Kutkale Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sajida Niger Category :  Love

Chapter   40 / 54

117K to 120K   out of 159.5K words

hawa sai shi

Su duka a kasa suka zazauna suka tankwashe kafafuwansu

Sai da malan ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce" tsarki ya tabata ga Allah ubangiji subahanahu wata.ala,
Alhamdulilah,
Kamar yanda kuka ji, an daura auren mamana yau bisa sadaki mafi kankanci jika goma , sai kyautar uwa da ta uba mota kirar Ferari daya daya, sai motar jigilar kaya wato babar mota ta uba, sai kujerar haji in sha Allah ta uwa uba da yan uwanta da iyayenta wato ku

A tare suka kalli juna sannan suka kale shi

Malan ya ci gaba da fadin" za.a kawo lefenta jibi idan Allah ya nuna mana sannan za.a saka bikin kusa kamar yanda kuka sani bana taron wunin biki a gidana, ba.ai min kade kade bale wata diner, almajirai nake tarawa a wuni ana sabkar alkur.ani mai girma da neman zaman lafia a wajen Allah

Shiru ya yi yana kallon yannayin kowace, shirun da ya biyo baya daga garesu ne ya saka shi guara babar rigarsa yana sauraron su

Hajia mama ce ta muzguta ta ce" uhum

Malan ya saki murmushi yana kada kai, sauraron su kawai yake yana jiran jin fatan alkhairi daga bakin dayarsu, aman cikin ikon Allah shiru ba wace ta yi fatan alkhairi

Dubansa ya kai wajen mama ya ce" Ramatu

Da sauri ta dago da dubanta ta kali malan

Malan ya gyara zama ya ce" daga yau, na umarce ki da ki nuna kulawa wa yayan da kika haifa, na soke maganar jin kunya kawar da kai ko kara, na umarce ki da ki buda baki ki yiwa yarki adu.a, ina so ki kula da shirye shiryen tarewar yarki!

A karo na biyu ta kuma kallonsa, kwarai ba wasa da gaske malan yake, da gaske yake ba wasa a maganarsa

Hannayenta ta hade ta shiga murzawa a hankali ,
Cikin nutsuwarta ta ce" Alhamdulilah, Allah ya basu zaman lafia

Malan ya gyada kansa yana murmushi ya mike ya shige ba tare da ya kuma tankawa kowace ba

A hankali ta mike itama dan ficewa a dakin dan gaba dayanta hankalinta a tashe yake , bata taba irin haka ba, ba.a taba haka da ita ba, hasbunallahu wani.imal wakim

Tana fita a dakin ta kama sauri, aman cikin ikon Allah sai da hajia mama ta cin mata, matar sosai dajikantaka ta fara bayana a jikinta aman dan tsabar fitina ta riko hijabin mama ta ce"malan ya yi haka dan ya nunawa duniya daban take da sauran ko? To kudinsa baya damuna! Sannan bana son kujerar makar domin ni ba zan je bautar Allah da kudin haram ba!

Ita dai mama tsayuwa ta yi sai da ta gama ta sakar mata hijab ta shiga daki

Tana shiga ta ga wayam ba Hafsat,
Da sauri ta daga kafarta ta shiga dakinta

Tarar da ita ta yi tsaye, daga ita sai dan dogon wando da rigarsa sai kai kawo take,
Yannayin fitina da neman balaki ya bayana a tare da ita

Kallon tsaf ta yi mata kafin ta tabe baki, lale Hafsat ta raina mata hankali, kuma ta yarda da ake cewa likita ya fi kowa rikicewa idan abin ya shafe shi.

Sai da ta gama kallonta sannan ta ce" ki lulube jikin ki, daga yanzu bana son na kuma ganninki ba da lulubi ba kafin a kawo magungunnan ki

Da kallo ta raka maman nata, iyeah? Shi ne abinda ta fada

Da sauri ta warto wayar nata, karfe goma sha biyun dare ne fa aman da yake ranar ta zo masu wani iri du gidan malan yara kananu kawai suka samu rintsa idannuwansu

Wayar ta danna ta danna masa kira

Ta yi ya kai sau hudu kafin ya daga da wata irin murya

Sai da gaban Hafsat ya fadi domin muryar wani irin kasa kasa, sannan bata fita da kyau

A hankali ya ce" Hafsat

Hafsat ta kara rintse idannuwanta ta kai zaune saman bed din dakinta
Niyarta ta daga murya ta darza rashin mutunci sai gata da sasauta murya ta ce" Abdul, dan me zaka min haka? Me na maka ne wai ni? Dan me zaka saka a aura maka ni bayan ka san da wanda ke so na yake shirin zuwa ya aure ni? Yanzu idan ya zo sakina zaka yi a kara aura min shi ko me?


Abdul ya kara lumshe idannuwansa yana sauraronta , a nitse ya ce" *ni ban aure ki dan na sake ki ba*

Me kake nufi da baka aure ni dan ka sake ni ba? Wani irin aure kake jiran yi da ni haka? Baka so na Abdul, bana son ka!, dan me ka min haka? Ta fada muryarta a sanyaye haka kuma tana rawa rawa

Abdul ya sauke ajiyar zuciya, a hankali ya ce" *na san bakya so na, ban roki ki so ni ba, Hafsat baki ga lokaci ba ne ni? Lokacin neman nutsuwa ne, idan kuwa zaki iya....ina nufin idan har kin san kina bukata, a yau kin saka haka a ran ki .... sai na sauka daga nan na zo in hau naki bed din*

Abdul ya karashe yana mai duban Na.ima dake kwonce kusa da shi

Shiru ya ji wayar, ba magana dan haka ya dubi screen din,
An kashe, murmushi ya yi yana girgiza kansa, dubansa ya kai wajen Na.ima, baci take kashirban, baiwar Allah, a gaskiya yana tausayinta, shi baima taba tunanin ta yanda zai fadi abu sai wannan lokacin

Kwonciyarsa ya gyara yana mika, a hankali ya furta" *na san bakya so na Hafsat, na jima da sani....sai dai ba zan iya sakin ki ba, ke na yiwa rabon wani garaje dan Allah ya kashe ni kafin ya fito daga tsatson ki ....Hafsat idan na rabu da ke ni kuwa na rayu a yaya?*



Bayan kwana biyu aka kawo lefen Hafsat
Lefen da ya kara kashe bakin mutanen gidan malan kowa sai dai ya labe daga daki yana leke ba um ba umum,
Anguwa du an dauka, maganar uwar malan kawai ake, da yawa na fadin alkhairin da yawa na kushewa

Kwana biyar kennan da maman malan ke zaune da auren Abddallah a kanta,
Bata kuma jin duriyar BS ba, haka kuma shi kansa abdul din daga daren da ta yi kiran nan nasa da ta kashe bata kuma nemansa ba

A yau ta tashi ta gama shiri da sanyin safiya cikin nikaf da abin hannun da mama ta bata, shima an ce dole sai ta je da kanta gidan mai dinki ne, hakan ya saka mama ta ce maza ta je ta dawo su yi dilkar safe domin ko dilkar basu yi ba

Har ta yiwa mama salama mama ta dawo da ita

A hankali ta ce" kin nemi izininsa ne?

Da sauri ta kalli mama cike da mamakinta, izini? Wai izinin wa?

Mama ta daure fuska ta mika mata wayarta da aka karbe du idan za.ai mata dilka ake amshewar

Amsar wayar ta yi ta kuma kallon mama gani ta yi ta tsareta da kallo dan haka ta danna wayar ta shiga kiran numbersa

Sabon wulakancin da take gani ya dauka yanzu ne ya yi mata dan sai a kira na biyu ya daga sannan ya ki yin magana

A hankali ta yi salama domin mama na kallonta ido cikin ido

Amsawa ya yi yana mamakin salamar daidai ya tsaya wajen danja

A hankali ta ce" an aike ni wajen mai dinki zan je na dawo

Ajiyar zuciya ya sauke kamar wanda ya yi tsere, a hankali ya ce" ki jira

Bai karasa ba ya kashe kiran , ta bi wayar da kallo
Sarai mama ta fahimci abinda ya ce dan haka sai ta dauko kujera ta zauna a kofar dakin mama

Ta kusan minti ashirin a zaunen nan, tana yi tana duba agogon wayarta tana kuma kallon hanyar fita

Kanshin turaran da ta jiyo ne ya sakata yin shiru ta ki motsi

A hankali yake takowa har ya iso inda take zaune
Bai yi mata magana ba sai tura kofar da ya yi ya yi salama

Da mamaki ta dago tana kallon wai da gaske dakin maman zai shiga? Yau ta ga ikon Allah, mazan yayunta basu taba shiga dakin mama ba sai yau shi bakon jiya zai shige har dakin mamanta

Mikewa ta yi ta yi gaba dan har an fara leke, bata son a bata mata rai da safiyar nan

Sai da ya gama gaishe su ya fito ya fita wajen

Ganninta waje tsaye ya sosa ransa, aman bai nuna a nan ba ya bude ya shiga itama ta bude ta shigan

A hankali ya tayar da motar ya dauki hanya

Batai masa magana ba sai murza yan yatsunta da take,
A hankali a hankali har suka karasa wajen da bata fada masa ba sai dai gani ta yi ya kaita ta tabata mama ya tambaya

Fita ta yi ta shiga akai mata aune aunen da za.ai mata baki daya ta fito ta dawo motar

Dagawa ya yi suka fara tafia,
Suna tafiar ya canza hanya a hankali ya ce" bana so kina fita Hafsat,

A hankali ta dan kale shi sai kuma ta kawar da kan nata

Hafsat talk to me;

Dubanta ta kai wajensa, sai kuma ta shiga shashekar kuka,
Kuka take a hankali a hankali wanda ya saka shi ja ya tsaya a cikin kwanar da suka shigo sabuwar anguwar yan gayu ba wasu mutane a waje da yake safia ce sai jefi jefi du suna gida suna baci

Mitar ya tsayar kasan wata shuka,
A hankali ya karkata yana kallonta,
Rufar fuskar nata ya dage ya cire mata baki daya yana kallonta

Gashin idannuwanta sun yi gazar gazar da su, sun shiga idannuwansa har sun zarta

A hankali ya fora yatsarsa saman girarta ya dan shafa kafin ya lumshe idannuwansa,
Muryarsa ya sanyayar ya ce" menene?

Hafsat ta dago da dubanta a hankali ta dube shi,
Muryarta ta sanyayar ita din ma ta ce" Abdul, ina BS ya shiga?

Abdul ya tsura mata ido, gabansa ne ya ji ya fadi lokaci guda,
Bai yi shishigi ba kuwa? Bai sako kansa wajen da zai zauce ba kuwa? BS? Tare fa ka gansu Abdul, shin wannan damuwa da shi ka san da tana son sa, idan fa bayan so din Hafsan ka ta yarda da BS ne?
Gabansa ne ya kara faduwa, hankalinsa ya ji ya tashi a hankali ya saka hannayensa bibiyu ya kamo fuskarta,

Matso da fuskar tata ya yi ya samu da kyar ya hada ido da ita,
A hankali ya ce".......



=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?=?B?


>???=???>???=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>???=???>???


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




5?? 3??



A hankali ya ce" kin kasance mai fadin gaskiya Hafsana,
Ki fada min, a cikin mazan da suka ringa kawo maki hari shin shi ya samu galaba a kanki ko menene wannan damuwar da shi?

Sai da ta wanna idannuwanta a cikin nasa sannan ta saka hannnayenta biyu ta janye hannunsa

Sakar mata fuskar ya yi yana kallonta, a hankali ta ce" haba Abdallah, me zan yi kwadayi da zaman yau da kulun? Na zauna da kai Abdallah! Bana son irin rayuwar nan, rayuwar da ba kula ba yanci? Ni wa na fi da zan yi tunani ai ni ce zaka waiwayeni? Ni ta nawa ce? Abdul shin ka taba so a rayuwarka?
So wani abu ne mai nauyi mai wahala, Abdul ni na taba so, so yakan saka mutun tsalake maganar manyansa, Abdul Bashir ya nunan so, ya bi ni sau da kafa...ya waka min, ya yi hakuri har na samu kaina sannan ya zo har gidanmu ya nemi soyayata da aurena
Shin me ya tsayar da shi? Ina cike da zulumin abinda ya tsayar da shi mai girma ne, Abdul du irin zagina da ake a kulun sai ya furtan kalmar so

Idannuwansa ya lumshe ya kuma budewa yana kallonta

Sai da ta sauke ajiyar zuciya ta kale shi ta ce" ban san kansu mazan ba bale har na ware shi dan hakan! Ka kaini nesa Abdul, ka yi yawo da ni sama a zuciyarka ka ajiye ni malan kar ka saka na kasa sauka=?D?
Ta karashe tana mai turo masa bakinta sannan ta gyara zama a cikin motar

Murmushi ya yi kawai ya girgiza kansa ya tayar da motar ya harba hanya

Ashe wajen da zasu je din babu ma nisa da inda ya tsaya dan kawai ta kwasan masa kukan rigima ne ya rikice ya ja ya tsaya kar ta halaka shi, da zata san irin abinda yake ji da bata yi haka ba

Kofar gidan ta karewa kallo, tamfatsetsiyen get ne da sojoji biyu a kofa

Buda kofar kawai suka yi ba tare da sun tsaya binciken wanda ya zo ba hakan ya tabatar mata da sun san ko waye a cikin motar

Sai da ya isa ciki sosai ya yi parking

Fita ya yi ya tsaya yana kallon kofar falon

A hankali ta fito bayan ta saki nikaf din fuskarta
Takawa suka yi tana biye da shi har suka shiga falon

Gabanta ne ta ji ya fadi sakamakon hango kanwar mamansa, kuma mahaifiyar matarsa hakimce saman kujerar falon tana amsa waya

Tana ganinsa ta kashe kiran tanai masa oyoyo

Murmushi ya yi ya karasa har inda take zaune ya dan duka ya bata peck a goshinta itin gaisuwar larabawa sannan ya zauna sosai kusa da ita ya rike hannayenta suna gaisawa

Itama cike da kulawa take amsa gaisuwarsa kafin ta tambayi wajen su na.ima

Sai da suka gama gaisawar ya dan waigo sai ya ga Hafsat na tsaye a bakin capet din bata shiga ba ta zauna

Mikewa ya yi ya karasa inda take tsaye ya kamo hannayenta ya janyota a hankali har wajen zama ya zaunar da ita

Dubansa ya kai wajen kanwar mamansa ya ce" ummi, matata na kawo ta gaishe ki

Daga ummin har Hafsat a tare suka dafo kai suka sauke dubansu a kansa

Cikin dakewa ya ce" Hafsat, ga mamana, kanwar mahaifiyata wace ta rage min kadai a duniya

A tare kuma suka kalli junna Hafsat din da maman Na.ima

Bata taba jin zufa ta karyo mata tashi daya sai yau, kan uba, shi ne abinda ta ayanna a kasan zuciyarta, a duniya bata taba haduwa da mutun dan rainin hankali irin Abdul ba,

A hankali ta sada kallonta daga duban mahaifiyar Na.ima,
Ita kam maman na.ima bata ma san me zata yi tunani ba,
Dan haka ta kali Abdul dake zaune yana kallonsu, bin kowace yake da kallo dan ya gane hallin da suka shiga

A nitse ta ce" ban fahimci abinda kake nufi ba, kana nufin aure ka yi?

Keyarsa ya dan sosa irin ya dan ji nauyin nan ya ce" eh moms, yau kwana shida da daura auren, auren ne ya zo kai tsaye hakan ya sa ban shaida maku ba, ita kanta bata tare ba ana shirye shiryen tarewar nata ne

Kanta ta gyada tana kallonsa kafin ta mike ta ce" Abdul mu je ciki ina son gannin ka

Mikewa ya yi ya bi bayanta ,
Suna shiga ta juyo da dubanta ranta a bace ta ce" aman Abdallah ni zaka wulakanta a cikin garin niger ka nunawa duniya ni ba kowa bace haka kuma ka nuna kai ka isa da kanka kai mai kudi ko? Aure ne zaka kara baka sanar da ni ba sai dai ka zo min da yarinya kai tsaye ka wani ce ga matarka? Ka manta y'a ta kake aure idanma baka dauke ni a uwa ba ai zaka sasauta ko dan yar da na baka take zaune a gidanka ko?

Habarsa ya rike da mamaki ya ce" moms aman me ya yi zafi haka?

Tambayana kake abinda ya yi zafi? Du abinda na fada wanene baka fahimta ba na baka haske!

Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" auren ne damuwar ko kishiyar da aka yiwa yar ki?

Idannuwanta cike da bacin rai ta ce" eh dan me zaka yiwa yarinya kishiya ko haihuwar fari bata yi ba? ????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 


Kansa kawai ya girgiza kafin ya dan matsa kusa da ita dan ya ga ta soma daga muryarta shi kuwa baya so wata baraka ta fito daga wajenta, ko ba komai fa kanwar mamansa ce

A hankali ya ce" aman ai na fada auren kai tsaye ne ko Moms? Kuma kin dai san ina aure aure ai bai dace hakan ya bata maki rai ba, moms kawai sai dai idan zaki nuna kin fi son Na.ima a kai na ne, ni da na zo dan ki lalaba min ita kar ta daga hankalinta? Kin dai san tana so na bana son abinda zai hanata sukuni

Tsareshi kawai ta yi da ido, a gaskiya dan yar uwarta ne na jini, sai dai rashin mutuncinsa na wahalar da ita, ta rasa a ina ya dauki dabi.ar wulakanta mace haka? Wulakanta mace mana dan mace na sonka sai ka mayar da ita banza? Ai kuwa larabawa akoysu da ririra mace, rayuwar balaraben mutun da matarsa duda shi ba balarabe bane aman ai a can aka raine shi

Shiru ta yi masa hakan ya saka shi sasauta murya ya ce" ki yi hakuri momy, a matsayinki na uwa q wajena ban kyauta ba, aman ki yarda da ni ban aureta dan na wulakanta yar uwata ba, su duka zan hada na zauna da su daga su bani da ra.ayin kara wasu sai dai idan sun gaza da ni ne

Kawar da duban da take masa ta yi, a hankali ta ce" idan ka je ka kawota nan mahaifinta ya rarashe ta, Abdallah ka yi adalci tsakanin su

Kansa

40 / 54