#Asli Smasher.
[2/9, 10:54 PM] My number 1: 30...
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
*Subscribe and read happily without feeling any guilt.. It's ₦200 via 0060746882,Hauwa Muhammad Usman,Access Bank or MTN recharge card/VTU and then show ur evidence of payment through my whatsapp account 08165726609 to be added in the paid group.*
Since ta wucesu hankalinsa ya bar kan hiran da suke yi,ya d'auki wayarsa yana operating,Manar tana kwance cikin d'akin taji shigowar text a wayarta,tana dubawa taga Waleed ne "Hi *LILAC!"* Shi ne abunda ya turo mata,wani murmushi tayi tace "hello!" Yana ganin reply d'inta yayi ajiyar zuciya,he never thought za ta amsa masa,yace "wane laifi na maki d'azun kika harare ni?" Sanda ta gani kamar yana gurin ta d'aure fuskarta tace "ba kai ne da Daddy yana tambayar ka ba ka wani basa amsa" ya zaro idanunsa yana sakin murmushi yace "wane tambaya ne?" K'in fad'a masa tayi,yayi murmushi sanda ya gane abunda take nufi yace "ba kya so nace komai ne?" Tace "ehh" dariya yayi daga haka ya tashi ya fita parlon ya kirata,tana ganin kiransa tak'i d'auka can da ya katse ta tura masa text "ni ka daina kirana fushi nake yi" yace "da ni kike fushin!" Tace "ehh" yayi murmushi bai sake kira ba ya koma parlon ya zauna yana sauraren hiran da su Daddy suke yi. Washe gari Saturday tun asuba da suka tashi a gidan babu wanda ya sake kwanciya aka fara girke²,Mother da Aunty sai maids kad'ai suke girki a can babban kitchen dake backyard,kayan soye² kuwa tun daren suka gama su,Manar da Ameerah sai Dadda su kuma suna ta had'a bags da za'ayi rabo a can b'angaren Dadda,Mama kam daga ita har y'an gwal d'inta ko kyallinsu babu a gurin,sai da su Aunty suka kusa gama aikinsu around 9am,ta fito sai kai wa da kawowa take tana jira wani cikin su ya tanka mata,ta shiga ta fita ya fi a k'irga da taga babu wanda ta ce mata ci kanki,tayi tsaki ta bar gurin,Mother ta d'aga kai ta kalleta tayi murmushi,Aunty ta kalli Mother tana dariya tace "Aunty Mammy ba ki da dama fa" Mother ta sake yin dariya bata dai ce komai ba suka ci gaba da aikinsu,kafin 10am sun gama komai suna dai zaune ne kawai,can Ameerah da Manar suka shigo kitchen d'in sanye da sababbin d'inkin da Amaar yayi musu na ankon sauka,d'inkin Manar da Ameerah iri d'aya da hijab d'insu fari har k'asa,sosai suka yi kyau,Aunty tana kallonsu tayi murmushi tace "y'an mata na kun yi kyau sosai" suka yi murmushi suka ce "mun gode Aunty" Mother tace "toh za ku wuce ne ko tare za mu tafi?" Manar tace "a'a mu za muyi gaba sai kun taho" Mother ta gyad'a kai tace "to kuyi sauri dai,Allah tsare sai mun zo" Manar kamar za tayi kuka tace "mother za ku zo da wuri please?" Mother ta harareta tace "a'a late za muzo" dariya ta kyalkyale da shi ta juya da sauri ta kama hannun Ameerah tace "let's go Sis.. Aunty mun tafi" suka yi musu sallama suka tafi,a parking space suka had'u da su Deejah sun fito suma,basu kulasu ba suma basu ce musu komai ba suka shiga mota,jiniyar motocin sojoji da ya cika estate d'in tun basu k'araso ba Manar ta fara dariya tace "tabb' Daddy zai cika gurin saukarmu da yaransa" Ameerah tayi murmushi tace "yeah! And za'a samu security kuma" driver ya ja su zuwa islamiyyarsu,sanda suka k'arasa a cike suka tarar da gurin da mutane an baza sojoji a ko ina,Daddy da Abba suna cikin manyan bak'in da aka karrama,Azaan da Waleed a bayan su sai Amaar da suke tare da su Asad da aka je da su gurin saukar,sosai gurin ya had'a manyan mutane ba na wasa ba,basu wani jima ba sosai su Aunty da mother suka k'araso suma,sosai Manar ta ji dad'in ganinsu don ita da Ameerah aka zab'a cikin matan da za suyi karatu,tunda suka je wajen taga Waleed da Azaan take sakin murmushi,seeing her family a gurin ya k'ara bata nutsuwa,but jama'a da suke gurin kad'ai ne suka sa take jin gabanta yana fad'uwa,sai dai bata sake yarda ta kalli kowa ba,aka fara kiranta ta mik'e cikin nutsuwarta Dadda da suka zo tare da su Mother sai washe baki take,hak'orin makkanta hud'u suka bayyana,cikin jin dad'i take fad'awa tsofaffin da suke tare "jikata ce aka kira" Baba Tasallah itama tana gurin dan Dadda ta gayyatota taron sai murna suke,sanda ta fara rera k'ira'anta na hafs her tajweed da yanda take a nutse mutane gaba d'aya sun mayar da hankali kan karatun da take Dadda sai gyad'a kai take tana fad'in "Allahu akbar.. Kunji yanda take karatu kamar balarabiyan makkah" tana gamawa gurin ya d'auki takbiir,Daddy da Abba babu wanda ya kaisu farin ciki,tana gamawa aka kira wani namiji yayi sai Ameerah itace last,dama su uku aka zab'a,Dadda dai sai murna take an zab'i jikokinta biyu,nan taita bawa tsofaffin da suke gurin labarin zaman su na saudiyya,Mama bata zo gunrin ba sai around 12pm lokacin har an raba allo anyi darasu ana shirye²n tashi,sosai makaratar ya samu kyautar kud'ad'e daga manyan mutanen da suka halarci taron,Daddy ma 1ml ya bada,ana gama rufe taron su Manar suka tsaya d'aukan pics da friends da malaman su na makaranta,after then suka shiga cikin family suka dunga d'aukan hoto a gurin,sojojin Daddy duk sun zagayesu kamar su kad'ai suka fi kowa a gurin,can Manar ta juya tana kallon Waleed dake zaune ba shi da niyyar tashi ta matsa kusa da shi a hankali ta rik'o hannunsa tace "Yaya taso mu yi hoto" ya dunga kallonta da sexy idanunsa yana sakin mata k'ayataccen murmushinsa a hankali yace "sai yanzun kika tuna da ni a gurin?" Ta turo baki tace "ni dai ka taso muyi" yayi murmushi yana tsokanarta,bata ce komai ba ta dunga jansa sai da ya tashi,photographer ya dunga d'aukansu Mama da su Deejah da suke tsaye gefe sai kallonsu suke cike da jin haushi saboda babu yanda basu yi da Waleed yazo suyi pics ba ya k'i tashi,Mama ta gyad'a kai cike da takaici tace "za ka ci ubanka da ni kake zancen" sanda aka tashi ma motar Waleed su Manar suka shiga ya wuce da su gida,driver da ya kawosu ya d'auko su Dadda da tsofaffin k'awayenta,Waleed yana driving Manar sai hira take masa,yana sakin murmushisa har suka isa gida,yayi parking Manar ta kallesa a hankali tace "Yaya yaushe za ka ba ni gift d'ina?" Yayi murmushi yace "sai anjima idan na dawo,yanzu kije ana jiranku" har ta fita motar za ta wuce sai kuma ta tsaya tana kallonsa cike da tuhuma tace "ina za kaje toh kai?" Yace "zan je gida na dawo" wani kallo ta dunga masa,lokaci d'aya haushi ya cikata saboda dama bata ga Afiyah ba duka a gurin saukar she thought ko ita zai koma ya d'auko,ta masa wani kallo dabsauri ta juya ta bar gurin,dariya yayi mai sauti kafin ya kashe motar ya fito ya bi bayanta zuwa b'angaren Dadda da zuwa lokacin babu mutane sosai,tana shiga d'akinsu ya biyota,ta juya tana kallonsa fuskarta a d'aure tak'i masa magana,ya k'arasa inda take yana kallonta yace "what happened?" D'auke kanta tayi ta fara kokawar cire hijab d'in saboda zafin da take ji,za ta wuce bathroom ya rik'ota,tayi saurin waigawa tana kallonsa,yace "am asking!" B'ata rai tayi tace "nothing" ya dunga kallonta yace "ban yarda ba" kamar za tayi kuka cike da jin haushi tace "wai Yaya dan ka ga ba na son kana min maganar matarka shisa sai ka wani dunga min,ni Allah duk ranan da ka k'ara min haka sai na daina kulaka" zaro idanunsa yayi yana kallon yadda ta rufe idanu tana masa magana cikin fad'a,yace "ohhh! Nooo" wani kallo ta masa ta kwace hannunta za ta shige bathroom ya rik'o waistband d'inta da sauri ya dawo da ita ya jiginar da ita da bango yana kallonta yace "I'm very sorry my lilac" d'aga kai tayi tana kallonsa ta k'i cewa komai,ya marairaice yace "please mana" shammatarsa tayi ta tsuguna ta fice ta k'asa bata sake ce masa komai ba tayi shigewarta bathroom,yayi murmushi a hankali yace "i said i'm sorry fa" tana daga cikin bathroom d'in ta turo baki tace "na ji.." Dariya ya fita yana yi,yanda ta amsa yasa shi jin kansa kamar zai nutse saboda shauk'in da ya shiga,yana fitowa b'angaren zai wuce suka had'u da Daddy dake fitowa,kafin ya wuce Daddy ya kirasa "Waleed!" Ya amsa yana k'arasawa inda yake ya d'an rusuna,Daddy ya d'agosa ya d'ora hannunsa a saman shoulder sa suna tafiya cikin compound d'in gidan kamar wasu friends yace "ina za kaje yanzun?" Waleed yana shafa kansa yace "zanje gida na dawo" Daddy yace "alright! But za ka tsaya yanzun muna da guest idan sun tafi sai ka tafi ko?" Waleed yace "toh uncle" tare suka bar gidan da Daddy a motarsa zuwa guesthouse d'insa sai soldiers d'in Daddy da suka bisu. Ba su dawo gidan ba sai after maghreb,lokacin Manar ta fito bedroom bayan ta yi wanka ta canza kaya tasa wani lightweight pyjamas purple ta d'ora k'aton hijab akai,Dadda sai hira suke a parlor da su Amaar ta wuce su ta fita daga gidan,b'angarensu ta shiga ta samu mother tana jera abinci kan lallausan carpet dake parlon,ta shiga ta taya ta suka gama,dai² lokacin Daddy suka shigo tare da Waleed,ta musu sannu da zuwa,Waleed dai sai kallonta yake bai iya cewa komai ba,mother tace "sannu da zuwa,ga abinci" k'arasawa Daddy yayi ya zauna,Waleed dai bai zauna ba yace "Uncle bari naje" Daddy ya d'ago kai ya kallesa yace "dawo maza ka zauna,idan munyi dinner sai ka wuce" Manar dai sai kallonsa take yi ganin ya k'i kallonta duk ta damu,da kyar ta zauna kusa da Daddy suka ci abincin su uku,har suka gama Waleed bai yarda ya kalleta ba,ya tashi ya yiwa Daddy da Mother sallama zai fita,da sauri Manar ma ta mik'e ta bisa tana cewa Mother "na tafi gurin Hjy" Mother tace "alright! Za ki dawo ko can za ki kwana?" Tace "A'a zan kwana a can" mother tace "okay! Allah ba mu alkhairi" ta fita da sauri ta bisa,ganin har ya wuce parking space ta kwalo masa kira "Yaya!" Tsayawa yayi ba tare da ya kalleta ba ta k'arasa da d'an gudunta fuskarta d'auke da damuwa tace "Yaya me ya faru?" 'Dago idanunsa da suka yi mugun ja yayi yana kallonta,ta rik'o hannunsa da sauri a rikice tace "Yaya please talk to me" lumshe idanunsa yayi ya bud'e yana kallonta wasu hawaye suka ziraro daga idanunsa,ya kai hannunsa ya gogesu da sauri ba tare da ya yi magana ba ya juya ya bud'e motarsa ya shiga,sosai jikinta ya mugun yin sanyi,yanayin da ta gansa a ciki yasa ta kasa k'wak'waran motsi ta dunga kallonsa ya had'a kansa da steering wheel,idanunta cike da hawaye ta zagaya d'aya side ta shiga ta rufe,ba kad'an ba yanayin da ta gansa ciki ya tsorata ta,muryarta yana cracking ta kai hannunta ta d'agosa tace "Yaya! Please talk to me, what happened?" Sauke kansa yayi jikin shoulder ta yana sauke ajiyar zuciya a hankali yace "Manar!" Da sauri ta amsa "na'am" yace "ba kya so na ko?" Girgiza masa kai ta dunga yi tace "a'a! Ina son ka Yaya" d'agowa yayi da sauri yace "k'arya kike ba kya so na" kuka tasa masa tana kad'a kai tace "believe me Yaya" saurin rik'o fuskarta yayi da hannuwansa biyu yana kallonta hawaye suna sauka kan fuskarsa yace "ki fad'a min gaskiya Manar,kina so na ko a'a?" Cikin kuka tace "i love u Yaya" wani murmushi yayi mai tafe da hawaye ya girgiza kansa yace "idan kina so na why kika bawa wani damar aurenki?" Saurin kallonsa tayi tace "ni Yaya wa na bawa dama?" Strictly yace "Azaan!" Wani fad'uwa taji gabanta yayi tace "Yaya" da sauri ya d'aga mata hannu yana goge hawaye yace "enough Manar,ba sai kin ce komai ba,na fahimta yanzun.. Allah ba ku zaman lafiya.." Kuka ne ya kwace mata da sauro ta fad'a jikinsa ta k'ank'amesa,ya dunga kallonta ya kasa ce mata tayi shiru,a hankali ya d'agota ya zaunar da ita ya juya back seat ya d'auko wani jaka na kwali ya mik'a mata,muryarsa a sanyaye yace "ur gift" da yaga ta kasa karb'a ya d'ora mata kan thighs d'inta yace "kije gida kada aga kin dad'e" kallonsa ta dunga yi ta kasa cewa komai ya kai hannunsa ya bud'e mata k'ofar ya zuba mata idanunsa,da kyar ta sauke k'afarta waje tana waiwayensa ta fita ta rufe masa motar,yana kallonta a hankali yayi mata murmushi yace "bye.." Ya tada motarsa,har ya fita daga gidan bata iya yin k'wak'waran motsi ba,sai da taga ya fita get keeper ya rufe,ba ta gano ko kyallinsa kafin ta juya da gudu ta bar gurin tana kuka..
#Afuwaan habibtiies kwana biyun nan uzuri suka min yawa,and za muyi biki cikin satin nan,sai kunyi hak'uri da ni,har mu gama..
#Asli Smasher.
[2/11, 9:54 PM] My number 1: 31...
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
*Subscribe and read happily without feeling any guilt.. It's ₦200 via 0060746882,Hauwa Muhammad Usman,Access Bank or MTN recharge card/VTU and then show ur evidence of payment through my whatsapp account 08165726609 to be added in the paid group.*
Da Azaan ta fara had'uwa a wajen apartment d'insu kafin ta k'arasa gidan Dadda,yana mata magana ko saurarensa bata tsaya yi ba ta shige tana kuka,ya bita da kallon mamaki har ta shige,then ya wuce yana sakin wani murmushi,tana shiga d'aki ta fad'a gado tana kuka,har Ameerah ta shigo bata sani ba sai da ta dafa ta a rikice take tambayarta "sis what happened?" Cikin kuka Manar ta d'ago idanunta da suka yi ja tace "Yaya ne" Ameeah tace "me ya had'a ku?" Tana share hawaye ta mata bayanin abunda Waleed yace mata,Ameerah ta sauke ajiyar zuciya tace "to ke mene ne yasa ki damuwa tunda ba kya sonsa?" Wani kukan ta fashe da shi tace "ai baza ki gane ba" Ameerah tace "mene bazan gane ba?" Ta mata banza bata k'ara kulata ba can ta d'auki wayarta ta dunga kiransa amma bai picking ba,dole ta hak'ura ta ajiye wayar tana sauke ajiyar zuciya. Washe gari da rana ta shiga part d'insu har lokacin she's not moody,ta tarar da mother tana jera abinci a kan rug,ta k'arasa ta gaisar da ita tana k'irk'irar murmushi,mother ta kalleta tace "ga abincinku nan ke da Daddy" ta k'arasa ta zauna kan carpet d'in tana bud'e warmers d'in tayi d'an murmushi,Daddy ya fito daga d'aki ya k'araso cikin parlon ya zauna saman lallausan carpet d'in shima yana kallonta yace "sweetheart!" Dariya tayi tace "Daddy good afternoon" yace "afternoon dear,how are u?" Tace "alhamdulillah!" Daddy yana kallonta yace "I'm proud of u sweetheart! Keep it up dear" tace "thank u Daddy,but ni ba ku bani gift ba,duka gidan nan Yaya kad'ai ne ya bani" murmushi yayi yace "let lunch first" ta d'auki plate ta zuba musu mother tana zaune a parlon har suka gama cin abincin,Daddy ya kalleta yace "hope u will also pass ur up coming exams!" Ta gyad'a kai tace "sure Daddy" Daddy yace "good sweetheart" d'an k'aramin box ya fito da shi daga pocket d'insa ya mik'a mata yana sakin murmushi yace "this is my gift" tayi dariya tana kallon mother tace "mother saura na ki" murmushi mother tayi tace "ki fara bud'a wannan muga abunda Daddy ya baki" ta mak'ale shoulder a shagwab'e tace "ni ki ba ni naki na had'a" mother tace "alright!" Ta shiga d'aki ta d'auko wani jaka mai kyau,Daddy yana kallonsu yana sakin murmushi,ta mik'a ma Manar jakar hannunta tace "my gift for u dear! Allah sa na tsoron Allah ne" tace "ameen!" Ta karb'a ta had'a su guri d'aya,tana sakin murmushi tace "Daddy ka ajiye min yanzu zan dawo" yace alright" ta fita da sauri ta nufi part d'in Dadda,jakar da Waleed ya ba ta jiya ta d'auko ta taho part d'in,tayi sallama ta shiga,Daddy yace "me kika samo mana?" Tayi dariya tace "kyautan da Yaya ya bani ne jiya" ta zauna jikin Daddy ta fara d'auko na Mother tana sakin murmushi ta bud'e ta d'auko madaidaicin Qur'an mai kyau sai littataffai k'ananu biyu,d'aya Azkhar ne,d'ayan kuma Addu'a'u min-kitaab was-sunnah,Manar tayi murmushi tana kallon Qur'an d'in tace "wow! Thank u Mother,i love it and i love u too" mother ta dunga kallonta ganin yanda tayi murna da gift d'in tayi murmushi itama tace "really?" Tace "sure mother" d'an k'aramin box da Daddy ya bata ta d'auka tana cewa "saura na Daddy bari muga" ta bud'e box d'in key ya fad'o,ta bisa da kallo ta kai hannu ta d'auka,so excited tace "Daddy!" Tana d'aga key d'in motar da ta d'auko tana kallo tace "u brought me a car Daddy?" Mother sai kallonsu take cike da jin dad'i,Manar ta rungume Daddy tace "i love u Daddy,Allah ya k'ara girma" murmushi yayi yace "Ameen,za a kawo motar da yamma" Manar da ta rasa me za ta ce saboda murna tace "toh Daddy,Allah ya kai mu,thank u so much,Allah saka da alkhairi" yace "ameen" ta juya tana kallon mother dake sakin murmushi tace "mother kinga gift d'in Daddy na" mother ta gyad'a kai tace "yeah! Muna godiya yallab'ai Allah k'ara girma" Daddy dai bai ce musu komai ba sai murmushi yake,ta d'auki jakar gurin Waleed ta bud'e ta fito da manyan turaruka masu tsada da kwalin sabon waya k'iran iPhone 12,wani k'ara ta saki ta mik'awa mother key d'in da kwalin wayarta tsabar farin ciki ta rasa me za tayi kawai ta fara tattare warmers da plate d'in ta kai kitchen bata fito ba sai da ta wankesu,Daddy sai kallonta yake yana sakin murmushi mother ma tana mata dariya,Daddy ya tashi ya bar parlon yana cewa mother "yarinyar kin nan aka sake ba ta want gift d'in za ta iya tafiya zariya" daga haka ya shige bedroom d'insa,mother said dariya take musu. Da dare lokacin ta fito b'angaren Dadda suka had'u da waleed za shi gun