Kutkale Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sajida Niger Category :  Love

Chapter   32 / 54

93K to 96K   out of 159.5K words

4?? 1??


Cikin yannayin rashin tsoro da kyama take duban keayar idannuwan Muhammad dake dan langi sakamakon kwayoyin da ya hadiya ta shiga mayar da zancen duka kaf da ta gano wajen bincikenta, da irin sato tan da suka yi shi da sojansa mai bashi goyon baya, da komai da komai

Sai da ta ja numfashi ta kai dubanta wajen BS da har jikinda bari yake tsabar firgita da ikon Allahn nan, ya ga lamari da yawa, ya ga gaba da yawa, aman bai taba gannin ci amana irin wannan ba

Idannuwanta cike da hawaye ta ce" wannan da kake gani, wanda ba zan iya kiransa da madaukakin sunna irin MUHAMMAD ba, domin ya kasance azalumi, mai izgili da rashin tsoron Allah, wannan aljanin mutumen wanda ban ga sunnan da ya dace da shi a musulunce ba!

Ta kuma rinyse idannuwanta sannan ta ce" *shi ne mai kashe kashen nan baki daya ban cire maka ko daya ba, kuma yana yi ne dan vengeance*

Sai da BS ya dafe gaban kirjinsa dan luguden kidan da yake masa,

Dubansa ya kai wajen algungumin a daidai lokacin da ya daga hannunsa ya nuna Hafsat ya ce" karya ne!


Gindin bindigarsa ya saka ya daki keyarsa hakan ya katse masa fitsarar da ya dauko a bakinsa ya silale wajen a sume

Da kallo ya bi shi sannan ya bada umarnin a nufi asibiti da Abdul da Hafsat
Shi kuwa ya dadaure Muhammad dauri irin na huhun goro sannan ya shiga bincike da harhada du abubuwan da zasu isa cikaken shaida haka kuma ya tabo ikon garin wa.inda bai isa ya aiwatarwa da Muhammad wani abu ba sai abinda aka yanke masa a kotu

A lokacin da aka saka masa ankwa bayan sun dankara masa wata gigitaciyar allura mai taba kwakwaluwa aminin Abdul mai sunna Ahmad ya yi tsai yana kallon motar da aka shigar da shi baima san inda kansa yake ba,
Tabas shima ya girgiza, sai dai da wuri ya kwabi kansa a lokacin da ya tuna cewa Muhammad fa mutun ne, dan adam ba, dukan abubuwan da ya ringa yi ke dawo masa a idannuwansa,
Sai da ya kalli BS dake kokarin tayar da mota dan bin bayan su Abdul sannan shima ya buda motar da shiga wace ke dauke da gagan sojoji wa.inda ba alamar sun taba sannin wani abu mai sunna dariya a rayuwarsu sannan ya gyada kai a ransa ya ayyana........shara.ar Muhammad ya dace a barwa Allah, bai ga hukuncin da za.a yiwa wannan bawa a nan cikin duniya ba, bai ga irin abinda za.a iya yiwa wannan bawa ba a huce ko a rama irin abubuwan da ya shuka, tabas zasu tura shi kasarsa a hukuntashi a can, ya tabata kisa ne ta hanya mafi muni ya je can kuma ya fuskanci wanda ya halice shi!



A asibiti kuwa tun a hanya BS ya samu ya kirayi number Malan, domin tun ranar da Abdul ya je BS ya gane akoy fahimta tsakanin datijon da Abdul, a irin yanda Abdul ya zame kasa ya duka ya gaishe shi wanda hakan shi ne gannin farko da ya yi ya mutunta mutun

Bayanin da ya yiwa malan ya saka shi jin zufa ta keto masa, cikin nutsuwa ya nuna masa cewa da zai samu jirgi a lokacin tabas da ya zo da kansa domin kuwa dole Abdul na bukatar mutun a kusa da shi

BS na jin haka ya ce da shi ya kasance cikin shiri koda yaushe ana iya zuwa daukansa in sha Allah za.a kawo shi

BS ma karasawa ya tarar likitoci na kan Abdul , famansu shi ne su dawo da numfashinsa da bugawar zuciyarsa daidai,

Hafsat kuwa na zaune saman kujera an saka mata magana a fuskarta an gyara mata an yi an yi ta kwonta ta huta aman ta kasa tana zaune ta saka wata riga baka mai dogon hannu aman bata canza wandon jikinta ba ta faure kanta da dan kwali baki ta yi zuru da ita tana kallon waje daya, a kasan zuciyarta kuwa sai adu.a take kan Allah ya sa ya yi hakuri ya dauki komai da sauki

Sun dauki kusan awa kafin a fitar da shi a kai shi dakin hutu sai a lokacin ta mike ta koma dakin da ya dace a kwontar da ita ta shiga bayi ta yi wani irin wanka sannan ta fito ta dauki wani wandon da rigar baka da hijab da Hasana ta kawo mata ta saka ta kabarta sallah a nitse

Ta jima tana ramuwar salolin dake kanta, ta dauki lokaci tana sallah kafin ta salamce ta shiga adu.a da godiya ga Allah

Jaka kawai ta tsinci kanta da yi masa adu.a mai nauyin gaske, ta jima tana rokon Allah ya taimaketa ya ji kanta duda baya barin wani dan wani ya ji dadi ita kam bata tunanin zata ci gaba da walwala idan bai mike ya samu kansa ba

Tana ta jero adu.o.in ta ji wata kamilaliyar murya, nitsatsiyar murya, muryar da ta kasance mai yi mata nasiha da lalaba ta, muryar dake tsananin girmamata ta hanyar kiranta *UWATA* muryar da ta kasance daya daga cikin adu.o.inta na Allah ya nuna mata ranar da zata kara jin muryar a duniya

Kasa kunne ta yi tana mai jin zuciyarya na bugawa a lokacin da ta ji BS ya yi magana sai kuma ta ji muryar ta ce" Allahu ya tashi kafadar bawan Allah, ya bashi lada da juriyar wannan jarabawa, domin Abdallah mutumen kirki ne

Wata irin mikewa ta yi ta doshi kofar, sai dai me, Hasana ce ta riko hannunta da karfin gaske ta ce" ki koma ki zauna H, kar ki jazawa kanki kin san kina cikin mission ne

Wani kallo ta yiwa hannunta da ta riketa da shi sannan ta ce" ki cika ni

Hasana ta saketa ta ce" zaki lalata aikin ne

Hafsat bata ce da ita komai ba ta buda dakin da saurin gaske ta fita

Tsayuwa ta yi ta shaki kamshin turaransa, bai canza shi ba shi dai ne har yanzu,

Da sauri ta shiga raraba ido tana neman inda zata gan shi, ina zata ga hasken idanniyarta,

Kyalkyalin tazbaha da ta gani a daidai kofar dakin da aka saka Abdul ya sakata nufar wajen har tana hardewa , muryarta ta buda ta ce" *ABANA*

Da sauri ya saki kofar da ya buda da jiyar shiga domin likita ya ce ana iya shiga Abdul ya farka ya juyo inda ya ji muryar

Ita ce tsaye gabansa
A hankali ya furta" Alhamdulilah.... *UWATA*

AI kuwa Hafsat ta fashe da kuka sannan ta arta a guje , tana zuwa ba wata wata ta fada jikin mahaifinta ta kankame hannunsa tana wani irin kuka , bata wani damu da tunawa ya hana su fadawa jikinsa ba, ko jikin wani namijin haka kawai ba, shi kansa sai da ya ji kwala ta cika idannuwansa sannan ya yi mamakin yanda mamansa ta girma a dan lokacin nan fuskarta ta nuna alamun ta nutsu.

A hankali ya cirata a jikinsa yana kallonta ya ce" ya isa haka ko Uwata?

Tana haki da komai ta ce" Aba, ba guduwa na yi ba Abana, Abana ka min auren da du wanda ka zaba min na maka alkawarin da zauna da shi koda kuwa yankan naman jikina yake, Abana ka yafe min, ina mamana? Abana ka san inda aka kai ni? Ka san me aka min? Abana gidan yarin *KUTKALE* aka kai ni a matsayin wace ta yi laifi na zama budurwar dan ta.ada, Abana daga nan aka kai ni .....

*UWATA* ya fada cikin nutsuwa yana kallonta,

Han??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????nunsa ya saka ya share hawayenta sannan ya ce" Abdallah ya je ya fada min,

Shiru ta yi tana kallonsa, sai a lokacin mamaki ya kamata na jin wai Abdallah ya je wajen mahaifinya ya fada masa wannan maganar,
Ikon Allah, sai yanzu tunanin me ya zo yi asibitin ya dirar mata,

Dubanta ta kai cikin dakin marar lafiar nan ta hango Abdul kuri su yake kallo
Gabanta ne ta ji ya yanke ya fadi lokaci daya kuma ta damki hannun mahaifinta a hankali ta ce" Abana, ya farka

Malan ya kai dubansa wajen Abdul din, ya ga gaba daya hankalinsa a kansu dan haka ya ja hannunta da niyar shiga da ita, sai dai ga mamakinsa hannun ne ya fara rawa ta kasa motsawa harma ta iya furta cewa" Aba

Tsayawa ya kuma yi da mamaki ya kalli yannayinta, a hankali ya cika hannun nata sannan ya juya ya shiga dakin , sai dai ya kasa rufe kofar dan du ji yake idan ya rufe ba zai bude ya kuma ganninta a wajen ba

BS ne ya zo ya yi mata magana fuskarsa a tamke hakan ya sakata bin bayansa suka je suka tsaya nesa da dakin, bai ce da ita komai ba sai dai shirun da ya yi shima yana kallon waje daya kamar yanda ya ga hankalinta ya raja.a dakin da mahaifinta da kuma Abdul ke ciki

Tun da malan ya shiga ya nemi waje ya zauna, ba abinda yake karantawa Abdul sai girman hakuri mahinmancinsa da sakamakon da ake samu mai kyau idan an yi shi,
Jarabawar da ya shiga mai girma da duhu ya ringa bashi baki da musalai da kuma ribar da zai samu idan ya yi hakuri da ita a hakan,

Shiru ya yi yana kallon yanda Abdul ke kallon kasa bai ce da shi komai ba
Ci gaba ya yi da bashi baki, da nuna masa kar ya dauki maganar cewa zai dauki fansa shima, hakan ba zai kai shi ga ci ba, ba zai samu wata nasara ba

Abdul ya dago idannuwansa da suka yi jajajir da mugun nauyin da sukai masa ya sauke a kan malan
Sai da ya hadiyi yawu mai daci da kuma yauki a hankali ya ce" ba komai *ABA, ALLAH YA JIKAN DU WA.INDA SUKA MUTU*
Sai da ya ji zuciyarsa ta girgiza, ba komai fa yace? Tabas yana iya karbar abin aman ba komai din na lokaci daya ya bashi mamaki, ko dan yana cikin hali na rashin dadin yannayi shi sai ya ce kamar yau baya cikin yan magana ma,

Ajiyar zuciya ya sauke ya mike da niyar fita, sai dai muryar Abdul ta dawo da shi cewa" Aba,
Dama amini na zama makiyi? Aba dama alkhairi na jazawa mutun kiyaya? Aba, shin a gabanan zan iya yarda da wani dan adam komai kusancina da shi kuwa?

Aba ashe aminina ya kashe min kanwata? Ya kashe min mahaifiyata? Ya kashe mutanen dake tare da ni? Du dan ya kai ni ga ciwon hauka kafin na bar duniya? Aba........zuciyata sai nake jin tamkar ba zata kuma gannin haske ba, ji nake tamkar na gama da farin ciki, idannuwana na gannin kowa da fuska biyu, *ABA, shin me zai saka na yarda da kai kanka?*





Halin rudani na rudar da zukatanmu a likacin da wani lamari ya dake mu=??, sauki na Allah ne

>???=???>???=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>???=???>???


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




4?? 5??

Sai da ta yiwa kanta fada kan irin rikicewar da ta yi dan kawai ya rubuto mata haka sannan ta rubuta" *NI KUWA, BANA JIN KEWAR KA*

murmushi ya saki , sannan ya ki bata amsa ya dai kurawa magangannun su ido yana kallo haka kuma Na.ima dake gefensa tana kallonsa bata dai san me yake yi a waya ba, aman kuma ta ga ya bada hankalinsa sosai hasalima bai san ta farka daga bacin gajiyar da ya tara mata ba

Hafsat dake jiran gannin amsarsa na ya rama da fada fada ta ji shiru sai abin ya dameta,
Tunani ta yi kan yanzu fa ba aiki take masa ba, mutun ya nuna damuwarsa a kanka bai dace ka yi masa abinda zai iya taba ransa

A hankali ta rubuta message kamar haka" *Yaya jikin ka?*

Mikewa ya yi zaune yana murmushi mai sauti, sannan ya bata amsa da" bani da lafia ne?

Hafsat ta yi shiru da wayar a hannunta, ajiyar zuciya ta sauke sannan ta rubuta" *malan meye wai? Zakana wani neman bani wahala ka manta da maman malan kake magana?*

Wannan karron har sai da ya buda hakoransa wajen murmushi, a fili ya ce" come on, relache toi, i really miss yannayinki,

Na.ima dake kallonsa ce ta yi motsi irin wanda zai saka shi gane ta farka

A hankali ya kai dubansa kanta, bata sanye da riga sai gajeran wando baki mai santsi
Yan berayan mamanta ya kalla haka kawai lokaci daya siffar Hafsat ta fado a ransa

Wani irin mikewa ya yi tsaye ya rintse ido lokaci daya, a hankali ya yi baya baya ya jingijar da bayansa jikin garun wajen,

Sai da ya jima a jaka kafij ya buda idannuwansa ya ga dai kuri shi take kallo

Takowa ya yi inda take ya tsaya mata kerere yana kallonta ya ce" ki daina zamarmin ba riga dan Allah, idan nemanki na yi ina gamawa ki saka rigarki....hakan zai sama min kwonciyar hankali

Yana gama fada ya juya ya nufi bayi ,
Da kallo ta raka shi tana mamaki halayarsa,
Mikewa ta yi ta shiga saka rigar a kasan zuciyarta kuwa ayyanawa take cewa.... ban san yaushe zan fahimceka ba, tanzun kuma wane zan yi? Nan ka ce da ni na ringa zama ba kaya, nicema nake saka wandon nan dan ba zan iya zama haka ba, kuma yanzu kaine da cewa na ringa saka kaya hankalinka zai fi kwonciya?

Tana gama sakawa wayarsa ta dauko ta ajiye masa gefen gado ta yi tsuru tana kallon wayar, da wa yake magana? Da wa yake nishadi har haka? Wacece ita? Wata dabara, wani irin kyau, ko wani irin iya girki ta iya wanda ya saka shi sakewa da ita har haka?

Gabanta ne ta ji ya fadin mata lokaci daya, ta sani ba tun yau ba ko ba dade ko ba jima Abdul sai ya kara aure dan kuwa a da can ma ta san da ba mijin mace daya bane bare a yanzu da yake jajan wai dama haka take da son jiki?
Tsoro ne ta ji ya rufe mata zuciya lokaci daya, in dai wannan da yake magana da ita budurwarsa ce kuma aurenta zai yi ai kuwa da zaune bata sameta ba, tabas da ta hadu da tsayuwa kennan, dan tana tunanin auren so kennan, ganninsa ma zai iya yi mata wahala

Tana cikin tunanin ta ji ya janyota baya, wato saman bed din, gaba dayanta ta tafi jikinsa a hankali ya saka hannunsa cikin rigarta sannan ya ja hannunta ya kai wani sashe na jikinsa daban wanda ya sakata jin gabanta ya kwonci kwonci ya fadi, aman da yake yanzu ta gama daukarwa kanta niyar gwada juriyar sai ta rintse ido ta shiga bashi hadin kai du da irin tarin tsoron kasancewarsu abu daya,


Hafsat dake jiran amsa shiru shiru haushi ne ya isheta, cike da jin haushi ta ajiye wayar kasa ba saman bed dinta ba dan kuwa an hanata ajiye waya kusa da kai dan babu kyau yana hadasa rashin lafia

Kwonciya ta yi saman hannunta na dama bayan ta gama adu.ar baci ta yi shiru tana kallon waje daya

Wani uban tsaki ta ja ta mike ta zauna saman gadon tana kallon waje daya

A fili ta saki wata yar karamar dariya kafin ta tafa hannayenta, hannun nata ta dago ta zunguri kanta a fili ta ce" Hafsat baki da mutunci, ke da zaki yi baci kina mai yabon ma.aiki aa sai kawai ki je duniyar baci kina hangen rayuwarki ta Bodyguard? Rayuwar ta hatsari? Wace har harbi akai maki a can? Wajen da kika hadu da dan rainin hankalin nan wato Abdul?

Kanta ta girgiza ta ce" to ki yiwa kanki fada, ki yi aurenki ki tafi abinki, ki je ki yiwa BS biyaya, .....

A daren nan ta jima tana kokowa kafin baci ya dauketa , hakan ya sa da asuba sai da mama ta shigo dakinta da kanta ta tasheta tana yi mata fadan cika dare dan kar ta fara makara a sallah kuma!


Ranar Lahadi da yama wajen karfe biyar Hafsat ta gama shirinta tsaf cikin sabin suturunta sannan sabin shiga a wajenta wanda ta mayar shigarta na yanzu wato Abaya

Ta yane kanta, fuskarta ta gyarata daidai misali ba abinda ta saka mai yawa ko mai daukan hankali sosai aman a banza dan kuwa irin yanda hankali ke kaiwa kanta abin ba.a cewa komai

Ta jima duke dakin malan tana shafa fatiyar adu.ar tsarin da yake ta binta da ita, shi kam dan an fito masa da cewa haka zata yi ta zama a gida sannan aka daure shi cewa ai Allah ke tsarewa da shi aka bi, da ba zai taba yarda ta fita ba sai dai idan za.a kaita dakin mijinta


Sai da ya gama sannan ya dauki kudi jika biyu ya bata tare da cewa ta shiga taxi idan ta gaji

Mama dake tsaye murmushi kawai take zubawa, a ranta kuwa fadi take wai a nan malan gani yake yana mugun kokari na boye soyayar yar tasa, yanzu ba fita bane zata yi? Ta tabata ta siyarwa kanta

32 / 54