Kutkale Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sajida Niger Category :  Love

Chapter   35 / 54

102K to 105K   out of 159.5K words

ta fi ta barwa Allah ya saka mata?

Sai da ya lakaci hancinta yana kallonta ya ce" shekarun ki arba.in da bakwai da wata hudu da kuma kwana ashirin da biyar yau maman Uwata, aman har yanzu akoy rigima.........
Ki kwontar da hankalin ki, adu.ar nan dai da muke yi in sha Allah ba zata kuma ba, ai yanzunma Allah ya dawo mana da ita lafia ba karfinmu ko dabararmu ba ko?

Kanta ta gyara a hankali sai kuma ta shiga sauke ajiyar zuciya

A kadan dai sai da Malan ya jima dakin mama yana ta yi mata nasiha sai da hankalinta ya idasa kwontawa sosai sannan ya mike ya kalli agogon hannunsa ya ce" yau ban ga ana shirin zuwa turakata ba

Murmushi ta yi tana rufe idannuwanta irin ta ji kunyar nan, hakan ya saka malan kara sakar mata murmushi ya juya ya fice a dakin, har tsakiyar ransa yana so ya je ya ga kar a je fadan da mamanta ta yi mata tana can tana kuka, kai a duniya da ake cewa ko cikin yaya Allah na saka maka kaunar wani ta fi ta wani, haka yake jin kaunar mai sunnan mamansa har baya iya boyewa, dalilin wannan ne ya saka shi daukan damarar boyewa ko a gaban mahaifiyarta ne bale a cikin yan uwanta da sauran matansa ko za.a shafa mata lafia


Bayan kwana hudu.....

Hafsat a kilace take cikin gidansu, an yi gumurzun an kare an yi rigimar da tashin hankalin an kare, an yi yawan maganar da tsegumin du an lafa, masu jiran su ga ta tsiro da dabanci kala daban daban sun ga shiru, Abdul aziz ya yi sau ya fi a kirga bai ga ko kalar mai kama da ita ba bale ya ganta, kai hasalima ta zama kawar mamanta da kuma yayarta

A yanzu du zama da tashinta tana lure da kyawawan dabi.un mahaifiyarta, idan aikin mamanta ne takan shiga ta zabga masu girki na ji na gani mai dadin dandano a zuba kowa ya ci da sabon taste wa.inda ta koya a wajen Formation na zama bodyguard

Bata da waya, bata damu da rikewa ba , ita ta kanta take sai a yamacin yau mahaifiyarta ta mika mata wayarta ta da wace masoyinta na da wanda sanadiyarsa ta afka tashin hankalin rayuwa

Ta jima tana juya wayar kafin ta kai ta saka a caji ta ci gaba da sha.aninta

A rana ta shida mai dinki wato hajia Farida ta kawo dinkunnan da mama ta bata ,
Ai kuwa dinkuna ne masu shegen kyau rufafu tsararu sannan na gayu masu tsadar gaske,
Ba karamin farin cikin kayan nan ta yi ba, haka ta hau sama wajen mahaifinta dan yin godiya, tana zuwa ya kara mata abayoyi kala biyar masu shegen kyau na yayi dukansu masu botira da mayafansu bakake masu tsari

Kanta kawai ta sada ta rasa bakin magana, a hankali ta dago da idannuwanta sai ta ga mahaifin nata na kallonta yanai mata murmushi, ba komai yake jin dadinsa ba sai yannayinta na yanzu, wai mamansa ce ke nuna farin ciki dan an saya mata sutura, yarinyar da a da hayowa zata yi, ba ruwanta da neman izini sai dai ta afka idan a gaban wa sai dai ta fadi muradinta na kudi ta karashe da fadin" kuma a bani ko na je saurayina ya bani!
Sai gashi yanzu a gidan duniya Allah ya nuna masa ita tana godiya harma ta rasa bakin godiyar

Hannunsa ya daga mata dan ya tabata tana iya yi masa kuka a gurin , shi kuwa baya so , dan haka ta mike har ta kusa fita ta tsinkayo muryarsa ya ce" su ABDALLAH zasu dawo gari da zama karshen satin nan, kwana biyu ina tsaye kan saukar alkur.ani a gidan da zai zauna , kulun muna zuwa a sauke a yi sadaka dan gudun fitinar zamani

Sai da gabanta ya fadi, a ranta ta ayanna me kuma zai dawo da shi kasar Niger?

Kafadunta ta daga a lokacin da ta tuna asalin dan niger din ne shima fa, haifafan garin ne, haka kuma dangin da suka rage masa yan nan ne wato matarsa da kanwar mamansa

Bata baiwa Malan amsa ba sai karasawa da ta yi da murnarta suka dadaga kayan da mahaifiyarta kafin su shiga yi masu turaran wuta da adu.ar Allah ya sa a mora lafia


Bayan kwana goma

Kwonce take tsakar dakinta wajen karfe biyar na yama, juyi kawai take tana tunanin wai yau zata yi zance, zancen ma da BS, zuwansa biyu sai yau Malan ya bashi damar ya zi su gana

Mikewa ta yi zaune tana kallon madubin dakinta mai tsayi, kanta ta girgiza ta koma ta kwonta gashi har karfe bakwai din ta kusa,

Tana nan kwoncen har karfe shida ta buga, buda kofar da aka yi ne ya sakata mikewa zaune tana kallon yayarta da ta shigo da yaronta da ya fara rarafe yana yawonsa ko.ina

Bayan sun gaisa ne yayar tata ta bita da kallo,
Can ta ce" Maman malan, ni ba bako aka ce zaki yi yau ba?

Hafsat ta dubeta ta ce " eh

Yayarta ta ce" to ya haka baki shirya ba

Hafsat ta kaleta da mamaki ta ce" shiryawar me kuma auntu ? BS ne fa??

Sai da ta rike habarta sannan ta yi dariya ta girgiza kai ta ce" dan BS ne shine ba zaki kimtsa jikinki ba? Oya tashi tashi malama

Mikewa Hafsat ta yi tana kallonta kafin ta shige ciki ta dauko abaya daya daga cikin abayoyin Aba ta saka abinta a nan sannan ta shiga saka turarukan wutar da ta miko mata

Tana kokarin yana mayafin dan kwalin ta tsayar da ita ta zauna ta dan gyara mata fuska da kwalinta sannan ta yana mata dan kwalin a kanta

Tsaf hafsat ta fito tamkar ba ita ba, wani irin kyau ne ya bayanna a tare da ita wanda ita kanta sai da ta shafa gefen fuskarta sannan ta yi murmushi


Ana fitowa sallar magariba aka suka zauna tsakar gida inda malan ya basu minti talatin su gana

A zancen nan Hafsat banda tambayoyi a kan aiki ba abinda ta tsare BS da shi, shi kansa sai ya kasa wani yi mata zancen soyaya sai da ya tashi tafia ne ya ce da ita" Hafsat, ina son na turo a yi komai da wuri a gama, dan kin ga malan baya son dogon zance

Sai da ta ji gabanta ya fadi, ta dan tsura masa ido aman sai ta kasa ce da shi komai,

Murmushi ta sakar masa sannan ta shige ciki da dan gudu gudu hakan ya saka shi sauke ajiyar zuciya ya juya ya tafi ya shiga galeliyar motarsa yana tunanin sai dai a waya ya mata maganar aikinta da kuma dukiyarta


Can wajen karfe biyun dare, dare ya tsala Hafsat na zaune tsakiyar gadonta daga ita sai dan gajeran wandonta da yar rigarta na barci ta yi zuru da wayarta a hannunta tana dannawa tana game

Message ne ya shigo mata kamar haka " *KAURIYATA, NA KASA BACI*

kurawa harufan ido ta yi tana kallo, bugun zuciyarta ne ya canza lokaci daya hannunta ya fara rawa,
Du duniya ba wanda ke haye mata irinsa, shi ne, walahi shi ne

Wayar ta ajiye tana kallon rubutun tamkar wanda ya yi da hannunsa idan hasken wayar zai dauke sai ta danna ta kara kallo

A hankali ta rubuta " *ME YA HANA KA BACI?*

mikewa ya yi zaune daga kwoncen da yake yana mai hararar wayar, kafin ya rubuto " *ke, gida kika je kika tara samari haka? Bakya dan jan aji daga yi maki magana har ki bani amsa ko kin sanma da wa kike magana ne?*

A lokacin da ta karanta sai da ta saki murmushi, sannan ta rubuto" *na san ko kasuwa na yi a tsakiyar dare irin na barawo? Dole bazawara ta ringa damka da karfi karfinta mana*

Wani uban tsaki ya ja a lokacin da ya karanta message din,

Zama ya gyara ya shiga dandankara magana son ransa, har ya so saki sai kuma ya koma da baya ya zauna ya jinginar da kansa jikin bed din, ajiyar zuciya ya sauke yana kallon waje daya sai kuma ya rubuta message kamar haka" *Na yi missing din ki amaryar BS*

Numfashinta ne ta fara ji yanai mata sama sama, lokaci daya kuma ta koma ta mike kafafuwanta saman bed din , sai da ta yi mika nitsatsiya sannan ta rubuta message kamar haka.........



>???=???>???=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>???=???>???


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




4?? 6??






Suna nan tsaye kusan minti ashirin har ta fara kitan layin Malan dan ta fada a zo a dauketa sai ga wata mahaukaciyar hamer baka wulik ta tsaya a gabansu sai maskin sabuntaka take tana dana ashar din rashin mutunci ita kadai sai lillon iskanci take tsabar an murxata an yi gudu da ita, bakaken gilas ne a jikinta gaba da baya hakan ya sa koda wasa ba.a gannin na ciki komai kwakwarka dan sabuwa ce , komanta sabo ne

Daga cikin motar ya kare masu kallo lafin ya sauke gilashin yana jinjina rainin hankalin Hafsat, ta sab sarai ko waye a motar aman ta wani kawar da kanta tana kallon wannan jajir fin uwa gwonda,

Dariya ya yi a lokacin da yake sauke gilashin ya rage sautin cikin motar ya kali na tsayen
Muryarsa ya dan daga dan zuwa lokacin ta ga dama ta kallo infa yake ya ce" tsakaninka da Allah da wannan tsatson tamkar zaka karye da kuma wannnan jar fatar taka uwa yumatir ne zaka zo ka tsaya gaban wannan yarinyar kanai mata bunsuranci kaima ga namiji ko? Yanzu kaima dan iska ne?


Daga Hafsat har mutumen kallonsa suke baki da ido bude,....
Hafsat har sai da ta murje idannuwanta tana kallonsa, dama kiran da ya yi mata dan ya tardota infa take ne?

Kanta ta girgixa ta kara dagawa mai taxi hannu aman ya fice ba tare da ya tsaya ba

Abdul ya sasauta murya ya ce" Kauriyata mu je mana

Dai da ta galawa motar harara sannan ta ce" wai kai haka Malan ya yanka min ragon sunna?

Abdul ya kikifta ido yana kallonta sannan ya girgiza kai ya ce" aa

Ta kebe bakinta gefe sannan ta kawar da kai

Mai jan kunnen nan da wani mamakin kuma ya kalli Hafsat, gannun kamar fitsara ce ta yiwa wannan fitsararan aman ya bata amsa a sanyaye

Ki shigo mu tafi kin ji?
Abduk ya fada cikin muryar rarashi da kwontar da murya

Motar ta karewa kallo, sannan ta shagwabe fuskarta ta ce" ni aa, ka je kawai

Fuskar ya kurawa ido dan ta yi hakan ita kanta bata san ta yi ba aman ba karamin kashe shi abin ya yi ba,

Motar ya shiga citewa a ky sannan ya ce" idan baku shigo ba, na rantse zan fito na dauke ki na saka ki a motar nan bayan na fafala maki mari

Hafsat ra kale shi da kyau ta ce" Malan fa? Ya hana ni shiga motar karti!

Sai da ya zazaro ido sannnan ya yi murmushi ya ce" daga wajen malan din nake Maman malan

A hankali ta faga kafarta ta nufi mitar cikin nutsuwa ta bude ta shiga ta zauna
Mai siyar da shadojin nan na tsaye yana kallon ikon Allah yau ya hadu da tantiran da suka fi shi iya shegantaka har Abdul ya tayar da motar ya harbata bakin titi
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" gaske kike dizga maza!


Abdul na fara tafia ya juyo ya kali Hafsat, bata ankara ba ta ji ya saka yatsarsa ya lakaci man leben da ta goga a bakinta,

Kansa ya girgiza ya ja tsaki ya ce" kema yanzu sai kwaliya da saka kaya masu maki kyau dan ki yi samari ko? Samarinma maimakun ki sami jarumi ingarma aa sai wannan lange langen tamkar igiyar leko? Hafsat kin ji kunya, kin ji kunya kin kara jin kunya!


Hafsat ta lumshe idannuwanta tana jin yannayin wani iri, Abdul ne ya dawo niger da zama? Shine da walwalarsa? To aman yaya ya yi da damuwar Muhammad? Yaya ya yi da Muhammad?

Abdul ya kaleta ya ga shi ke haukansa ita batama san yana yi ba ya girgiza kai daidai sun tsaya a danja ya yi shiru

Hafsat ta karkato ta kale shi a hankali ta ce" me ya sa jiya ka min magana kuma ka min banza a waya? Sannan wama ya baka number wayana ne?

Abdul ya juyo yana kallonta ya ce" number wayarki satowa na yi a wayar malan a lokacin da zai ja salar juma.a ya banu komai ajiya ni kuwa na koma gefe na sata!
A jiya kuma a daidai lokacin da muke magana da ke madame ta farka, tana farkawa ta jefo min kallon kauna, lokaci daya na rikice na fita a hayacina, kin san lafia idan ta yi yawa , ga na koshi, a hankali na kamo matata na kwontar na.....
Niyar Abdul fayace mata abinda ya yin sai horn din mutane ya saka shi waiwayawa ya ja tsaki ya tayar da motar ya kara daukan titi a nitse yana tafia a hankali

Cikin nutsuwa Hafsat ta ce" sai mun biya ta chateau 9 na kai dinkin Aunty

Kansa ya gyada mata ya dauki hanyar chateau noeuf din, aman yana tafe yana neman fitina yana takalarta rigima ita kuwa ta yi malakas tamkar ba ita ba

Sai da suka tsaya wajen dinkin ta sauka ta nufi ciki a ranta tana girmama girman masifar Abdul, wai yaushema ya zama haka ne? Wato duka kaf masifar da yake era mata ne yake sauke mata a yanzu, to wai inama tuwansa ne? Ita kam ta ga ta kanta

A lokacin da ta bayar , Nadiar ta umarci daya daga cikin yarenta fa ya dauki awon yannayin jikin Hafsat,

Dan kwalinta ta warware dan ta ce a yi mata baban wuya sosai

Daukan abin awon ya yi da litafin rubutawa ya zo da nuyar dauka sai ji suka yi Nadia na gaishe shi ta mike da kanta tana tambayar dinki aka kawo ne?

Kallonta ya yi yanda man shafe shafe ya bi ya kokona mata fuska, shagon cike da karti sai dinki suke da wasu irin manyan yan mata irin yan dunuyan nan kowace sai fama take da atach cike a kai ya kada kansa sannan ya kaleta ya ce" ke baki iya aunawar bane zaki saka wannan ya dauki awonta ko ita tace sai namiji?

Kallonta ta kai wajen da ya nuna, da sauri ta ce" yi hakuti oga,
Sannan ta karasa ta karbi abin awon ta shuga auna Hafsat da kanta

Sai da ta gama Hafsat ta tambayi kudin, nan ta yanka mata tsada sosai na dinkin nasu ita da auntynta , dan haka ta buda jakarta ta ciro kudin ciki baki daya ta mika mata ta ce zata kawo sauran idan an gama

Yana tsaye yana kallonta har ta gana ta fice ta shiga motar kamar ta zabga masa mari dan haushinsa take ji sosai,

Daya daga cikin yaran ya yafito ya juya shima ya buda motar ya shiga,

Cofre ya ja ya janyo yan jika goma goma har kwaya takwas ya mika masa ya rufe motar ya kana hanya

Yana kama hanya Hafsat ta kale shi ta ce" Abdul, ya isheka haka ka ji ko? Mme ya shafe ka da dinkina ne? Makan da zaja ringa yi min ihu a ka wai yarka ce ni? Haba haba, kuma walahi idan ba.a yi min wuyan da na zaba ba ba zan saka shadar ba, kuma sai ka mayar da ni ma karbi canjina dan ban iya almubazaranci ba!

Satar kallonta yake yanda take daga murya tana dukan cinyarta wai ita nan tsakaninta da Allah masifa take masa?
Bakinsa ya hade sannan a hankali ya ce" kin zama fitsarara kin gama! Hafsat ba dai ni ba ko? Ni dai ne ko? Na ji

Shiry ta yi tana kikifta ido tana kallon hanya har suka shigo anguwarsu,

Suna shigowa ta sasauta muryarta ta ce" Abdul, dan Allah ka ajiye ni a nesa da gida na karada gidanmu a kafa kar a je wani ya ga an ajiye ni a wannan motar a ci gaba da jifana da munana kalmomi fa munanan furuci ka ji?

Kallonta ya kara yi, yanda ta marairaice, wani tausayinta ne ya ji ya tsirga masa, dan haka ya fage gudun aman bai tsaya ajiyetan ba

Tun tana kallon kamar zai ajiyeta har ta ga ya iso lusan gidansu,

Sai da ya tsaya kofar gidansu ya danna horn

Wangame get din gidansu aka yi dan ana tunanin malan ne zai sako motarsa, sai dai gannin wannan wuleliyar mota ta saka mai budewar kansa yayansu tsayawa yana kallo

A hankali ya ja motar ya shige cikin gida da ita,

Motar ya tsayar yana kallon yanda du ake lekowa ra taga ana kallon abinda ke faruwa

Tsoro ne karara ya bayana a fuskarta, harma wata kwallah ta tarun mata a idannuwanta, kallonta ta kai wajensa a hankali ta ce" ka san a zaginsu wanda ke tayar min hankali har nake tsoron wataran su kaini bango? Bama son suna saka mahaifiyata a shirmen su, idan sun yi kirana da karuwa shin du lalacewar uwa zata aiki danta ya je ya yi karuwanci ne? Abdul

35 / 54