Author : Hajara L Sadeq Category : Romance
nan wlh duk hukuncin da ka yanke mun na yarda dashi amma ka janye wannan " ta karasa fad'a tare da durk'ushewa tana fashewa da kuka mai tab'a zuciya cikin tashin hankali Mama ta ce "Haba Alhaji wannan ai ba adalci bane taya zaka Aurawa y'arka tsohon nan " Aysha ko rik'e Aira tayi da ta haukace ta ke risgar kuka Ta kalli Abba ta ce "Abba Dan Allah Inda wasa kake ka fad'a mana" Mamy batasan lokacin da wani kuka ya Kufce mata ba cikin kuka ta ce "Daman nasan Ba kaunata kake ba Nida y'ata inbanda Rashin so da Rashin Adalci Duka cikin Y'ay'anka wa ka tab'a yiwa haka wak'a tab'a Aurawa tsoho Duka gatan da kakewa Y'ay'anka babu d'aya da kayiwa y'ata Wlh Alh nayi maka Allah ya isa saita bika chutata kawai kake ko ni uwarta a zamaninmu ma Anyimun Haka na yarda bare ita" Ta k'arasa fad'a cikin kuka Abba ne ya ce "Daman wannan ranar nake jiran zuwanta Duka kince cikin y'ay'ana babu wacce na tab'a yiwa haka bakiyi karya ba Amma ki duba kiga cikin y'ay'ana babu wacce ta tab'a yimun kwatar abunda y'arki tayimun Aira ta kwana A waje,ta fita cikin dare sunje sun had'a iskanci a idon duniya Wanda cikin y'ay'ana ko a cikin gida basu tab'a hadawa ba,na hanata Abu tayi" na rabata da Yaron Chan yafi a k'irga amma tak’i rabuwa dashi ,ido k'arara ta rainani zan fadi magana yanzu kafin a jima ta take ta a idonki ido na Bayan na k'ara rabasu muka gansu a kofar gida ,sannan ko ranar da ta fita Ke da kike d'aure mata gindi Kika kareta to a mota naje shan round na ganta ita dashi na kyaleku ne.kawai naga gudun ruwanku sannan duk sayayyar da take shigowa gidan nan akan idona Yarinyar Chan bama nema take ta kangare ba ta Riga da ta kangaremun ta lalace yaron Chan ya iskantata Dan haka wlh ba a gida na ba ban haifi d'an da zai kunyatani a idon duniya ba duk k'ok'arin da zanyi nabata tarbiya Inma ke kika koya mata Rashin tarbiya to ga k'arshen abun yau na kawo Idan Kinga Anfasa auran nan Saidai in bana numfashi kuma godewa Allah da zamu Aurar da ita Bata d'auko mana magana ba "Mamy sosai take kuka ta kasa maidawa ma Abba magana Aira ko tuni ta haukace fisgewa tayi daga hannun Aysha ta Ruga ta rik'e k'afar Abba ta ce "Wlh Allah bazan yarda ba ni Inma Auren ne Abba wlh ni Yaya Arman nakeso A Auramun inshine wlh ko yanzu na yarda Dan Allah karka Auramun tsohon najadun nan Wlh Abba bani ba ko Mamy ya Haifa " D'auketa da Mari Abba yayi ba arziki ta sakeshi tare da kama kumcinta Abba ko tsallaketa yayi ya fice daga d'akin Aira na mik'ewa Goron ta D'auka ta wullashi tare da warwareshi a d'akin da dinga watsi da kayan d'aurin Auren ta hau watsasu tana kuka tana sabbatu ruk'ota Aysha Da Amma sukayi da suma kuka suke "Rungume Aysha tayi ta ce " Aunty shikenan Abba ya kasheni wlh ni yaya Arman nakeso Allah idan suka rabamu mutuwa zamiyi Aunty ku taimakamun ku ce Abba ya fasa Dan Allah"Rungumeta Aysha tayi ta ce "Kiyi hakuri ki nutsu" Fisgewa Aira tayi taje ta fad'a kan Mamy dake kuka ta ce "Mamy ki taimakamun kar Abba ya auramun tsohon nan mamy wai Dan Allah Abba baida magaya da zanje na samesu Dan Allah idan kinsan wani Wanda yakejin tsoro ki fad'amun ko shi baida mafad'a"kasa daga baki Mamy tayi magana d'anji take zuciyarta kamar zata rabe gida biyu Kamar wacce aka tsunkula Aira Haka ta tashi tare da rugawa da gudu tayi waje Binta Aysha sukayi Amma ta ruga ko kallabi kanta babu haka ta fito ko Baba mai gadi bata saurara ba ta bud'e kofa ta fice a guje Binta Aysha Da Amma sukayi suna cewa" ina zaki Aira ki dawo wai baki da hankali"Tana fita Aira gudu kawai take Ganin su Aysha sun biyota ya sanyata tsaida napep Mai napep din kanshi saida ya tsorata da yanayin ta Amma Hakanan ya d'auke ta tunda ta shiga kuka kawai take mai napep ya ce "Hajiya ina za a kaiki cikin kuka ta ce Hotoro su Aysha ganin ta hau napep cikeda firgice suka koma suna zuwa Suka tarar da Inna gaban Abba sai surfa masifa ta ke ta na cewa"wannan Ai zaluncine Habubakar zakayiwa y'arka to wlh indai na isa dakai kaje ka mayar musu da kayan auran su kai dama ban isa da kai ba ka rainani kodan bani na haifeka ba " cikin girmamawa Abba ya lallab'ata Inna ya ce "to shikenan kiyi hakuri Inna za a mayar musu Dan Allah ki koma ki kwantar da hankalinki " Dak'yal Abba ya samu ya lallaba Inna ta koma part d'inta sai famfami take Su Aysha ne cike da damuwa ta ce "Abba Aira fa ta Ruga bako kallabi mun bita ta tari napep Dan Allah a fito da mota mu bita karta shiga wani halin" Tsawa Abba ya daka wa Aisha ya ce "wuce ku ban wuri " ba arziki Aysha suka koma ciki Sai kuka take da magriba mijinta yazo zai d'auketa ta ce "ba Inda zata ba yanda ya iya sai komawa yayi Dan tace sai gobe.
Aira a napep ma sai kuka take mai napep ya dinga bata hakuri ya ce " sai hakuri baiwar Allah dukkan mai rai mamacine"Dan a tunaninshi mutuwace aka mata ita dai Aira bata tanka shiba har suka isa Hotoro suna zuwa inda zata ta ce ya isa tana sauka ta hau buga gidan da karfi ta na kuka a lokacin har ankira magriba mai napep kam girgiza kai yayi ya wuce Dan ko kudi bata bashiba Aira na cikin bubbugawa Khady ta fito ta bud'e kallon Aira tayi ta ce "Lafiya ke kuma" Aira ba ta ko saurareta ba ta bangajeta tayi ciki "yaya Umar yaya Umar kawai take fad'a harta isa palourn Tana zuwa ta sameshi yana shirin fita Sallah fad'awa jikinshi Aira tayi tareda sakin kuka cikin tashin hankali Umar ya ce " Lafiya Aira waye ya mutu ko ba lafiya "cikin kuka ta ce " Yaya Abba ne...Abba ne yayi me ya Umar ya fad'a cikin tashin hankali Dan a tunaninshi wani abun ne ya samu Abban Kuka ta k'ara fashewa dashi ta ce "Abba ne ya ce zai auramun Abokinshi wai har sun sanya Aure wlh yaya mutuwa zanyi karkaga tsohon ya haifi Mamy Dan Allah kaje ka hana shi Nasan kaikad'aine magayinshi" Daddab'a bayanta yaya Umar yayi ya ce "Subhanallahi kiyi shiru yanzu zauna naje nayi salla saimu tafi gidan insha Allahu bazai aura maki ba " zaunawa Aira tayi ta hade kanta da gwuiwa sai risgar kuka take yaya Umar fasa fitama masallacin yayi ciki ya koma Dan yayi Sallar a gida ya gama su tafi Dan ta rud'ashi Yana shiga ciki Khady dake tsaye taja tsaki ta ce "Allah ya k'ara aniyarki ce ta koma maki ni ai kikaso mijina yamun kishiya kika mak'alamai wata sai gashi Allah ya maida maki aniyarki saikije Chan Allah raka taki gona daman ai kun saba Auren tsaffi uwakkima Auren kud'i tayi waye bai saniba taga Abba yafi k'aninshi kud'i lokacin shiyasa ta aureshi ta had'a y'an uwa gaba Ai gashi nan Alhakine ke ta binku " Aira cike da masifa ta mik'e sosai taji zafin maganganun Khady cikin b'acin rai Ta ce "Alhamdulilla tunda uwata Auren kud'i tayi ke Ai naga uwarki ta samu Mai kudin da ta aura ince ubanki ba shi bane Salisu mai wankin hula a bakin titi Banza y'ar matsiyaciya da kika taso cikin tsiya kin samu wuri shine har zakiyiwa mutane iskanci banza juya wacce ko B'ari bata tab'a shekara Shida Da Aure juya kawai y'ar matsiyata" kasan abunda zaka fad'a bakasan abunda za a mayar maka ba Khady sosai Maganar Aira ta k'ona mata rai Kukan kura tayi ta Kama Aira da dambe ta ce "Yau zakisan ni kika zaga itama Aira Daman ranta a mugun b'ace yake Aiko ta chukunkume Khady suka hau Dambe dukda Aira ke cutuwa Dan Khady Nada jiki Amma k'arfin hali na Aira Farcenta tasa ta yage ta a fuska har saida jini ya fito Yaya Umar ne ya fito Cikin tashin hankali ya shiga rabasu ya ce " meye haka bansan iskanci ubanme ya had'aku.dak'yal ya samu ya rabasu dukansu sai huci suke Khady ta fashe da kukan munafurci ta ce "wai baby daga zuwanta ta hau mun gori wai juya bani haihuwa " Itama Aira kuka take ta ce "Karya take yaya ita ta fara zagi na da Mamy wai Mamy tayi Auren kud'i ta auri Abba Dan yafi Daddy kudi nima wai Allah Kara da za a auramun tsohon" ta fad'a tana Kara rushewa da kuka "D'auke Khady umar yayi da Mari Dan yasan kome akace zata aikata ya ce " Dan iskanci iyayena sa annin kine ina ruwanki da harkar gidanmu nasan kome akace zaki aikata fiye da haka"Rushewa tayi da kuka ta ce "Shine ka mareni gaban kanwarka ka goyi bayanta a kaina Umar" Tsaki Umar yaja sannan ya kalli Aira ya daka mata Tsawa ke kuma da yake sa'arkice har zakiyi dambe da ita wuce muje biyoni "ya fad'a yana bin hanyar fita"Cikin Sauri itama Aira ta bishi juyowa tayi tare da yiwa Khady gwalo zata taso ta Ruga" A motar yaya Umar Aira suka taho suna isowa gida Ya ce "wuce ki shiga ciki zanje na samu Abban" to yaya nagode "tafada tare da shiga ciki idonta duk yayi jawur taranta Aysha tayi ta ce " Alhmdllh ina kikaje duk kin tada mana Hankali "Goge hawayenta Aira tayi ta ce 'gidan yaya Umar tare muke dashi yana part din Abba ya bashi hakuri " Ajiyar zuciya Aisha ta sauke ta ce "Ai nazata wani wajen zaki " ina Mamy"Tana d'akinta "cikin Sauri Aira ta nufi d'akin tana zuwa ta sameta a Gado sai risgar kuka take Amer na kanta shima yana kuka ita har tafi Aira shiga tashin hankali " Fad'awa jikinta Aira tayi itama ta fashe da kukan cikinsu ba mai Lallashin wani "Mama ce ta shigo dak'yal ta rarrashesu ta ce " Haba Rahama kamar yarinya tun d'azu fa ake baki hakuri ko ita Airar batayi kukan da kikayi ba Kara tayar mata da hankali kike keda zaki kwantar mata da hankali"Haba Yaya wlh dole nayi kuka kawai Alh ya cuceni ya zalinceni Aure fa ya sanya mata da sa'anshi kwata kwata ya kashe rayuwar y'ata ta fad'a tana kuka"Cikin kuka Aira ta ce "Mamy wlh ni nasan abunnan bazai yuba Yanzu ma tare muke da yaya Umar yana wajen Abba yana bashi hakuri nasan kila ya hakura " Kallonta Mamy tayi ta ce "duk ba ke kika ja ba duk yanda nake nuna maki kika k'i ki gane shi umar d'in Gidanshi kikaje " Eh Mamy har mukayi fad'a da Matarshi ta fad'a tana saka kuka"Fad'a kuma Mama da Mamy suka fad'a nan Aira ta kwashe komai ta fad'a musu sosai ran Mamy ya b'aci amma ta Danne Mama ko fad'a ta shigayi sosai ta ce "zataci ubanta tunda ita y'ar gidan matsiyata ce zan nuna mata fushi na sannan kinyimun daidai da kika goranta mata tunda ita bata da hankali" Mamy ko cewa tayi "Ai Inda sabo na saba da jin maganganunan Su har yanzu mutane basa Duba Aure da haihuwa yafi gaban wasa wani baya haihuwar d'an wani Kome rubutaccene Amma bakomai Ai akwai Allah duk na barsu da Allah "Ba irin magiyar da yaya Umar baiyiwa Abba ba akan ya janye maganar nan amma yak'i yace ya gama yanke hukunci har Tara Umar na Abu d'aya daga karshe sai tafiya yayi ko ciki bai koma ba Dan baisan ya iskesu cikin tashin hankali Ranar Aira daki daya sukakwan da su Aysha kuka tayi ta risga musu suna Lallashinta Har karfe sha biyu tana kuka ga kanta dake mata ciwo Dak'yal Aysha ta Rungumeta ta dinga Lallashinta tana shafa bayanta a haka har wahalallen bacci ya kwasheta a hankali Aysha ta kwantar da ita tukwana itama ta kwanta gefenta cike da tausayin y'ar uwar tata Dan tasan Abba baya magana biyu"...........✍🏿
*Karki fitarmun da Littafi mu Rikewa juna amana y'an uwa duk maiso ta biya ta karanta cikin kwanciyar hankali*
*_Miss Hajo ce_*🤙🏿
[6/19, 10:19] Hajo hajo: 🅿️..........*51&52*
.....Washegari haka Aira ta tashi sukuku kallo d'aya zaka mata ta baka tausayi lokaci guda harta rame Ba irin yanda ba ayi da ita ba akan taci abinci ba Amma takiya had d'ure Aysha tazo zata mata amma ta cije Haka.ta yini har dare bataci komai ba kwance ta yini a d'aki Tunanin Arman yaki barin kwalwarta Yama zaiji idan yaji wannan mummunan labarin shi yafi damunta saida dare Mamy taje har d'akin da take kamar zatayi kuka ta ce "ki tashi kici abinci Dan Allah Aira inba so kike hankalina ya k'ara tashi ba wani abun ya sameki ba " Aira da harta gaji da kukan tashi kanta dafe da kanta dake tsananin sarawa sai hawaye da take ta ce "Mamy bazan iya ci bane Dan Allah Mamy ku bawa Abba hakuri ya janye Auren nan Ji nake mutuwa zanyi kafin lokacin" Rungumeta Mamy tayi itama tana hawaye tayi Sauri ta Goge Dan son kwantar mata da hankali ta ce "ki kwantar da hankalinki yanzu haka Inna na wajenshi kuma Halima ma ta kirashi Suna Chan suna kokari zai janye insha Allahu Amma kici abinci kinji y'ar kirki" Goge hawayenta Aira tayi cikin muryar da ta gaji da kuka ta ce "Allah yasa ya yarda A baki Mamy ta dinga bata abinci har ta samu ta d'anci sai sannan hankalin Mamy ya Dan kwanta ita ta taimaka mata tayi salla har isha'i tukwana ta kwantar da ita Dan taji jikinta zafi ta ce " kiyi bacci Dan Allah "gyada mata kai Aira tayi ta ce " to Mamy "kallon aysha mamy tayi ta ce " ki shirya mijinki ya zo ku tafi" mamy bazan iya tafiya ba Aira na wannan halin please ku ce mashi ya bari sai gobe"a a a aysha ba za a yi haka ba shiryawa zakiyi ki tafi goben zaiki dawo tunda ba wani abu ake ba mijinki karya daukemu k'ananan mutane"Aysha ta Goge hawayen tausayin y'ar uwar tata ta tashi ta sanya hijab d'inta zuwa tayi ta Rungume AIRA ta ce "karkisa damuwa a ranki plz sis kiyi bacci gobe zandawo kinji kuyimun Alk'awarin" gyada mata kai Aira tayi daga kwance hawaye nabin gefen idonta Badan ta so ba Aysha ta koma gidanta cike da tunanin tausayin y'ar uwar tata Mamy ko tashi tayi ta nufi dakinta itama cike da tausayin y'artata Aira ko har 1 bacci bai d'auketa ba wajen karfe ukku kallon gefenta tayi taga amma ce kwance tana bacci tashi tayi tare da shiga toilet ta d'auro alwala Tana fitowa ta sanya hijab nan ta tada salloli ba abunda take sai rokon Allah akan ya lalata wannan Abun karo na farko kenan da Aira ta shiga tashin hankalin da har ta tashi cikin dare take k'iyamul laili inba da azumiba idan sunje tuhajji Har asuba tana salla Sai Bayan asuba bacci ya kwasheta akan sallaya bama tasani ba da safe Mamy ta shigo Dan ta bata break fast ta ganta kwance kasa kan sallaya da hijab amma data fito daga toilet ta tambaya tace ya na ganta kasa kwance "wlh mamy kwana tayi tana salla inad'anjinta cikin bacci to bayan tayi asuba ne bacci ya kwasheta shiyasa ban tashetaba Dan ta d'an samu baccin girgiza kai Mamy tayi ta ce "Allah mai iko kenan Wai Aira ce da Sallar dare Allah Amsa maki abunda kika roka Mamy ta fad'a tana barin d'akin ta na fita part din Abba ta nufa zaune ta sameshi yana Tasbihi saida ta jira ya gama ta gaisheshi " Bayan ya amsa "hawaye ta fara ta ce " Dan Allah Abbansu kayi hakuri ka janye maganar Auren nan wlh yarinyar nan zata shiga wani hali ka tausaya mata Dan Allah"bazaki gane bane Rahama nafiki Sanin abunda nake Idan na zubawa yarinyar nan ido wlh abun Kunya zata d'auko mana ke uwace kiyi mata addu'a kawai Allahsa hakan shi yafi alkhairi bawai ki rik'a zuga ta ba "Cikin muryar kuka Mamy ta ce " to tunda zarginsu kake Abbansu ka Bari su Auri juna mana Ita dashi tunda kana zargin sunsan juna a waje kaga Inma sunyi Auren Chan su karata asiri ya rufu amma Dan Allah karka Aura mata tsohon nan ka barta ta Auri Wanda takeso "tsaki Abba yaja ya ce " ki tashi kiban waje indai Akan maganar wannance Har abada indai Nina haifeta bazan tab'a Aura mata Mujahid ba akan idonki wace irin Maganace ubanshi bai fad'a mana ba Har cewa yayi indai na isa da y'ata na rabasu sannan y'a mace ke abun Kunya ba d'a namiji ba irin maganganu masu ciwo da baifadamunba akanta Shine kike zancen wai na barsu su Auri juna karki Kara zomun da wannan shashanci Aure ne an Riga ansanya gwarama ku fara shiri"tashi Mamy tayi cikin fad'a ta ce "To Dan kaga muna Binka lakwa lakwa karka fasa d'in mu zuba mu gani niko Allah banga Auran nan ba Allah kaimu lokacin Saimuga ta yanda za a daura Wannan ai zalinci ne kake kai ba a isa a baka hakuri ka hakura ba Allah baza ayi Auren ba Indai Nina haifi Aira aiba y'arka bace kai d'aya bare kayi ikonta kai d'aya nima y'ata ce kuma ni nasha wahalar Haihuwarta harda za adinga mun iko akanta" ta k'arasa fad'a cikin kuka" tsaki Abba yaja ya ce "Karki samun ciwon kai da safen nan mai k'aramar kwalwa kawai har yanzu kwalwar yara gareki wlh shirmen da zakiyi ko Haidar d'anki na biyu baya yiba Dan ta farkonma irin kanki tayo shiyasa take bani matsala duk maganar da tazo bakinki ki dinga fad'amun Kamar