Author : Hajara L Sadeq Category : Romance
wlh zargin Aira tare da Buzun nan nake nan ta bata labarin duk abubuwan da take gani a tare da su"Dafota Sa a tayi ta ce "Meye abun had'a jijiyoyin wuya Ai wannan babbar dama ce ta samemu da zamu fitar da shegiyar yarinyar nan daurewa kawai kikaga inayi amma babanki yanzu zaman hakuri kawai nake dashi hankalinshi duka yana kan figigiyar yarinyar chan Dan haka ki k'ara sanya musa ido sosai har lokacin da zaki kamasu Turmi da tabarya Kinga daga nan ai ko ta gwal ce ya saketa " Goge hawayenta Laila tayi ta ce "Mama son buzun fa nake " Harara ta galla mata ta ce "Ke bansan shirme ki rasa Wanda zakiso sai na kasa dake wuce kiban waje sannan kiyi abunda nace kinji" gyada mata kai tayi ta ce "Insha Allahu Mama" Tundaga ranar Laila ta k'ara sanya musu ido sosai.
Yau Aira tunda ta tashi ta tashi da zazzabi mai tsananin gaske ga ciwon ciki da ya addabeta ko fitowa ta kasa Haka ta yini a d'aki rufe cikin bargo Koda Alhaji Yusuf ya leko ya sameta a wannan halin sosai ya damu tare da cewa ta shirya ya kaita Asibiti ta ce "a a a taji sauk'i parasitimol ya b'alla mata Tasha wanda saida ta amayoshi A toilet bayan barinshi dakin .
washegari ma haka Aira ta tashi da wannan zazzab'in Dak'yal dai ta samu harta fito palour abincima dak'yal taci saida Alh ya takura mata Mama ko Sannu ita da Laila basu mata ba a palour ta zauna gefen kujerar da Laila take Amai ne taji yazo mata da gudu ta fad'a toilet d'in palour tare da Fara kwarara amai duk abunda taci saida ta amayar Alh Yusuf shi ya taimaka mata ta gyara jikinta sai Sannu yake yi mata harta fito Mama Ce ta Kalleshi ta ce " Gaskiya ya kamata a kaita Asibiti tunda naga Ta fara galabaita "Eh daman asibitin kawai zamu ya fad'a yana Mikewa tare da Kallon Aira ya ce " Jeki sanyo Hijab d'inki "Ba Dan Aira tasoba taje ta sanyo hijab Hajiya saudema Mikewa tayi tace muje Tare Laila ko sai aikawa da Aira harara take har suka fito a lokacin Arman Na wajen mai gadi suna d'an hira Kad'an yana ganinsu Ya taso tare da cewa Alhaji lafiya " nuna mashi Aira yayi data tsugunna Dan ta kasa jurar tsawuyar ya ce "Amarya ce zamu kai Asibiti ba lafiya " Subhanalla Arman ya fad'a tare da cewa Allah ya bata lafiya Aira na jinshi bata d'agoba Arman ya ce "To bari na d'auko motar na kaiku" A a a ka barshi zan tuk'a da kaina Alhaji Yusuf ya fad'a tare da nufar parking space ya d'auko mota Arman ko sai kallon Aira yake tama d'ago taki Dagowa Saida Mama saude ta mik'ar da ita tare da kama hannunta suka shiga mota a lokacin ne Arman ya kalli fuskarta sosai yaga ta fad'a da ka ganta kaga marar lafiya saiyaji daman ciwon ya dawo jikinshi dukda baisan abunda ke damunshi ba a haka har motarsu ta fice daga gidan koda suka isa Asibiti basu bi wani layi ba saboda Dr d'in d'an Yayar Alhaji ne hakan yasa aka amshesu cikin mutuntawa gashi daman private hospital ne "Kallonta Dr Luqman yayi ya ce " Me yake damunki"Cikin k'arfin hali ta ce "Tun shekaranjiya ne nakejin zazzabi to jiya da yau yafi matsamun " Kina amai ko jin tashin zuciya? A a banajin tashin zuciya Amma dai jiya da dazu nayi amai"Kallon nurse Yayi ya ce "Kuje da ita lab ki fara mata gwajin fitsari?A tare da Nurse din Suka nufi lab ta dauki jininta tare da fitsarinta Tukwana Aira ta dawo office d'in Inda ta tarar Alh suna Hira da Dr Jan kujera tayi ta zauna tare da buga tagumi Ba ayi 20 minutes ba Nurse d'in ta dawo tare da Result a hannunta ta mik'awa Dr Amsa yayi tare da fara karantawa Yana gama karantawa cike da Fara'a ya d'ago ya kalli Daddy tare da cewa " Congratulations Alhaji ur Wife she's pregnant for 4 months Allah ya raba lafiya"A tare Alhaji da saude suka Mike sukace " Ciki wata hud'u Luqman"!!!!! Aira ma cikin tsananin tashin hankali ta mik'e ta ce ciki Kuma Dr.........โ๐ฟ
*Tofa wata sabuwa ana wata ga wata me ya had'a Aira da ciki Kuma*๐๐ฏ
_*Miss Hajo ce*_๐ค๐ฟ
[7/7, 16:40] Hajo hajo: ๐
ฟ๏ธ...........*85&86*
Ciki Kuma Dr Gaskiya ka duba badai niba"Shima Alhaji cewa yayi kadai duba Luqman "Mik'a musu Result d'in yayi gashi ku gani da idonku Alhaji shekara nawa ina Aikin nan Ciki ne da ita wata hud'u ma kuwa " Amsar takardar Daddy yayi tare da karantawa yagani Tabbas cikine wata hud'u "Cikin tsananin tashin hankali Ya kalli Aira ta ta ma rasa Inda hankalinta yake tsabar rud'u ya ce " Cikin uban waye"Kuka Aira ta fara tana hawaye sosai Tare da Jan baya ta ce "Nima bansaniba Wlh Daddy" Da mamaki Luqman yake kallonsu Ya ce "Me kake nufi Daddy kaida Matarka " dafe kai Daddy yayi sai sannan ya tuna gaban Dr suke "Mungode Dr ya fad'a tare da fardar hannun Aira yayi waje da ita ba abunda take In banda kuka Cikin Sauri Hajiya saude ta bisu Tana " Allah ya k'ara a cikin ranta "Yana zuwa back sit ya wullata tare da rufewa Hajiya saude ganin haka cikin Sauri ta maza ta shiga gaba kafinma ta k'arasa rife kofa yaja motar a guje Airako Had'e kanta tayi da gwaiwa tana kuka mai cin rai to ita mema zai had'ata da ciki Alhaji Yusuf ko baka tab'a Tantance irin b'acin ran da yake ciki Suna isa cikin b'acin rai ya fito tare da fito da Aira ya jata bai dire ta ko ina ba sai palour ya wullata kan kujera tare da wanketa da wani wawan Mari rik'e kumcinta tayi Dan sosai Marin ya shigeta tare da fashewa da kuka shak'eta yayi ya ce " Cikin uban waye kikazomun gida dashi Dan ubanki"nima bansaniba Daddy "ta fad'a cikin kuka Kara shak'eta yayi ya ce " bazaki fadamunba har saina sauya maki kamanni "sosai Aira take kuka duk ta rikice tama kasa maidamai Laila ko Mamaki tayi ta ce " Ciki Kuma "Daddy ko Kara wanke Aira yayi da wani Marin da yafi na d'azu ya ce " bazaki fadamunba har saina sauya miki halitta "Hajiya saude ce da takejin ranta kall taje ta rikeshi ta ce " Karka illata ta Alhaji kabari abi komai a Sannu har a samu ta fad'a Wanda yayi mata d'in"Cikin huci ya nuna Aira da yatsa ya ce "Kin ban mamaki wlh bantab'a zaton haka halinki yake ba y,ar iska kawai " Aira ko sosai take kuka gwanin tausayi Tana ganin ya sake shakewar da yayi mata da gudu ta ruga ta fad'a d'akinta Tare da kullewa a jikin kofar ta durkushe ta fashe da kuka maicin rai Ta ce "wannan wace irin jarabawa ce bata rabu da bibiyata ba ni Aira na shiga Ukku to cikin waye jikina Bayan Bantab'a zina ba Sosai take kuka tunowa da Ranar da Arman yayi kokarin Tab'ata a hotel tayi saurin Mikewa tare da dafe saitin zuciyarta ta ce " na shiga ukku yaya Arman Kardai kai kayimun sosai ta k'ara fashewa da kuka ga wani azababben zazzabi da ya k'ara rufeta sosai take kuka a d'akin Daddy ko cike da tashin hankali ya zauna tare da dafe kanshi Hajiya saude ce tace kayi hakuri Alhaji To amma kai kana ganin ba cikin ka bane kuwa"Wani banzan kallo ya watsa mata ya ce "a gidan ubanwa ya zama nawa yarinyar da ba abunda ya tab'a shiga tsakaninmu" Dariya Hajiya saude tasoyi Ta fusge a ranta ta ce "Ai yau dole nayi rawa da wak'a duk dai d'okin da ake akan amarya saiga amarya tayi abun Kunya " Laila ko sosai taji tsanar Aira a ranta Arman ko yana ganin dawowarsu Aira da lokacin da Daddy Ya jata sosai ya shiga rud'u yanason ya ji abunda yake faruwa Amma ba dama Sukuku ya yini ranar Har karfe sha biyun Dare Aira na d'aki tana kuka saurin Mikewa tayi tanajin kanta kamar zai rabe gida biyu ta bud'e d'akin ta lek'a taga ba kowa cikin Sauri tabar part d'in tare da nufar BQ d'akin Arman Wanda dak'yal take tafiya tana tangadi harta isa zaune ta sameshi yayi tagumi Dagowa yayi ya Kalleta Itama din shi take kallo da gudu ta fad'a Jikinshi tare da fashewa da matsanancin kuka Sosai Arman ya shiga tashin hankali cike da damuwa ya shiga tambayarta me yake faruwa Amma ta kasa amsa mashi sai kukan da take tadau minti ashirin tana kuka batare da tace komai ba 'cike da damuwa ya ce Kin tayarmun da hankali cutie ki fad'amun me yake faruwa kin sanyani cikin duhu"Cikin shashekar kuka ta ce Yaya na shiga Ukku wai ciki ne dani"a zabure Arman ya Mike tare da rik'eta ya ce "What ciki fa kikace Aira ni na shiga ukku ba ke ba Daman Baki rik'emun Amanar da na bakiba Aira saida kikaba tsohon banzan nan kanki" cikin kuka ta ce "Yaya Wlh banbashi kaina ba bai tab'amun komai ba yaya kawai dazu muna zuwa Asibiti Dr ya ce Wai Ciki garan wata hud'u kuma Auren wata Ukku dayi Shima Kanshi Tuhumata yake dazu dak'yal nasha akan saina fito da Wanda yayi mun Bayan nima bansaniba" ta k'arasa fad'a cikin kuka mai cin rai "Sosai Arman ya shiga rud'u da damuwa Kallonta yayi ya ce " Kin tabbatar bai tab'a miki komai ba ko da bakya cikin hayyacinki"na rantse maka da Allah yaya bai tab'amun komai ba"Ajiyar zuciya Arman ya sauke tare da zaunawa itama ya zaunar da ita cikin k'arfin hali ya ce "To cikin waye Aira karki b'oyemun kinsan duk tsanani bazan tab'a gujarkiba ki fad'amun cikin waye ko wani ya tab'a miki fyade" Cikin kuka ta ce "Yaya wlh nima bansaniba Saidai idan cikinka ne" What cikina kuma Aira "ya fad'a da mamaki" Eh Yaya saidai in kai kayimun ka fad'amun Ranar nan Idan akwai abunda ya shiga tsakaninmu yaya Dan Allah karka b'oyemun ka fad'amun karka sanyani cikin wani hali"tashin hankali ba a gwada maka rana Arman cike da damuwa ya ce "Harfa da Qur'an na rantse maki Sannan idan nayi maki wani Abu aike kanki kinsani me yasa wai baki ganewane Aira babu abunda nayi maki wallahi tallahi ban tab'a zina ba Kuma banyi dake ba" Karawa kukanta volume Aira tayi ta ce "To yaya idan ba kai ba wa yayimun?Dafe kanshi Arman yayi ya ce " Ke zan tambaya Aira"Kuka ta fashe dashi sosai tace "Yaya wlh nima bansaniba nima na rantse maka da Allah bantaba zina ba idan na tab'a kar Allah yayi mini Rahama duniya da lahira Allah dawwamar dani cikin wutar jaha....saurin rufe mata baki Arman yayi tare da girgiza mata kai ya ce " karkiyi irin wannan rantsuwar cutie na yarda dake d'ari bisa d'ari dukta kare dai akwai lauje cikin nad'i"Fad'awa jikinshi Aira tayi tana ci gaba da kuka har karfe biyun dare Arman na Lallashinta dak'yal ya dinga daddabata ga jikinta da yayi rauu yad'au zafi Alamun zazzabi sosai ya tausaya mata. A haka har wani wahalallen bacci ya kwasheta a jikinshi sosai Arman ya shiga rud'u da damuwa akan cikin da akace Aira na da shi sai wajen hud'u na dare Shima wani wahalallen bacci ya daukeshi kanta na saman k'irjinshi yayinda shi kuma kanshi yake saman pillow.Daren ranar ba neman da Daddy bai yiwa Aira ba Amma bata part din d'akinta a bud'e palour ya zauna yaga ta Inda zata bullo amma ba ita ba labarinta a haka har bacci ya daukeshi washegari tunda Safe su Laila da Mama sun fito kallonsu yayi ya ce "Ina Aira ?da mamaki suke Kallonshi sukace Aira kuma ai Alhaji rabonmu da ita tun Bayan dawowarmu daga Asibiti" cikin tsananin tashin hankali ya ce "To ina ta kwana badai guduwa tayi ba " ya fad'a yana Mikewa "Laila ce ta ce " Dukta k'are a d'akin buzu ta kwana?What buzu fa kikace Laila "Eh Daddy Daman Tasha zuwa wajenshi nasha ganinsu tare har inama zarginsu banason dai na fadane ace na musu sharri amma Aira da Buzun nan take tare" kin tabbata Laila ba sharri kike musu ba "Wlh dady ba sharri nake musu ba muje Chan din mu gano Daddy kamar zai tashi sama haka suka fito Laila da Mama na biye dashi A haka har suka isa BQ d'in Suna yaye labulan d'akin suka same Aira da Arman suna bacci mak'ale da juna" Cikin tsananin tashin hankali dukansu suke kallonsu da mamaki kallon Daddy Laila tayi ta ce"Kagani Daddy Daman na fad'a maka"Daddy ko ya kasa magana tsabar tashin hankalin da yake ciki"ita kanta Mama saida tayi mamakin al'amarin nan cikin zafin Rai Daddy Ya buga kyauren d'akin da karfi ya ce "ku tashi y'an iska Yau asirinku ya tonu" Firgit suka Mike A tare Murza idonta Aira ta fara harta budesu ya sauka akan su Mama wara idanunta tayi ta kalli Arman da Shima su d'in yake kallo Bayan Arman ta koma Tare da boyewa ta ce "Yaya karka bari su dakeni" yaya Laila ta maimaita "Alhaji ko cikin zafin nama ya shake Arman ya ce " Daman kwarto na Aje gidana bansaniba Dโan iska na janyoka daga rana na sanyaka inuwa ka rasa dame zaka sakamun sai da haka tare da matata ta Dan cin amana yau zanga Wanda zai kwaceku a wajena duk saina kasheku '"Cikin tsananin Zafin rai Arman ya fusge chukumar da Alh yayi mashi tare da Wulli dashi har saida yayi taga taga zai fad'i Cikin masifa Arman ya ce "Kai harka isa ka dangantani da kazamiyar kalma waye kai a k'asar nan ta ubanwa kake ci to idan baka saniba yau ka Sani Ni ba kaskastacce bane ba Rashin Kudi ya kawoni gidanka ba soyayya ta kawoni gidanka soyayyar Wacce ka yi sanadiyar rabewar alak'armu Ba kaskantaccen buzun da kake tunani bane a gabanka Mujahed Kabir Umar kake magana dashi " cike da mamaki Alhaji ya ce "Mujahid Kabir Umar d'an gidan gwamnan kano kake nufi?su kansu su Mama saida sukayi mamaki musamman Laila kenan Arman din Aira ne shiyasa Duk sanda ta nuna tana sonshi take kishi Haba no wonder daman tasan mutumin nan baiyi kama da k'aramun mutumba Alhaji Yusuf ko cike da masifa ya ce " daman yaudara ta kayi Arman ne daman ?tsaki Arman yaja ya ce "Abunda yafi yaudara soko kawai tsohon najadu โChabd'i Alhaji ya fad'a tare da Kallon Aira da duk ta tsure cikin Tsawa ya ce "Waye uban cikinki kinsan dai karya kike ki lak'amun shege Bayan Kinsan ba nawa bane " Nine nan uban cikin nine nan na mata "Arman ya fad'a yana nuna kanshi duk a mamaki suke Kallonshi musamman Daddy da Yama kasa magana cikin k'arfin hali ya ce " Lallai Alh Abubakar ya cuceni daman yasan da ciki ya auramun ita shiyasa yasa gaggawa a bikin Dan kar asirinshi ya tonu ni ya tonamun nau "Mama ko cewa tayi Haba shiyasa Nayi mamakin Ace idan ba kangara yarinyar nan tayiba iyayenta su baka ita amma an cucemu wlh wannan ai b'acin suna ne " Kallon ta Alh yusuf yayi ya ce "Kansu zasu b'atawa suna ba dai niba Sannan ya kalli Aira ya ce " Kije na sakeki sake ki saki d'aya!!Duk tashin hankalin da Aira take ciki baihanata sauke ajiyar zuciya ba Hajiya saude ce ta ce "Alhaji meye abun saki d'aya kuma saki Ukku zakayi mata me zakayi da y'ar iska kuma " kallonta yayi ya ce "Kuma fa hakane sannan ya k'ara kallon Aira yace na sakeki saki biyu na sakeki saki Ukku " Ajiyar zuciya saude ta sauke Arman ko baka iya Tantance yanayin da yake ciki Fard'o hannun Aira yayi tare da nufar hanya kofa da ita cikin taananin bacin rai ya ce "Ku bamu hanya mu wuce" Cikin masifa Daddy Ya ce "Gidan ubanwa zaka da ita ai baka isa kaje ko ina da ita ba kamar yanda daga gidan ubanta na daukota hakan zan mayar masa da tsiyarsa............โ๐ฟ
*Ki biya ki karanta cikin nutsuwa 200 ta wannan number 07026166536*
_*Miss Hajo ce*_๐ค๐ฟ
[7/8, 20:01] Hajo hajo: ๐
ฟ๏ธ...........*87&88*
..Haka zan mayar masa da tsiyarsa "Cikin tsananin b'acin rai Arman yace wannan ne kuma baka isa ba ko kai wanene yana gama fad'ar ya fisgi Aira tare da bangajeshi yayi waje da ita janta kawai yake kamar zai tashi sama da ita A haka har suka bar cikin gidan Sosai Aira take kuka Wanda Arman jin kukan nata yake har cikin ranshi Alhaji ne da duk ya tashi hankalinshi Kallon Saude yayi ya ce " ji nake zuciyata kamar zata fashe saude "Haba Alhaji akanme zaka damu hankalinka Tunda Allah ya Rabaka da k'aya ai gwarama da ya tafi d'in da ita kuma zaman me zatayi mana a gida kamata fa akayi banda Cikin da tazo maka dashi gida kaidai kawai an cuceka wlh wannan Auren masifa ya zame maka" Numfasawa yayi ya ce "Alhaji Abubakar zaisan ni yayiwa haka wlh duk abunda na kashe sai ambiya ni Aure ko masifa ba abunda na Mora da Auren sai masifa wlh bazanyi asarar kudinaba hatta cida ta din da nayi saiya biyani yana gama fad'ar haka Fuuu yabar wajen Laila da Mama suka bishi Aira ko suna fita hanya Suka mik'a Arman xaka Kalleshi kasan ba k'aramun b'acin rai yake cikinshiba janta kawai yake Ita kuma sai kuka take sunyi nisa sosai Ja yayi ya tsaya tare da kallonta cikin b'acin rai ya ce " Kukan me kikemun ko so kike ki koma gidan matsiyacin chan ?Girgiza mashi kai tayi ta ce "A a a yaya ina tsoron Abba ne Idan yaji abun nan nasan tsinemun zaiyi ta k'arasa fad'a tana rushewa da kuka" Sosai ta bashi tausayi Hakan ya sanyashi saurin Saukowa cikin lallashi ya ce "Kiyi shiru ki daina kukan nan Hamdala zakiyi da Allah ya rabaki da k'addararran Auren nan sannan bazai tsine miki ba