya fi soyuwa a wajen ki da wajen Alhajinmu."
Girgiza kaina na yi kafin na ce" ba ka san Alhajin mu ba ne. Ko ni ko Gimbiya duka ba zai bambata mu ba."
"Duk da haka dai. Hausawa suka ce abin cikin ƙwan ai ya fi ƙwan daɗi."
Dariya na yi shima yana taya ni,na ƙara rumgume shi ina faɗin.

"I love you Yallaɓai na."

"I really like you Sadiya ta "

Na ɗago ba zato kawai ya haɗe bakin mu, yana sumbata na. Sai nima na rumƙumƙume shi da hannayena na zagaye da su zuwa maransa ina shafawa. Hannu ɗayan kuma na saman kirjinsa ina masa wasa. Ban ɗauka za mu zarce ba sai da na ga Yallabai na sabule mini ƙaramar rigar da jikina da sauri na riƙe masa hannu ina kallon shi.

"Ina so.

"Mu yi a falo."

Ya faɗa ararrabe saboda a lokacin ya ɗan kai sama can yana buƙatar matallafiya.

"Yara fa? Kar su shigo."

Sai ya tashi yana layi, ya je ya rufe mana ƙofar falo ya kashe wutar amma bai kashe kallon ba. Tun yana tafe gare ni ya cire farar vest ɗin jikinsa ya yi kuma fatali da dogon wandon dake jikinsa, kaina ya ƙariso ya jawo ni a saman kujera mai zaman mutum ɗaya ya zaunar da ni a saman jikinsa muna masu kallon juna.

Ƙura mini ido ya yi da ɗan hasken Tibin da ke falon idanuwansa sun juye sun yi ja sannan sun ƙanƙance.

"Sadiya ta."

"Uhm"

Na faɗa a ƙasan makoshi.

"Ki agaza miniiiii"

Ya faɗa cikin wani yanayi sai da tsikar jikina ya tashi da gudu na haɗe bakin mu waje ɗaya shi kuma hannayen shi na kara kaina wajen raba ni da yar ƙaramar shimin dake jikina. Ba ka jin komai sai tashin nunfashin mu sama sama.

Gaskiya Yesterday was cool. Na faɗa a cikin raina jiya nan mun yi nishaɗi da ni da Yallabai mun gamsu da juna fiye da tunanin mai tunani. Yallabai na ƙarshe ne wajen sarrafa ma mace da jan ragamar tunaninta in ta shiga hannun sa. A jiya nan haka ya ruka juyi da ni kamar waina ni ma ba a bar ni a baya ba na yi ƙoƙari sosai wajen faranta masa rai. Sai wajen ɗayan dare muka koma ɗakin mu bayan na je na ɗauko Yumna. Da asuba kuma a tiolet ya yi ɓarnan ruwan shi,  ina ya bari ya bari amma bai ji ba sai ya ɗaga ni sama sai ji na yi kawai ya baƙunce shi, ban ɗauka har a tiolet lamarin zai ba da armashi ba sai da ya nuna mini hanya. Kai jama'a ni dai na faɗa muku Yallaɓai duniya ne wallahi."

Ni dai tun da faɗan mu ya kare da Yallaɓai na manta da maganar Rahila sai da ta zo gidana na tuna na yi mata zencen me ya haɗa ta da Ya Muntari? Magana ta kawo magana na ba ta labarin artabuna da Yallaɓai, har dalilin da ya sa na ji batun su ita da Ya Muntari
Shi ne take faɗa mini kan wata budurwansa ce da ya ke kashe ma kuɗi, tana ɗauke masa hankali, ai ni na yi suman zaune kar ka raina namiji. Ya Muntari da nake gani sumu sumu kamar na Allah ashe kwallo ne..
Rahila na hawaye tana faɗa mini irin tashin hankalin da watsttatsiyar yarinyar nan ta saka ta a ciki. Ta hargitsa mata gida ba zaman lafiya ita da Ya Muntari, ta daina wanka ta daina mgana ta daina girki shine da ya gaji da magiya ya kawo ƙaranta wajen Alhaji.

"Tabdijam amma dai Ya Muntari bai da kunya."

Rahila ta jinjina kai kafin tace" Dakyar na samu ya rabu da ita
.Kuma ba shi da ƙudin auranta amma tana cinye masa kuɗi daga waje."

Ni dai har Rahila ta tafi ina ta kambama lamarin a ƙasan raina. Wai Ya Muntari tabdijam! Ban taɓa tunanin haka daga gare shi ba. Ai daga nan na daina raina wayan namiji. Yana fama da rayuwarsa amma yana ɗebe ma kansa aiki.
Allah dai ya kyauta. Yadda ni kaɗai na sani sai ban furta ma kowa ba amma na yi ƙoƙari sosai wajen taimakon yar uwata ta dawo cikin hayyacinta da shawarwari da jikina kuma da Aljihuna. Lokaci kaɗan kuma ta manta ta dawo kamar ba ita ba.
Maza maza mutanen mu.

***

Tun bayan abin da ya faru ba mu ƙara haɗuwa da Gimbiya ba sai da ta yi arba'in ta zo gidana kuma ina da tabbacin Yallabai ne ya matsa mata tun da shi ya kawo ta da kan shi. Da sunan an kawo mini Ammar na gan shi. Ban nuna komai ba na yi musu kyakyawan tarba, gidana ta yi yini tun safe har dare har yara da suka dawo makaranta nan Salisu ya kawo su tun da mamansu ta na gidana.

Da farko ta ɗan yi ɗari ɗari, amma daga baya da ta ga na nuna kamar ma wani abu bai faru ba sai ta saki jikinta. Amma ban ƙyaleta ba sai da na yi mata maganar da man kuma na yi alƙwarin ko ba jima in dai muka haɗu sai na fada mata gaskiya.
Ce mata na yi a duk abin da za ta yi to ta riƙe gaskiya da amana. Ta sani Allah na sama yana ganin ta, in har ta nufi wani da sharri to ta sani ƙaiƙayi na iya komawa kan masheƙiya. Sai ta fara kame-kame da cewa wai ba ita ce ta faɗa masa abin da ya faru ba kawai dai ya zo ya ganta tana kuka ga targaɗe a hannu shi ne ya fusata tana ta dai ƙoƙarin kare kanta na ƙarya ahalin ni da ita mun san ba gaskiya ta ke faɗa ba.

"Magana ai ta wuce. Da man na ce sai na faɗa miki gaskiya. Ki sani ni tsakani da Allah na ke zaune da ke ban taɓa nufin ki da wani sharhi ba. Ruwanki ne ki gyara alaqata da ke a zuciyarki ruwanki ne ki cigaba da ɗaukata tun farko. Amma ni dai ba zan fasa zama da ke tsakani da Allah ba sannan ba zan fasa mutumtataki a matsayin  ki na matar mijina kuma uwar yayansa ba."

"Na gode in sha Allahu zan gyara. Don Allah ki yi haƙuri "

"Ba komai. Ban riƙe ki ba, koma na ƙullaceki a baya na yafe miki. Ni da ke ba mu isa mu hana kan mu jin kishin juna ba tunda kishi gaskiya ne. Amma in ya taso mana mu koyi yadda za mu sarrafa shi akan mu. Allah ya ba mu zaman lafiya."

Ta amsa Amin duk ta ji kunya ni kuma abin da ke zuciyata na faɗa mata. Tare muka yi ma tuwon shinkafar da na yi mana da daddare muna yi muna ɗan hira jefe-jefi a bakinta ma na ke jin Nene ta yi zazzabi kwana biyu na ce ban sani ba ai da na je na duba ta. Da Yallaɓai ya dawo da daddaee ya ji daɗin ganin mu tare gwanin ban sha'awa. Ranar girkina ne saboda haka na yi kwalliya yar caras da ni ina tashin ƙamshi. Tare muka yi dinner gabaɗaya har yaran cikin farinciki abin da ba mu taɓa yi ba.

Ni ban faɗa masa wani abu ba shi ne muna falon shi tare ya kallemu ni da ita yana faɗin" Na ga chanji daga gare ku na ji daɗi kwarai."
Sai ta ce masa ai ni ce na yi mata nasiha kuma ta ji za ta gyara in sha Allahu. Ya yi ta washe baki yana jin daɗi ya taso ya rumgumeni yana sumbatana a ƙuncina na ture shi ina hararan shi.

"Ke ce jagoran mata na ko a gidan Aljanna Sadiya ta. Ni da duk abin da na mallaka duka na ki ne."

"Har wannan gidan?

Na faɗa ina dariya.
Sai ya gyara zama a hannun kujeran da nake zaune ya ce" Wannan gidan da abin da ke cikin shi ai ya zama na ki, yau ba fata nake yi ko mutuwa ko rabuwa ba wanda ya isa ya fidda ke daga cikin sa. Sai dai ni ki kore ni ma domin kin cancanta."
Ina dariya na ture shi ina faɗin"Bana son daɗin baki."
"Wallahi da gaske na ke yi "
Ya faɗa yana ƙoƙarin ya dawo ya zauna kusa da ni sai na tashi na koma kusa da Gimbiya na zauna.

" Ni za ku haɗe ma kai?

Ya faɗa yana kama baki ni da ita muka haɗa baki wajen fadin" E ɗin."
Muka faɗa a tare muna dariya sai ya koma ya zauna akan kujeran da na tashi yana faɗin" Za ku neme ni yara "

"Yara?

Na faɗa ina kallon shi sai ya zare mini ido yana faɗin" E yara ko kun girme ni ne?
Sai na yi shuru tun da na fahimci yana jin magana ne.
Saboda jin daɗi sai wajen goma ya tafi kai su gida da ya dawo bayan mun kwanta sai da ya yi mini maganar.

"Na gode Sadiyata. Don Allah ki cigaba da haƙuri. Ba ki ji farincikin da na ji ba lokacin da na gan ku tare da Daughter ba"

"Uhm"

Kawai na iya cewa domin sai na ga kamar Yallaɓai na sane a duk wasu iskancin da Gimbiya ke yi. Me ya sa ba zai mata faɗa ba? Sai ni ce zai yi ta nanata ma in yi haƙuri da ita, ita ba zai ce ta yi haƙurin ba.
Ni dai na yi masa yaƙe kawai ban nuna komai ba, sabo da kauda maganar sai na yi masa maganar zazzabin da aka ce Nene ta yi kwana biyu. Sai ya ce mini ta ji sauƙi ne shi ya sa bai faɗa mini ba amma na bari weekend sai na shirya mu je da yara mu gaishe ta na amsa masa.

Haka ko aka yi ranar lahadi muka je Gwammaja tun safe muka yini. Da man su Baby sun yi hutun Tahfez saboda gabatowar azumi, Nene ta ji sauki amma jikinta ba karfi ina gidan sai ga Halima wataƙila saboda idanuwan Nene ne ya sa ta gaishe ni, nima saboda mahaifiyarta na amsa. Ni saboda ita a bangaren Maman farko na yi yini na, sabo da ba na son abin da zai haɗa ni da yarinya. In ta neme kawo mini wargi ba zan ɗauka ba. Muna gidan har dare tun da Yallabai ne ya kawo mu sannan shi ya ce zai biyo ya ɗauke mu. Motata a gida na barta. Tun la'asar Halima ta tafi gida shi ya sa na koma ɗakin Nene, duk da ba ta fito fili ta furta mini ta ji maganar hatsniyar da muka yi a gidan sunan Ammar ba a maganganunta na san jirwaye take yi mini mai kama da wanka. Hausawa suka ce ruwa cikin cokali, ya ishi mai hankali wanka.

Ta yi ta ba ni haƙuri ne, tare da nuna mini na cigaba da haƙuri ina kauda kai. Sannan ta gangaro kan maganar Halima ta na nuna mini na yi hakuri da ita akwai yarinta a tare da ita, da ta ji labari ta yi mata faɗa sosai tun rashin kunyar da ta yi mini na farko. Ni dai ban ce komai ba illa to, amma ina ganin beken Nene, Haliman ce yarinya? Mata da mijinta da yayanta ai ta san abin da take yi. Na dai nuna ma Nene komai ya wuce amma a ƙasan raina na kudiri niyyar ba zan bi ƙanwar miji ta samu damar cin kasuwa a kaina ba. Ni ko yayar miji na ga tana tozartani kama kaina nake yi ballanta ita ƙaramar alhaki.

Mune sai goman dare Yallaɓai ya biyo muka tafi gida. Mu dai mun tsaya mun ci tuwo shi kuma sai da na dafa masa Tea da Indomie ya ci kafin ya kwanta. Sabgogin gaba na kawai na cigaba da yi ga matsowar azumi, shi ya sa na saro inears da yaawa wannan sallar har da mayafai da takalma na yara da manya. Yallabai ya ba ni 100k rance a cewarsa zan biya shi in na haɗa ribata na ce na ji na karba da shi na samu na ganganɗa na ɗinko hijabai diffirent ɗinki kala kala sama da hamsi suna gida sai dai da an saka oder na saka a leda na naɗe Baby na taya ni muna sawa a jaka ko a leda. Tun da Jidda na makaranta sai Baby ke taimakona yanzu. Kuma Alhamdulillah, ana siya sosai ina samu ga Jidda ma tana saka mini a status tana yi mini talla har yan makarantan su sun ce suna so. Irin mata yan dapertment din su, akwai wata ma course ɗin  ɗaya sannan ɗakin su ɗaya Ummu Salma Hamza ɗiyar Iyan

36 / 55