NI DA YAYA ARMAN Lokacin da So Ya Zama Laifi by Hajara L Sadeq

Author :  Hajara L Sadeq Category :  Romance

Chapter   13 / 54

36K to 39K   out of 160.7K words

maganarshi ba ta gyada kai ta ta ce "Amma ya akai Inna ta bari ka tafi dani hadafa yimana saimun dawo Murmushi yayi ya ce.........✍🏿

*littafin Ni da yaya Arman na kud'ine it's #200 via Katin MTN to 07026166536 v t u #300 PC #300*

_*Miss Hajo ce*_🤙🏿
[6/12, 17:01] Hajo hajo: 🅿️.......*37&38*



.....Ya ce "Keda kikasan Inna saurin sayuwa gareta sayayya na had'o mata na rikita ta nace ta bani ke zaki rakani wani bikin best friend Dina kuma kowa da budurwarshi yake zuwa sannan na had'ata da 100k nace ko minti ashirin bazamuyi ba zamudawo "karkiga yanda ta rude hada cewa bari taje ta tadoman ke" Dariya sosai Aira tayi ta ce "Kai yaya amma wlh kasan logar Inna" shafa sajenshi yayi ya ce nid'in na wasa ne "cikin shagwaba tace" to baka tunanin Abba Da kowa zai gani me yasa kakira yan gidan television"Murmushin gefen baki Arman yayi ya ce "Saboda su shaida kalar son da nake maki" Uhm kawai ta ce "ta d'ora kanta a saman kafad'arshi Ta ce " My yaya wai tun yaushe ka fara sona haka"Tun ranar da kikazo duniya "ya fad'a yana murza lallausan hannunta sannan ya ce " kece ma zan tambaya yaushe kika fara sona haka kodan Kinga d'an beautiful ko"Hararar wasa tayi mashi ta ce "Kaine dai kaga y'ar beauty ka rud'e" Dariya Arman yayi ya ce "to oya nima fad'amun yaushe kika fara sona" Cikin k'asa da murya ta ce "Tun sanda ina zanin goyo" Dariya sosai maganarta Tabawa Arman saida ya dara Suna isowa Gidan Aunty Halima Har cikin get d'in gidan Mai gadi ya shiga dasu Shima had'adden gidane flat da ya tsaru da shuke shuke Saidai baida wani girma sosai Dan Parking space d’in bazai wuce ya d'auki mota Ukku ba Aira ta fara fita tukwana ARMAN Shima ya fito Hafsat ce ta rugo da gudu daga ciki ta Rungume AIRA ta ce "oyoyoy my Fav sis sannunku da zuwa Gaskiya i'm glad to see you” " Itama Rungumeta Aira tayi ta ce "Nima nayi farincikin ganinki sister Tukwana suka shige palour Arman ma yabiyosu Bayan sun zauna Hafsa ta ce " bari na kira Mama ta na ciki ta fad'a tare da shiga Tare suka fito Hafsat da Mama da harara Mama ta tare su da ita Arman ko murmushi yayi tare da cewa "Sannu da fitowa big Mom uwata ta kaina" Harara Mama ta aika mashi ta ce "marar mutunci nizakayiwa dad'in baki kai yanzu abunda kayi ko ince kukayi ganinku kun kyauta" Haba Mama ki bari mu gaisa mana sauran fad'a saiya biyo baya "Arman ya fad'a " Aira ko kasa tayi da kanta "Mama ta ce " baza a gaisa ba d'in wlh karkaja nayi maka shegen Duka a gidannan "Dariya Arman yayi tare da tashi yaje fridge ta d'auko ruwa ya ce " tunda ba ayi mana tayi ba bari mu d'auka da Kanmu ya fad'a tare da d'auko cup ya tsiyaya ya sha sannan ya k'ara tsiyayawa Ya mik'awa Aira ya ce "My cutie amshi kisha nasan kinajin kishi" Aira da duk kunya ta isheta ta lura Arman kwata kwata baisan meye kunya ba k'asa tayi da kanta Mama ta ce "Marar kunya kawai " Aira ta d'ago gabanta na faduwa ta ce "Ina kwana Mama "Lafiya qalau Mamana ke yanzu abunda kukayi kun kyauta kenan kuje ku jawa kanku bakin duniya bakin mutane ma aka barku dashi ya isheku dole saita hakane zaku bayyanawa duniya kuna son junanku Dan tsabar shak'iyanci" Aira tuni idonta ya ciko da k'walla cikin kuka ta ce "Mama kuyi hakuri bazamu sake ba" Haba Mama Kinga kin sanyamun ita Kuka Dan Allah abar fad'annnan haka shikenan "Arman ya fad'a yana mik'awa Aira Handchiep Girgiza kai kawai Mama tayi ta ce " Allah kyauta kai daman ai nasan ba kunya gareka ba Sannan ta kalli Hafsa ta ce "jeki hado musu breakfast" Aira da Arman sukayi rigen cewa "mun karya kafin mutaho" Hafsat ce taja Aira ta ce "Taho muje ciki sis Arman har suka wuce yana kallonta cikin so da k'auna " Mama ce ta sauke ajiyar zuciya Bayan su Aira sun wuce ta kalli Arman ta ce "Wai me ya kaika hada abun nan jiya maimakon kazo ka sameni ka fad'amun komai mubi komai a hankali har mu samu Iyayenku su Amince Amma kaje ka rikita Abu karkaga irin fad'an da Babanta ya dingayi dazu da na kirashi " Mama a tunanina hakan da mukayi shi zaisa su gane kalar son da mukeyiwa junanmu har su hakura su bari mu mallaki juna "girgiza kai Kawai Mama tayi ta ce " Allah ya kyauta Gaskiya zance nafi kowa jin dad'in wannan al'amarin Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya ida nufi"murmushi ARMAN yayi cikin jin dad'i yace "Ameen Mama yanzu kikayi magana wlh ina son Aira sosai Mama bazanso abunda zai raba mu ba Dan Allah kiyi mana kokari ki shawo mana kansu" ya fad'a kamar mai shirin yin kuka"Insha Allahu zanyi iya bakin kokarina "Daganan suka cigaba da hirar duniya sai wajen Azahar Arman yayi musu bankwana ya wuce Abuja.

Aira ko suna Chan suna shan hira da Hafsa tana nuna mata hotunansu da vedio wadanda ta gani a social media sosai Aira tayi mamakin yanda abunsu ya bazu duniya cikin k'ank'anin lokaci.
Mamy ce zaune gefen kujerar Abba ta na hawaye ta ce " Abban Aira Dan Allah ka taimakamun a nemo Inda Aira take harfa Azahar yanzu kayi hakuri mu nemeta karta b'ata"cike da b'acin rai Abba ya hayayyak'o mata ya ce "Ke ki tashi kije ki nemeta da yake ni na aiketa na rantse da Allah kika k'ara zuwamun da maganar nemanta ranki zaiyi mugun b'aci ki barni da abunda ke damuna Dan tsabar rainin hankali harma nemanta kike yarinya ce ita kuma ina nan ina sauraran zuwanta Saidai ki haifi wata y'ar badai ita ba" Kuka Mamy ta fashe dashi ta ce "Wlh ko ta dawo bazaka kashemun y'a ba duk ba kai kaja ba da baka raba suba da duk haka ta faru ina dalili tunda suna son junansu ku barsu mana Su auri juna kawai in banda ana son a samun y'a cikin wani hali nidai wlh na gaji kawai a nemu mafita" Abba ji yake kamar ya d'auke Mamy da Mari tsabar bacin rai da kyal ya iya control d'inshi ya tashi ya bar mata d'akin tare da barin gidan Gaba d'aya mamy ko durk'ushewa tayi ta na kuka mai tab'a zuciyar mai sauraro.
Da misalin k'arfe Tara na dare Aira suna dinning suna dinner ita da Hafsat da Mama sai faruq Wanda Aira tsakular abincin kawai take hankalinta duk yana wurin Mamy "Mama ce ta lura da haka ta daddabata ta ce " Mamana Yadai ko bakyajin dad'i"girgiza kai Aira tayi ta ce "a a Mama " to menene"Mamy ta fad'a ta na hawaye "to shine kuma saikinyi kuka uwar y'an shagwaba Bari mu gama na kira maki ita " cikin murna Aira hada Dariya ta ce "thanks Mama" suna gama dinner Mama ta kira Mamy ringing Biyu ta d'auka Daga d'ayan b'angaren mamy tayi sallama Mama ta amsa Tare da cewa "Yadai Naji muryarki wani iri maman Aira" ba dole ba Halima tun jiya fa Aira bata dawo gida ba Gashi Abbansu yaki saurarena "Ajiyar zuciya Mama ta sauke ta ce " Aira fa ta na gidana Ni nasa ya kawomun ita saboda nasan halin yaya a lokacin nan zai iya illatata"Ajiyar zuciya Mamy ta sauke Wanda har saida Mama taji cikin waya ta ce "Alhamdulilla Halima kin taimakemu wlh kuwa da ta dawo din da illatatadin zaiyi gwara da take nan din daman tashin hankali na ba asan Inda take ba " Ai nasan hakan zata faru shiyasa idan komai ya lafa zanzo muyi zama Dan Gaskiya yaran nan nason junansu inba wani hali akeso ajefa rayuwarsu ba"Mamy ta ce "Wlh maman Hafsa nima tuni na hango hakan amma Abbansu yaki ganewa kamar ma Kara zugashi ake ni da sunbi ta tau kawai su barsu muga yanda Allah zaiyi" Hakane Allah dai ya shige mana gaba Mama ta fad'a sannan ta ce "ga Airar ku gaisa A tsorace Aira ta amshi wayar ta ce " Hello Mamy ina yini"Lafiya qalau ya kaduna d'in"Alhmdllh Mamy "Sosai Aira tayi mamakin Mamy yanda ta nuna mata kamar ma komai bai faru ba " To sai anjima "Mamy na fad'ar hakan ta kashe wayar Ajiyar zuciya Aira ta sauke Dan kashi Hamsin cikin d'ari na tashin hankalin da take ciki ya ragu yanzu kuma saura na Abba batasan Me zata tarar ba.

Sosai Zaman Aira gidan Mama Halima yayi mata dadi Hankalinta ya d'an fara kwanciya kayan hafsat take sanyawa Arman ko ya maida kd kamar gida kusan kullum sai yazo sosai yake son fita da ita amma mama halima ta kasa ta tsare tace bazasuyi mata shiriritar yawon da suke a kano ba dan haka kome zasuyi suyi a gidanta yau ma Arman yazo Dagashi sai ita a palour suna zaune kujerar 2siter kamar zasu shige juna Aira sai shagwaba take mai akan ya tafi da ita Abuja shikuma yana biyeta sai Lallashinta yake " da Hira tayi dadi Aira ta ta d'ora kanta kan kafad'arshi tana shak'ar daddad'an k'amshin turarenshi har wani lumshe ido take shiko baiyi kokarin dagata ba dukda duk lokacin da jikinsu suka had'u Dana juna yana cutuwa "Mama Halima ce ta shigo d'akin Salati tayi ta ce " me zan gani haka Mamana"Cike da rud'u Aira ta tashi ita tama manta da d'akin Mama Halima suke "Hararta tayi ta ce " Wuce ciki"cikin sauri Aira ta wuce hada tuntub'e Mama ya zaki korata kuma saboda ita fa nazo ki bari mu gama hira mana "Arman ya fad'a" kai daman nayi maka Ittik'afin kanka marar kunya Kunzo kun wani manne kamar chumgum "Dan murmushi Arman yayi tare da tashi ya ce " Ai munmafi gum Mama chumgum ai yana fita cikin Sauk'i "Pillown kujera Mama Halima ta d'auko tare da wulla mai tace wuce kaban wuri marar kunya so kake ka fitsarar mun da y'a" Dariya yayi ya kauce tare da Yin hanyar fita ya ce "y'artakice dai take son ta fitsarar dani" ya fad'a yana barin d'akin "Ja'iri ai zaka dawo ka sameni Mama Halima ta fad'a tare da wucewa Dakin da Aira take ita da Hafsat kwance ta tarar dasu Suna kallo a wayar Hafsa cikin fad'a Mama ta ce " Ke yanzu Mamana Dan gidanku haka ake hira kije ki lik'e jikin namiji Ko kunya gaku fitsararru'cikin shagwaba Aira ta ce "Mama yaya Arman ne fa " Arman din dan gidanku to wlh daga yau ki kama kanki kar in karaga kina shigemai jiki da da yanzu ba d'aya bane ki shiga hankalinki "To Mama yi hakuri Bazan sakeba" Yawwa y'ar kirki Mama ta fad'a tare da cewa ku fito ku d'ora mana abincin Dinner kunsan dai inada zakad'a zakad'an y'an mata kamarku bana shiga kitchen ba Dariya Aira da Hafsa sukayi Aira ta ce "Gaskiya ne big Mama muje ta fad'a tana kama hannun Hafsa suka sauko kan gadon.
Aira saida tayi sati biyu a Kaduna Tukwana Mama.Halima ta fara tunanin yanda zata kaita gida Mamy ta kira Bayan sun gaisa ta ce " ya ake ciki nan din Maman Aira Yaya ya huce kuwa"eh ko a a zance Dan Gaskiya bai sake maganar ta ba Kuma na fad'a masa tana wajenki baice komai ba "Ajiyar zuciya Mama Halima ta sauke ta ce " to kina ganin ba matsala gobe mu taho ko mu bari dai ya k'ara hucewa"Duk yanda kikace maman Hafsa Magana na wajenki "to bari muga gobe zamu shigo insha Allahu idan ya huce ni da sai ya bani ita ta zauna nan muga yanda hali zai bada" to Halima nagode sosai Allah dai ya bar Zumunci "ba komai ai yiwa Kaine ko na baki Airan ku gaisa" a a barta kawai sai anjima ngd "tukwana sukayi bankwana.
Washegari da safe Mama da su Aira sukayi shirin Tahowa kano Aira duk Inda hankalinta yayi dubu ya tashi sosai take fargabar haduwarta da Abba Wajen 10 suka fito Suna shirin shiga mota su tafi Airport motar Arman da danno dakatawa sukayi saida ya Iso kallonsu yayi ya ce " ina zuwa kuma Mama na ganku hada kaya"Kano zamu"Mama ta bashi amsa "Kano kuma Mama da kun bari ba yanzu ba" Yau mukayi niyyar zuwa ko zaka hanamu"Allah huci zuciyar big Mom Allah kiyaye amma nifa Gaskiya anshiga hakkina nan yafimun kusa ina ganin my cutie kullum ya fad'a yana tsare Aira da idanu sosai tayimai kyau cikin goduwar Riga Atamfa ta yafa gyale matching da kayan fuskar nan fayau sai hasken annuri "Itama Airan shi take kallo bako kyaftawa sosai yayi mata kyau cikin Shaddarshi da tasha aikin manyan mutane Fuskarnan tashi fayau ba ko Alamun damuwa a cikinta kafe juna sukayi da kallo bako k'iftawa Saida Arman yace karki cinyeni" Tukwana ta dawo daga duniyar tunanin da ta Lula "Hararar wasa ta aikamai cikin shagwaba ta ce " ba Kaine ka fara kallona ba "Murmushi yayi ya ce " To laifi ne Dan na kalli mata ta "Nima laifine Dan na kalli yaya na ta fad'a tana tsatsareshi da idanu irin ba wasan nan" Dariya yayi sosai ya ce "Keidai ki fad'i abunda ke ranki so kike kice laifine Dan na kalli mijina" ai tun kafin ki fad'a na shiga zuciyarki Naji abunda takeson furtawa"Uhm to ni ai bance ba Kaine kace haka"Kuma hakane ba Dan zuciyarki bazatayimun karyaba"Mama Halima ce ta ce "To marassa kunya a gaban nawa ma nafa lura kwata_kwata ku bakwamajin kunya ta ko " Murmushi Arman yayi ya ce "Wlhko Mama kamar kinsani " Bugu a baya Mama ta kaimashi ya kauce tace "ja iri da ka tsaya mana sannan ta kalli Aira ta ce " Saikishiga muje "Kallon Arman Aira tayi ta ce " yaya zamu wuce "Ai tare zamu tafi yaza ayi ku barni" Mama Halima ce ta ce "Wallahi baka isa ba Bazaka bimuba ka bari ma naje na samu na kashe gagarumar wutar da ka tada ba Inda zaka bimu ka k'ara tada mana wani bomb din" Dariya sosai Arman yayi ya ce "please Mama bansan cutie tayi nesa dani" tsaki Mama Halima taja ta ce "Saikayi kuma amma bazaka bimu ba Dan haka kama maza ka wuce Inda ka fito" Badan Arman ya soba yaki binsu ba ya koma Abuja su kuma suka kama hanyar kano Dan sunje Airport jirgin zai jima bai tashi ba hakan yasa kawai driver ya wuce da su kano.
K'arfe 12 da wani Abu tayi musu a Kano sosai Aira gabanta ya fad'i har suka isa gidansu addua take Dak'yal Mama Halima ta samu ta fito daga mota duk a tsorace take har suka isa Babban palourn gidan Mama da yaya Umar sai matarshi suka tarar a palour Ajiyar zuciya Aira ta sauke ganin basu tarar da Abba ba "Mama ce ta ce lale marhaban mutan kd sannunku da zuwa " Mama ta tarbesu Zaunawa sukayi aka gaggaisa Sannan ta kawo musu ruwa Aira duk ta rakube ta zama kamar wata bakuwa "Umar ne ya gaishe da Mama Sai kallon Hafsa yake khadija ko sai wani shashshan magani take a takaice ta gaida Mama Halima Aira ce ta ce " Yaya ina yini anzo lafiya "Lafiya qlau y'ar gidan Inna sannan ya kalli Hafsa ya ce " wai Mama Hafsa ce ta girma haka"Murmushi Mama tayi ta ce "Ai ka jima baka ganta ba shiyasa Mama Halima ta ce " Ai ganinka Babana wuya yake "Murmushi yayi ya ce " Mama yanayin Aiki ne sai a hankali yanzu ma Hutu ne muka Dan samu zuwanmu kenan"Allah ya taimaka yayi jagora "ameen " Hafsa ce ta ce "Ina yini ya Umar" Cike da Fara a ya ce "lafiya qlau Hafsa ya makarantar har Angama ko" Eh "to Allah ya taimaka " Ameen ta fada Sosai ta tsarugu da Kallon da ya Umar ke mata "Khady ko sai cika take tana batsewa tana Aika mata da harara Mamy ce ta shigo " zaunawa tayi suka gaisa da Mama Halima cikin mutuntawa Aira dai kanta a k'asa "dak'yal ta d'ago ta ce " Mamy ina yini"Lafiya qalau mutanen kd ke Kd dinma tafi amsarki harda k'iba"Murmushi Aira tayi Mama Halima ta ce "Nima haka nagani Ai shiyasa nazo mutafi da kayanta ni da kun bani ita ai sai Aure ya raba" Dariya Mamy tayi ta ce "nidai indai nice na baki halak malak sai ki hada kiyi twins Hankalina ma ni da yafi kwanciya" Dariya Mama Halima tayi ta ce "Kamar gaske " Sosai suka shiga hira cikin raha "Amma ce ta shigo Da gudu ta fad'a ta ta Rungume AIRA ta ce " oyoyoy sis Gaskiya nayi kewarki da yawa wlh gidan Duka baya yimun dadi da bakyanan"nima nayi kewarki sis daga ina kike"Amma bata kai ga Amsa mata ba Abba ya shigo sosai Aira ta tsure cikinta ya d'uri ruwa Cikin b'acin rai Abba ya nuna Aira da yatsa ya ce "........✍🏿

*Ni da yaya Arman na kud'ine ki biya #200 kachal to 07026166536 ki karanta cikin kwanciyar hankali karki fitarmun da Littafi kud'in karantawa kika biya ba na mallaka ba bazanyi Allah ya isa ba amma ki sani akwai hak'k'i*


*_Miss Hajo ce*_
[6/13, 08:16] Hajo hajo: 🅿️.......*39&40*





......Ya ce "me ya kawo wannan gida na me take a gidana maza maza ki gaggauta barin gidannan kafin na sauya maki kamanni" Aira cikin tashin hankali ta tashi ta Ruga ta boye Bayan Mamy ta makalkaleta tare da sakin kuka ta ce "Dan Allah Abba kayi hakuri Bazan sake ba " Mama Halima ce ta ce "Kayi hakuri Dan Allah yaya bazata sake ba ka zauna muyi magana ta fahimta" Ba wata maganar fahimta Halima daman na lura yanzu dake kike d'aurewa yaran nan gindi me ya maidota gidana ta koma gidanki bani ba ita na hakura da ita ko ita kad'aice y'ar da na Haifa na hakura da ita ku gaggauta

13 / 54