INTISAAR Ramuwar Kaddara By Khaleesat haidar

Author :  Khaleesat Haidar Category :  Romance

Chapter   22 / 41

63K to 66K   out of 122.8K words

dawowa kuma sae ki dawo mun
daure da tawul," Inteesar ta galla mata
harara tace "ku ji min tsohuwar nn me xan
maki idan ban tafi gurin mijina ba to," inna
ta bude baki, Inteesar tayi dariya ta dauki
xani ta cire towel din jikinta ta daura, inna
tace "ae ba dan jiya dare yyi ba da baxa ku
tashi ku tarar dani gidan nn ba, inteesar
bata tanka ta ba ta dauki Hijab ta sa ta tada
slh, ko da ta idar ta gaida inna maimakon ta
amsa sae ca tayi "ni tashi ki hada min kayan
karyawa nayi na bar gidan nn tun kan na
fara ganin abinda yafi karfina," inteesar xata
yi magana Aliyu ya bude kofa ya shigo dakin
yana kallon inna, daga tsayen yace "an tashi
lfya," inna ta galla masa harara tace "ban
tashi ba, hka kke gaida uwarka," Aliyu yace
"har gida xan xo na rama abinda kika min
daxu wllh," Inteesar ta mike ta fita daga
dakin ya bi ta da kallo ya tabe baki yana
kallon inna yace "yar nn bakuyi mata trainin
me kyau ba a gida, bata san ta tashi ta gaida
mutum ba da safe," inna tace "ae gun
uwarka ta gaji hka, wae ni Aliyu ya naji
shiru har ynxu ban ganta da ciki ba," Aliyu
yace "ita ce tace bata son Haihuwa,shine ma
yasa xan auro warce ke son Haihuwan"
inna tayo waje da ido tace "kmr yaya," xae yi
magana wayar inna ta cika daki da ruri ta
daga da sauri tare da cewa "salama
alekum," ya mike ya fice daga dakin, kitchen
ya sameta tana hada ma inna break, ya
karaso kusa da ita yana kallonta yace "ke
gidanku ba a koya maki idan kin tashi da
safe kiyi gaisuwa ba ko," ta tabe baki bata
ko kallesa ba bare ta basa amsa, kmr xae yi
magana sae kuma ya fasa ya matsa dab da
ita yace "gobe xa a xo ayi ma amaryata
danki, kuma tace dakin da kike ciki take so
don hka nake so kije ki fara fiffito da
kayayyakin dakin ki xaba wani dakin ki
xuba su ciki," tayi yar dariya bata ce komai
ba, yace "hope dats clear," tayi masa wani
mugun kallo ta juya xata fita daga kitchen
din ya kamo hannunta.

Inna na xaune a daki tana kallo bayan ta ci
tayi kat, inteesar kuwa na wanke Bathroom
Aliyu ya shigo yana kallon inna yace "inna xo
mu je indan xaga dake gari mana tunda ina
gida yau," inna na kallonsa da mamaki don
daxun nn suka gama fada tace "kai da
gske? Amma fa ba tukin nan taka ta
ganganci xaka yi dani ba fa," yace "wllh a
nutse xan tuka ki," ta mike da sauri tana
gyara daurin dankwalinta tace "to ita
Inteesar ita kadae xa mu bari gida, wae ma
to wa xae je ya kwaso min kayana ne," yace
"ehh xan kira Zainab ta kwaso maki, inna
tace "Inteesar ke baxa ki je bane, Aliyu yace
"ki dae gaya mata me xata girka maki kafin
mu dawo," inna tace "to kiyi min tuwan
semo da miyar kubewa," inteesar ta fito
tana kallonsu, ko kallonta inna bata yi ba
tace "sae mun dawo," ta fice Aliyu ya juya ya
galla mata harara snn ya fice shima, mai
gadi na bude masu gate tace "yauwa Aliyu
wnn ba mutumin arxiki bne jiya kokuwa ya
dinga yi dani ka koresa," yace "to inna,"
suna ta tafiya suna hira inna sae kyalkyale
dariya take duk da Aliyu bae ga abun dariya
ba don hiran ma ba ganewa yake ba, tafiyar
kusan minti talatin suka yi snn yyi parkin
yana kallon inna yace "to fito in siya maki
nama," inna ta fito da sauri tace "yauwa dan
albarka" tana kare ma inda suke kallo
bakinta a wangale, can sae fara'ar dake
fuskarta ya bace tace "nn ae anguwansu
farida ne Aliyu," yace "yauwa ashe kin gane,


*************************⬇**********************
************* Top Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.thn.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > tophausanovels@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Top Hausa Novels

Twitter: Top Hausa Novels

Telegram: Top Hausa Novels

Watsapp Group: https://chat.whatsapp.com/BRN8VEA8BczD61ZGjoOUod

********************** ⬇ **************************
*************** Top Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************


kuma nasan xaki iya gane gida daga nn
kina shan kwana xa ki ga gate, in kin koma
sae kice da Haisam ya siya maki naman don
ban fito da kudi ba" yana kai wa nn ya shige
motarsa yyi gaba inna ta fasa ihu tana salati,
mutanen dake gun suka taho da sauri suna
tambayar lfya. Inteesar na kwance da
daddare ya shigo gidan ita dae tasan bbu
maganar dawowan inna gidan, tana ji ya
bude dakinsa ya shiga, ta mike xaune ta
rafka tagumi tana naxarin abinda yace mata
daxu da safe ita har lkcn ta kasa gaskata
wae Aliyu aure xae yi nn da kwana hudu,
tunanin hkn yasa hawaye ya cika idonta,
tana nn xaune har kusan karfe daya ganin
bacci ya kaurace mata yasa ta mike a
sanyaye ta shiga bathroom ta dauro alwala
ta fito ta fara sllhn dare. Da safe tana gaban
madubi tana gyara fuskarta ya shigo dakin,
1st tym in history Aliyu ya shigo mata daki
da sallama ta amsa ba tare da ta kallesa ba
yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace
"kina jina, ki kama kanki safeenah xa su xo
gidan nn anjima don nasan baki da kunya,
infact bance ki fita ba ma," tace "akan me
baxan fita ba? Wllh bbu abinda xae hanani
fita," yace "shknn, ni kuma xan ce mata duk
abinda kika yi mata tayi min maganinki" ya
juya ya fice daga dakin bayan kmr minti
goma ya dawo yana kallonta yace "kinga
dakina yyi kama da dakin kaya, c'mon kin
wuce kin dauke min kayanki da kika ajiye
min a ciki ko sae na bata maki rae," xata ce
wani kaya sae ta tuna kayan baccinta dake
dakinsa ta mike fuskarta daure ta fita tayi
hanyar dakin ya bita a baya tana shiga
dakinsa ya jawo kofan yasa key, ta juya da
sauri tana kallon kofar ta shiga bugawa
tana cewa "meye hka," yace "hka xaki tsaya
har sae na dawo," ya rufe nata dakin ma da
key snn ya fice ya bar gidan, kuka ta fashe
da ta durkushe tana kare ma dakin kallo,
sae a snn ta lura da kayan tea da cakes din
da ya ajiye mata kan fridge sae plantain
chips, karfe sha biyu taji ana shigowa gidan
da motoci ta mike da sauri don bayan ta
gama cin kukanta ta gaji kwanciya tayi, ta
karasa jikin window taga manyan motoci
shake da kaya har kusan guda uku, wasu
lafiyayyun motoci suka shigo gidan, manyan
mata kusan su goma suka fito suna
daddaga hanci, sae ga wata motar ma ta
shigo safeena da kawayenta suka fito daga
cikin motar tana gwada masu ta inda xa su
bi su shiga gidan, tuni aka fara sassauke
lafiyayyun funitures din da aka shigo da,
Inteesar ta sake labulan a sanyaye ta koma
kan gado tayi kwanciyarta tare da lumshe
idonta da taji na neman kawo kwalla, duk
suka cika gidan da hayaniya wasu na sakin
magana, ana ta shigo da kaya. Ko minti sha
biyar ba ayi da shigowarsu ba Anty Nafeesa
da Zainab suka shigo gidan, suna shiga falo
duk aka juya ana kallonsu, batare da Anty
Nafeesa ta kallesu ba tace Sannunku fa,
Zainab kuwa dama ko kallonsu bata yi ba,
Safeena dake kwance kan kujera da
kawayenta suna ta hira da shewa ta bi su
da wani irin kallon raini hka ma iyayen nata,
cikin daga murya Anty Nafeesa tace "to ina
uwar gida sarautan mata kuma ran gida
take ne," Zainab tace "ina xata iya da wnn
hayaniyar Anty, kila tana can cikin daki,"
.
Safeenah da 'yan uwanta suka bi su da kallo
har suka haura sama Anty Nafeesah na
cewa "gskya kam ina xata iya da wnn
hayaniyar," wayar Zainab yyi ring ta duba ta
ga ya Aliyu, tace "ashe dae ya Aliyu na da
nmbrna," ta daga yace "ki fito waje ki
karbar maku makulli," tace "na me," yace
"ban sani ba snn ya katse kiran" ta kalli Anty
Nafeesa dake buga kofar inteesar tana
kiranta tace "wae yaya naje na karba makulli
a waje," Anty Nafeesa tace "na me, ko tare
suka fita da Inteesar din ne," Zainab tace
"kila, ina xuwa na karbo keyn," ta fice da
sauri, yana cikin mota yana jiranta ta karasa
ya mika mata keyn dakinsa da na Inteesar,
tace "to ina inteesar din," yace "in kun bude
xa ku gani," ya ja motarsa yyi gaba, ta tabe
baki ta koma cikin gidan, dakin Inteesar
suka fara budewa bbu kowa ciki, snn suka
bude nasa, tana xaune ta hade kai da
gwiwa, suka karaso cikin dakin Anty
Nafeesah tace "amma Aliyu dan rainin wayo
ne kulle ki yyi a daki don ya isa," Zainab ta
dago kanta tana kallonta, kuka take, Anty
Nafeesa ta galla mata harara tace "ban san
shashanci kukan lfya" ita dae bata ce komai
ba ta gaida Anty Nafeesa, Zainab tace "meye
na kuka Inteesar" Anty Nafeesah tace maxa
tashi kije ki gyara fuskarki kiyi kwalliya kar
na bata maki rae ke dae baki gajiya da wnn
shegen kukan naki komai kuka komai kuka,
ita dai bata ce komai ba suka bar dakin
Aliyu Zainab ta kulle suka koma nata dakin,
sae da ta sake wanka snn Anty Nafeesa ta
sa ta gaba ta tsantsara kwalliyanta snn ta
fito mata da wata shaddarta dogon riga
maroon colour ta saka Nafeesa tayi mata
dauri mai kyau, Zainab tace"waw yan matan
yayanmu kin ga yanda kika xama kmr wata
balarabiya," inteesar ta galla mata hara, ba
karamin kyau tayi ba duk da ta rame ssae,
Anty Nafeesa tace "to akwae abinci ne a
gidan? Don ni yunwa nake ji," Inteesar tace
"sae da na girka maku," Anty Nafeesah tace
"to da dae yafi," ta ce "toAnty suna falo
kuma," Anty nafeesa tace "to ina ruwanki da
su ae don su ganki da kyau nake son kije
kiyi mana girkin," ta mike ta dauko mata
takalmikalan shaddar ta ajiye mata snn ta
feshe ta da turare tace "maxa sa ki tafi
indomie kawae xaki girka mana," Zainab
tayi dariya tana kallon Anty Nafeesa,
Inteesar kam murmushi tayi ta sa takalmin
gabanta na faduwa ta fita xuwa kitchen,
duk suna xaune falon har da safeena kusan
su goma banda wa inda ke ta jere a daki,
Inteesar bata ko kalle inda suke ba a nutse
cikin takunta mai jan hankali ta nufi kitchen
ta bude kofar kitchen din tana yatsine fuska
don duk sun dauki cups sun sha lemo da
shi, ta dan tabe baki ta shiga kitchen din,
duk kawayen safeena suka juya suna kallon
safeena da yanayinta ya sauya lkci daya
xuwa bacin rai tana kallon kofar kitchen din,
inteesar ta kunna gas ta daura ruwa snn ta
fito falon ta shiga kwala ma Zainab kira
cikin wani irin tsiga, da sauri Zainab ta
sauko tana cewa "na'am yan matan
yayanmu wnn kira hka," inteesar ta galla
mata harara da wasa tace "ban fa son
iskanci indomie nawa kike ga xae isheku,"
Zainab tace " wani irin tonan asiri ne wnn,
ko ma dae duka nace ae gidan yayana ne nn
bbu uban da ya isa ya hana," Inteesar tayi
dariya ssae tace "ikon Allah to shigo ki girka
maku kinsan dae ni ba daga nn ba ban gaji
rowa ba kuma duk yanda nace hka xa ayi a
gidan nn bare kice kina tsoran wataran ki
xo...," a fusace safeena ta mike tana nuna
Inteesar da yatsa tace "ke ki kama kanki kar
ki kaini bango don dukan tsiya xan maki
wllh wllh kuma sae dae mijikinki ya gode
min idan ya dawo," Zainab ta yo waje da ido
tace "wa xa a duka ni Zainb" Inteesar tayi
dariya tace"tambayan min ita don ni kaina
ban gane inda ta dosa ba," Safeena ta ciro
wayarta da sauri ta shiga kiran Aliyu, "Aliyu
Aliyu ka ja ma ballagaxar da ka ajiye a gida
kunni wllh ta fita harkata idan ba hka
bakafin na bar gidan nn yau sae na yi mata
kaca kaca, kuma wnn shegiyar kanwartaka
ita ma kaja mata kunne," Zainab tace "wllh
ni ba shegiya bace sae dae kece shegiya,"
Inteesar ta ja ta suka shiga kitchen suna
dariya, safeena tayi shiru tana sauraran
abinda Aliyu ke ce mata tana bubbuga kafa,
sun gama dafa indomien knn xasu wuce
samaAliyu ya shigo gidan, ba karamin
tsorata inteesar tayi ba tayi hanyar stairs ba
tare da ta kallesa ba, Zainab tace "ke kar ki
bada kanki mana ki tsaya ae Anty nafeesa
na nn," Aliyu na kallonta yace "ke xo nn," ta
galla masa harara tace "nayi maka me,"
karasowa kusa da ita yyi ta dake xuciyarta
na bugawa, duk yan falon suka xuba masu
na mujiya, ita kanta Zainab karfin hali tayi ta
tsaya, Safeena kosae taunar cingam take
tana jujjuya ido xuciyarta fal murna ita nn
kawayenta suka yanda ta isa da Aliyu, yana
isa kusa da inteesar ya kama hannunta ta
fixge tace "da'alla malam kyaleni," ya tsaya
kallonta da mamaki bae ce komai ba,ya juya
yana kallon Zainab yace "je dauko mata
mayafinta ko ki bata naki," Zanab ta cire
mayafinta ta mika ma Inteesar taki karba,
shi ya karba snn ya sureta kmr wata bby
suka fita daga gida
.
Inteesar ta tsorata ssae murya can kasa tace
"don Allah kayi hakuri ka saukeni wllh ita ce
ta fara,"Safeena kam binsu tayi da kallo da
mugun mamaki don tsabar mamaki kasa
rufe bakinta dake bude tayi, ita nn jira take
taga ya rufe ta da duka, Zainab kuwa dariya
tayi tace "kai irin wnn soyayya hka, ko me
Inteesar ke ma yayana hka oho," ta haura
sama tana ci gaba da dariya, bayan mota ya
jefata snn ya xaga ya shiga motar ya ja ta,
ita ko kallonsa kawae take gabanta na
faduwa ko ina xae kai ta, sun yitafiya ssae
snn taga yyi horn aka bude gate ya shiga yyi
parkin, ya bude mata kofa yace "fito kar na
mareki," ta fito tana kare ma wajen kalloduk
da tasan inda ya kawota don ta taba xuwa,
lallai ma Aliyu asibiti ya kawota, yyi gaba
tana biye da shi a baya kmr xata yi kuka,
nurses duksuka kama kansu ganinsa, suka
bi inteesar da kallo suna masu sannu da
xuwa, bae ko kallesuba sae ita ce ta
gaishesu ganin yanda suke kallonta, can last
flour office dinsa yake kusa dana aminin
dad dinsa don shine mai asibitin wato

dad din Sadeeq, ya bude office dinsa ya
shiga, ganin taki shigowa yasa ya fixgota, ta
shiga karema office din nasa kallo, ba
karamin haduwa yyi ba kmr ba office ba ita
fa bata taba gskata Aliyuna aiki ba duk da
tasan da sassafe yake barin gida ya dawo
late, ya shiga dakin da ke cikin office din ita
dae tana nn tsaye har ya fito bayan kmr
minti goma sanye da kayan surgery, green
colour yana kkrin sa hand gloves alamar
theatre xae shiga, ya galla mata harara yace
"kada Allah yasa ki xauna kuma idan lkcn
sllh yyi kar kiyi," snn ya fice, tayi tsaki kmr
xata yi kuka ta xauna kan kujera tana kare
ma office din kallo, ko minti goma ba ayi ba
da fitarsa wata nurse ta shigo rike da abinci
a rufe da lemo ta ajiye mata tace "sannu
madam," snn ta fita. Hka inteesar ta yi ta
xama kamar gantalalliya a office kmr tayi
kuka, abincin da aka kawo mata ma kin ci
tayi, ta gaji da xama ta kwanta kan gadon
da ake duba pregnant women tayi
kwanciyarta sae bacci, ko da ta farka taga
biyar ya kusa ita da ta kwanta tun kusan
daya da rabi, bata damu ba don dama bata
sllh, ta bude abinci daxu ta yatsine fuska ta
rufe, aka bude kofa wasu nurse biyu suka
shigo da jarirae har biyu suka yi ma inteesar
sannu, snn suka daura su kan gadon yara
dake office din daya ta kunna wani wuta
mai haske dae dae fuskarsu snn suka fita,
inteesar ta wara ido tana kallon yaran
kyawawa dasu, ta karasa kusa dasu da
mamaki tana kallonsu tace "yan biyu," a
hankali dayan ya shiga kuka yana tsotsan
hannunsa dayan ma ya karbe taji kmr ta
daukesu don tana bala'in son yara, ta rasa
yanda xata yi dukta rude ganinsu tayi can
tayi nn, aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo
ta juya da sauri tace "ya Aliyu yan biyu ne?"
ya cire abun bakinsa yace "ehh" ba tare da
tasani ba tace "waw a ina kukasamo su" ya
karaso kusa da gadon yana kallonsu yace
"daxun aka cirosu daga cikin mamansu,
bata farfado ba har ynxu ma" inteesar ta
juya da sauri tana kallonsa kmr xata yi kuka
tace "theatre aka mata," xae yi magana daya
yaron ya tsala ihu tace "wayyo ya Aliyu in
daukeshi," ya harareta yace "basu da
lafiyasuma," tayi shiru tana kallonsu kmr
xata yi kuka.Ya dauki dayan a hankali ya
mika mata yana kallonta.
.
A hankali Inteesar ta sa hannu ta karbi bbyn
da yake mika mata tana murmushi, tace "ya
Aliyu ni ina son twins ssae" yana kallonta
yace "kina sonki haifi twins knn," da sauri
tana kallonsa tace "eh mana ina so," ganin
irin kallon da yake mata yana murmushi
yasa taji kunya ta kauda kanta da sauri, wae
Aliyu take ma wnn maganar? Ita bata ma
sani ba, ya matso dab da ita ya tsaya har
tana iya jiyo numfashinsa a bayanta ya rike
kugunta yace "wnn waist din naki xae iya
daukar twins?," ta bar wajen da sauri nn da
nn ta tsorata xae yi magana ta riga sa da
sauri tace "Yaya yunwa fa suke ji ko," bae ce
komai ba sae kallonta da yake, ta daga bbyn
xata yi kiss dinsa ya dakatar da ita da sauri,
snn ya karbe shi ya kwantar gefen dan
uwansa, tace "yaya baxa a basu abinci ba,"
yace "sae xuwa karfe sha biyu na dare," ta
wara ido tace "sbda me yunwa fa suke ji,"
yace "eh xa ayi ta basu ruwa" kmr xata yi
kuka tace "to waye xae dinga basu kace
mamarsu bata farfado ba," ya daka mata
tsawa "ke da'alla kar ki dame ni" yyi tsaki ya
shiga daki, ta bisa da kallo snn ta tabe baki
ta koma kujera ta xauna, wata nurse ta
shigo rike da mug a rufe tana kallon
Inteesar tace "doctor fa? Ya shigo?" a dari
dari take tambayar, Inteesar ta gyada mata
kai, nurse din ta ci gaba da tsayuwa har ya
fito sanye da kananan kaya, yana kallonta
yace "wathappen" tace "coffee sir," ya daka
mata tsawa "to kaina xaki daura ko me," ta
karasa kusa da table ta ajiye ta fita sum
sum. Ya bude abincin da aka kawo ma
inteesar yana kallonta yace "meyasa baki ci
ba," tayi kamr bata ji sa ba, ya rufe ya koma
kan table dinsa ya xauna kan kujera ya bude
coffeen ya shiga sha, hka yaran suka dinga
kuka Inteesar taji kmr ita ma tayi kukan, ta
kasa jure kukan nasu tace "yaya kuka fa
suke," ya kalleta yace "cnt yhu see they re
under medication," bata sake cewa komai
ba bayan kmr minti sha biyar ya kira nurses
su kashe wutan su fita da su, inteesar ta bi
su da kallo kmr xata bi su suna fita ta bata
rae ta juya tana kallon Aliyu taga kallonta
yake yana murmushi, ta dauke kanta da
sauri, karfe takwas da rabi suka bar asibitin
bayan ya kaita ta kara ganin yan biyun da
mamarsu, ya biya ta eatry ya siya masu
abinci snn suka kama hanyar gida, gidan ba
kowa duk sun watse sae kamshin turaren
wuta ke tashi, ta haura sama ta bar sa nn
falo shima ya bi ta a baya, spare key Aliyu ya
dauko ya bata na dakinta don su Anty
Nafeesa sun tafi da shi, dakin safeena ma a
kulle yake ta tabe baki, ta bude kofar
dakinta, ba shiri ta koma baya da sauri tana
kallon dakin

22 / 41