Kutkale Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sajida Niger Category :  Love

Chapter   15 / 54

42K to 45K   out of 159.5K words

SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




2?? 7??



Fuskarsa ya hade sosai kafin ya ce" wa kike magana kanta?

Hafsat ta sauke lumfashi, ta dube shi da kyau, ta san fa ya gane wanda take nufi aman zai wani tambayeta!
Dan haka ta ce" mai aiki mana

Abdul ya lumshe idannuwansa ya ce" ki ce dai budurwar ubana!

Ido ta zaro tare da dora hannunta saman bakinta tana dubansa, bata san lokacin da ta ce" Abdul!

Idannuwansa ya bude daga lumshen ya kalleta da su kafin ya mike gaba dayansa ya shiga kokarin bin hanyar cikin gidan

Bayansa suke bi daidai da takun tafiarsa,

Bata gajiya ba a lokacin da zai shiga dakinsa ta yi saurin fadin sunnansa ta hanyar kafe shi da ido

Tsayawa ya yi yana dubanta , ido cikin ido suke kallon juna sai kuma ya yi kasa da idannuwansa ya mayar wajen lebenta da shi baima san nan ya kurawa ido ba a hankali ya ce " Hafsat, sunna zan raya, kin san bata jira dai ko?

Da sauri ta rintse idannuwanta sanadiyar kunyar abinda ya fada, gashi ya fada ne da yaren da kowa zai iya ganewa ga Hasana itama a kusa da su take sosai dan kuwa ita zata shiga ta gyara dakinsa kamar yanda aka saba,

Juyawa ta yi gaba dayanta ta koma gefe ta tsaya, ta kasa daga idannuwanta bale har ta yi ido hudu da daya a cikinsu, gaba dayansu kunyarsu ta ji ta mamayeta a haka har bata san lokacin da ya shige ba, sai takun takalman sarauniya ya shaida mata har ta karaso,

A hankali ta dago da dubanta ta sauke saman Ni.ima,.ta sha wani danyen lesh mai ruwan madara, ta sha kwaliya fuskarta tamkar ka saceta ka gudu,
Ni.ima ba ramama bace, sam bata da rama, sannan ba sakaken jiki ne da ita ba gashi ya hadu da kulawa dan akoyta kwaliya sosai, budurwa ce mai zamani wace dubai ke son malaka a wannan karni

Yannayin takunta ke tafiar da isarta, Ni.ima ta jiki, jika irin ta naira, dan kuwa bata nema ta rasa ba, ga kuma daidai gwargwado iyayenta sun bata tarbiya, so ne kawai ya sakata sangarta da shiga sabgar Abdul

Kanta ta sada dan kuwa du macen dake wajen a tsaye sai da Ni.ima ta kwasheta da kallo ta yarfata kasa da idannuwanta sannan ta tsayar da masu bin bayanta da hannunta ta juya ta buda dakin Abdul ta shige abinta ba tare da damuwar komai ba a fuskarta

Tana shiga gabanta ya fadi, dan kuwa ta san abinda ya kawota dakin, wai ita, yaushe zai zauna ya yi hira da ita irin na soyaya? Yaushe xai dubeta da duba na darajanta dan adam a matsayinta na matarsa?

Inda yake zaune ta je, tana zuwa ta haye saman cinyarsa ta zauna tana kallon yanda yake lunshe ido

Abdul dake binta da kallo ta kasan idannuwansa ya saka hannayensa ya janyota a hankali jikinsa sosai sannan ya shiga kokarin sarafata dan samun nutsuwar damuwar dake damunsa

Binsa kawai take, du yanda ya jirgata sai ta bi ba tare da ta nuna wani yannayi na shauki ko murafin hakan ba,
Tun yana yi da nuni a yannayinsa na muradin gannin shaukinta har ya cire a ransa ya shiga kokarin zuwa duniyar ma.aurata

Da sauri ta rike damtsen hannunsa wanda du girman hannunta sai ya kasance ko rabin damtsen bata cika ba bale har ta cike wajen da hannun nata,
Muryarta na rawa ta ce" ka...ka bari na birgeka mana?
Yakan ce da ita birge ni, a duk ranar da baya son zuwa waje mai kakant din , takan yi ta fama kafin ta samu ya samu kansa, har bata son yace da ita ta birge shi dan haushi take ji lamarin na wahalar da ita, sai gashi yanzu da kanta ta nemi ta birge shi?

Tsai ya yi da niyar shigar nata ya tsurawa yannayinta ido,
Tabas bata cikin ra.ayin hakan, sam babu muradin hakan a tatare da ita,
Aman rabonsa da ita fa yau 2 days, shi ne batama daukinsa?

A hankali ya janye hannayensa ya rage nauyinsa a jikinta sannan ya mike gaba dayansa,

Maimakun ta ga ya juyo ya bata damar birge shin sai ta ga ya nufi bayi

Da sauri ta mike zaune tana raraba ido, gabanta ne ke ta faduwa lokaci guda kuma ta ji wani haushin kanta wanda har ya hadasa mata zubar da hawaye, ya salam, ya yi fushi? Fushi ya yi ko me?

Nan take zaune tana ta sharar hawaye har Abdul ya fito da tawul yana goge jikinsa

Turus ya ja ya tsaya da mamaki yana kallonta tana kuka,
Yana son ya budi baki ya tambayeta abinda ke damunta aman bai san me yasa yake da nauyin baki a kan lamarin mata ba, shi dai zai maki surutu ne idan ya yi niyar dizga ki, shi banda Kauriyama wace mace ce yake sakewa ya yi ta surutu da ita?

Kallonta da yake ya sakata mikewa gaba dayanta ta nufo inda yake tsaye ta mika hannu zata taba shi ta ce" dan Allah ka yi hakuri kar ka yi fuahi da ni

Abdul ya dan ja baya yana dubanta kafin ya fahimci inda ta nufa,

Wajen ajiye tawul din ya nufa ya sarkafe shi ya juyo inda take tsaye ya ce" bana takurawa mace dan zuwa duniyarnan, ina son koda yaushe duniyar nan ta zama a kawace, ba fushi na yi ba, ki saka kayanki kinje ki tsaftace jikinki

Yana gama fada ya bude wajen suturunsa ya kurawa wajen ido,
Kaya ne kala daban daban, na manyan manyan kudade sannan masu kyan gaske,
Du a cikinsu ya janyo wata riga fara ya zura ba tare da ya saka komai ba ya dawo saman bed din ya zauna,
Har ta fice a dakin, da kuma kuka ta fita,
Bakinsa ya tabe yana mai kallon wajen windows din da ba damar ya shaki iskan wajen an rufe ruf

Karamar wayarsa ya mika hannu ya dauko ya kunnata,

Kara wayar ya yi a kunnensa bayan ya danna kira a wata bakuwar number

Bai jima yana wayar ba ya ajiye ya mike ya shiga shiryawa sannan ya saka akaiwa masu tsaron kofa maganar zai yi bako a bar shi ya shigo

A lokacin da bakon ya zo , Abdul ya nemi Hafsat da ta shigo wajen da zai gana da bakonsa dan ta kula da lafiarsa,

Bakon wani mutun ne da ba za.a kiraye shi yaro ba, magidanci ne ya kwana biyu sosai sai dai ba tsoho bane,

Irin mutanen nan ne wayayu, masu shegen wayo da son da bakinsu su sayi du wani gara,
Suna siyen kuwa dan idan ka yi wasa lokacin da zasu tafi da kai kai kanka sai ka laluba ka ga babu kai

Tunda ya zauna suka gaisa Hafsat ke tsaye gefe tana aikinta ba tare da ta bada hankalinta kansu ba

Tambayar da Abdul ya jefa masa ne ya sakata maido hankalinta inda suke zaune ta raja.a dukan wani nutsuwarta a kansu da rataunawar tasu, sannan sai a lokacin ta gane ya saka ta shigo ne dan wannan dalilin

Mutumen ne ya dago hannunsa na dama ya shafi gaban goshinsa kafin ya maida hannuj bayan keyarsa ya dan sosa sau biyu ya ce" eh Elhaj, tabas marabina da su na ga dan nata , sosai saurayi ne kakarfa sai dai sam baya kama da kai, kuma shi fari ne,

Abdul dake kallonsa ya ce" kuma yaya sunnansa ne? Yanzu a ina suke ne? Ko nace marabinka da su a ina?

Dan zakutowa mutumen ya yi ya saka hannayensa ya ja rigarsa ta kara yin sama hakan ya baiwa dogon wandon rigar damar kara bayanuwa,
Agogon hannunsa ya murza da babar yatsarsa, ya zagaye ya kuma zagayewa, sai da ya rintse ido na sakonni sannan ya budi baki ya shiga bada labarin marabinsa da matar da kakaninsa suka koreta da cikin mahaifinsa, wanda ya tabatar masa cewa namiji ta haifa harma ya ga mutumen da idannuwansa, ya tabatar masa cewa makudan kudadan da kakaninsa suka bata dan ta kula da rayuwar dan da zata haifa sun isheta rayuwa suna cikin wadata suna rayuwa cikin jin dadi,

Abdul ya sauke kafa daya daga saman cinyarsa ya ce" ta musulunta ne?

Sai da ya kurawa Abdul ido sannan ya ce" ae, eh eh mana Elhaj ta musulunta mana,

Abdul ya gyada kansa, kafin ya maida dubansa wajen Hafsat ya ga kawai mutumen take kallo da sexy eys dinta,
Komawa ya yi ya jingina da jikin kujerar ya ce" wane da wane kika yarda a cikin magangannun nan?

Hafsat da ta yi firgigit ta maida dubanta wajen Abdul, ta kasa cewa komai, dan ita dai ba sannin mutumen ta yi ba, duda yannayinsa na nuni da rashin gaskiya da son dole dole sai ya yi cinvaincre din Abdul din, ba zata iya cewa komai a kan hakan ba,

Abdul ya lumshe idannuwansa ya ce" wato idab mutun baya son gannin abu a zahiri ba zai gansa ba?

Mutumen ne ya ce" Elhaj ban gane inda ka nufa ba

Abdul ya bude idannuwansa aman bai basu damar budewa baki daya ba ya ce" karya kake min Murtala, gaba daya magangannun nan da ka fada ba daya dake gaskiya,
Kai hasalima baka ga wannan matar ba, dan kuwa da ka ganta da ba zaka ce ta musulunta ba dan can dama musulmar ce

Saukin mikewa tsaye ya yi yana zarar ido, hakan ya bashi damar tsayawa kerere gaban Abdul

Ya buda baki zai yi magana sai jinsa ya yi an dangwarar da shi zaune saman kujerar da ya miken,
Mamaki ne ya kama shi gannin yar budurwar an ce ta mayar da shi haka da zafi sannan ta yi tsaye a gabansa wanda yannayin kyakyawar fuskarta da ya nuna hadewa sam ba alamar annuri ya saka shi jin gabansa ya fadi,

Abdul dake zaune a hankali ya bi hannun Hafsat da ta saka ta mayar da Murtala zaune da kallo,
Wandon dake jikinta ne ya kuma bi da kallo , ya dameta sai dai na roba ne hakan ya saka take motsawa son ranta aman du wata halita mai rawa ko mai motsi a wajen tana iya mitsawa in dai Hafsat din ta motsa,
Sannan rigar dake jikinta mai siririn hannaye ce, dan kuwa tun harbin da akai mata ta daina saka mai dogon hannu ko fita zasu yi dan hannun ya warke kar ya danyace
Rigar ta yi mata caras a jikinta, kanta da dan karamin dan kwali baki sidik wanda ta yane kan da shi, fuskarta ba ko digon kwali aman lebenta haka yake jan idon wanda ya kale shi dan tamkar ta goga masa jan baki ne

Lebensa ya hade gaba daya sannan ya tabe bakinsa yana kallonta, irin tsayuwar da ta yi a kan Murtala,

Kansa ya girgiza sannan ya mike tsaye,
Hannunsa ya saka ya mayar da ita gefe hakan ya saka ta zama yar tsuwat a gefensa tana huci dan neman fadan dama take

Abdul sai da ya daura?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? agogon hannunsa da kyau sannan ba zato ba zamani ya saka hannunsa na dama ya dago wuyan Murtala ya ja shi ta wajen kujerar hakan ya saka wandon dake rige da kugunsa janyewa dan kuwa arzunzumi ne harka da yan gayu bai wani daure shi da kyau ba,
Kiiii ya ja shi sai da ya dangana shi da bangon dakin sannan ya saka dayan hannun nasa ya daga shi gaba daya ya raba shi da dandar kasa ya rike masa wuya sosai yana dubanda ido cikin ido ya ce" yaushe na zama bolar da har zaka daga muryarka a kan tawa? Bayan karya da cin amanar har raini zai shiga tsakanina da kai? Ka manta a gidan iskancin da na hadu da kai a irin halin da kuka hadu? Ko dan kana tunanin kai lauya ne sannan ka girme ni zaka raina ni?

Murtala dake harhaba kafafuwansa dan neman a sake shi, du idannuwansa sun ruruko yana ta kokarin yin magana a hakan ko zai sake shi sai rike hannayensa yake aman Abdul ya kasa sakinsa sai kara matsar masa wuya yake

Da sauri Hafsat ta matso ta tsaya ta ce" Abdul, ka sake shi, kar ka kashe shi Abdul=?O?
Idan ya kulata to lale dakin ya amsata,
Gannin yana neman yin kisa ya sakata dan kokari matsawa ta saka hannayenta dan kwaljwace wuyan Murtalan a hannun Abdul

Hannayen nata ya yarfe da hannunsa na hagu, bai saki murtalan ba ya hankadata da hannun nasa hakan ya saka ta yi tagal tagal ta hadu da kujerar wajen ta ja ta tsaya tana sauke ajiyar zuciya kafin ta tsinci muryarsa a kausashe ya ce" *Ke, bilahilazi kika yarda kika kara taba wannan jemagen sai na karya maki wuya!*

Yana gama fadi ya sake shi nan ya fadi yana kakarin tari , shi kuwa ya duka ya lalubi wayoyinsa ya juya da su ya fice ya nufi dakinsa ya rarumi computernsa ya zauna ya jona wayar ya shiga aiki yana mai jin shi bashi da abinda zai iya yiwa wannan mutumen ya huce sai dai idan zai kwakule masa idannu ne ya soye ya huta!

Hafsat kam sai da ta sha jinnin jikinta a lokacin da ta ga ya nufo kamar ita zai damka , sai kuma ta ga ya fice a dakin,

Ajiyar zuciya ta sauke a fili ta zabgawa hanyar harara a ranta kuwa ta ce" dama na bari ya hayeka a mikewar da ya yi dazun, ni na ga jaraba! Malan ana kare ka kana hana mutun aikinsa!

Juyawa ta yi ta fice a dakin ba tare da ta kuma bi ta kan Murtala dake yashe a nan ba ta fice gaba dayanta ta zagaya wajen sojojin dake gadin bayan gidan ta samu daya ta amshi aron mashin dinsa ta haye ta harba titi

Gudu take tamkar ba zata karasa inda ta nufa ba,
A haka man mashin dinta ya kare ta tsaya ta zuba harma ta yi guzurin wani, sannan ta dauki wayar da ta gama bincike ta kare a sunnan wani gagarumin malamin islamiya dake raye a kauyen garin Minna din, wanda ke rayuwa daga shi sai almajiransa, aman kuma mutumen har ya iya hawa social media, ba komai ya ja hanlalinta yau tsayun kwana biyar a kansa ba sai sunnansa,

Sunnansa *Muhammad bine Abdul Basid Abdallah*

Ta zama wata irin mutun ce mai kurmuwa dukan wani abinda zai bata damar samun gaskiyar abinda ke boye a tatare da Abdul, ba ruwanta da me zata tarar? Waye shi mutumen? Burinta ya kasance shi ne!


A lokacin da ta shiga cikin jejin, a bakin wata rijiya ta ga mutun zaune yana rubutun allo,

Babur din ta tsayar tana son saka jak ta ajiye mashin din mutumen ya dago da kansa daga saman allon karfen da yake rubutu samansa

A tare gabansu ya yanke ya fadi, a wannan lokacin a wannan wajen ya mike ya durfafa cikin jejin wanda kafin hafsat ta sauka a mashin din tuni ya bace mata bat ta nema ta laluba kamar ta yi hauka ba shi ba alamarsa

Wajen allon ta je ta tsugunna ta dauki allon da tawadar,
Yatsarta ta saka ta lashi tadawar, ta daga idannuwanta ta kai wajen rijiyar,
Ba komai ake rubutawa a jikin allon ba sai astagafari,
Mutumen ba wani yaro ba aman irin yanda lokaci daya ya bace mata ya tsoratar da ita

*Wannan mutumen shi ne ya damki hannunta a wajen daurin auren dan minister da yar Elhaj,*

Ta shiga rudu, waye shi? Ko shi ne mai wannan sunna? Me ya sa a page din da yake yawan rubutu baya saka komai sai jawabi da gargadi a kan zina? gashi dare na kokarin yi mata a jejin da ta daina gannin ko wulgawar tsuntsu ne bare na mutun.

Zuciyarta na son gaskata mata hasashenta, runguntsumin tashin hankalin Abdul na ture komai,

Idan haka ta kasance ina zai shiga da ransa?

*Wai wa ke neman ranka Ya Abdel?* hafsat ta mike ta kuga haka wanda gaba daya sai da wajen ya amsa da amon muryarta ......


Allon nan ta dauke ta juya wajen mashin din tana kokarin hawa ta tayar ta hang...........


>???=???>???=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>???=???>???


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




2?? 8??





Tana kokarin tayar da mashin din ta hango wani irin mutun,
Mutun ne zabaya namiji kuma wada ,
Kai ba dan ba dan ba sai tace ko ta yi gamo ne? Dan kuwa mutumen tsayawa ya yi yana kallonta kamar ya ga bakuwar halita

Adu.a ta yi sosai ta tofa masa yana kallonta tana kallonsa,
Gannin ya ki motsawa ya kuma kin yi mata magana ya sakata saukowa a hankali ta nufe shi inda gabanta ke luguden kida

Tsayawa ta yi dan nesa da shi ta

15 / 54