domin kuwa harta fara wari kasan cewar ba'a yi wannan allurar ba. Haka dai a ka kaita mutuware, wanda suma da kyar suka yarda suka 'kar'beta akan wai basu kawota da wuriba harta fara wari.
Kaman yanda kawunsu ya ce musu duk kwana 'daya dubu 'daya to tabbas hakane. Anan fa hankalin Daniel da solo ya tashi, sukace badamuwa zasu biya.
Bayan sun koma gidane, a ranar Daniel ya ce zai tafi gurin aikinsu domin a wannan lokacin har sun fara zuwa zana jarabawar neman aiki. Ya ce "zanje bayan kwana goma zai dawo sannan kuma zai dawo da kud'in da zasu 'kar'bo mamar tasu. Batare da sunce komaiba suka masa fatan dawowa lfy. Kafin ya fitane titi ta ce "yaya kafin mama ta mutu ta bamu sa'ko mu sanar mk? Ya ce "Ina jinku? AI kuwa nan suka kwashe komai suka sanar masa irin wasihar da ta basu. Nan shima ya 'kara musu nashi fa'dan akan addininnasu domin kuwa duk cikinsu yafi su kishin addinin nasu.
Yau kwanan Daniel koma sha hud'u da tafiya, amma bakajin ko labarinsa, cikin damuwa da fargaba titi ta kalli solo ta ce "Solo pls yaushe yaya zai dawo? Jin hk yasa kukansa 'kwacewa yana rarrshinta. Wasa-wasa saida Daniel yayi kwana ashirin da 'daya bai dawoba.
Ganin hk yasa solo sayarda d'aya gonar yaje ya biya kud'in mutuwaren sannan yazo gida da mamar tasu.anan fa kamar dama jiran beriyan sukeyi, kasancewar dama 'kwayan 'karamine yasa duk wani abu da a keyi a 'kwayan sai kowa yasani. Da 'kyar yayi sa'a ya yanka musu kaji suma guda uku sai kuma kayan shaye-shaye. Aikuwa nan aka fara zage-zage da 'korafe-'korafe. Haka dai ya toshe kunnuwansa daga jin kowani irin zagi daga cikin la'umman garin.
Kasan cewar an ɗan sayi gonar da daraja yasa tun kafin yayi komai saida ya ware kuɗin akwatin da ake siya kafin ya ɗan ware wanda za'ayi sauran hididdimun. Cikin yardar Allah akayi beriyar mamarsu batare da ɗan uwansaba. Kamar yanda aladarsu take wajan bikin anayin kwana uku anayi, wasu huɗu wasu biyar kai wasuma har sati guda.
Bayan kwana shida da yin beriyar ne solo ya shiga aikin dyarsu sosai shida titi, kasan cewar dama itama ta iya komai na aikin gona, hk suka tone doyar nan sannan ya ce cikin gari zai kaita ya siyar. Haka ya kasance basu da komai a cikin garinnan sai gidansu sai kuma doyar soloda ya gama shiryawa akan zai tafi da ita gari.
Misalin ƙarfe tara na dare suna zaune shida titi suna hirar idan solo ya siyar da wannan doye meye zasuyi da kuɗin. Ita dai titi ta ce kawai tindade yanzu basuda gona ga kuma shagon basuma babu kwai su tafi cikin gari da kuɗin sai yayan nata ya fara wani sana'ar itama ta fara. Solo yace "to a ina zamu zauna? Ta ce "Sai mu siyar da gidannan idan munje sai mukama haya. Solo ya ce "idan kuma Yaya ya dawo ya zauna a ina? Titi tayi shiru tana kallon solo.
Ya ce "kawai ni zan dinga shiga gari ina yin wata sana'ar kekuma kizauna agida kafin yaya ya dawo. Hk kuwa suka yanke shawarin shine zai dinga shiga gari yana yin kasuwanci. Hk suka cigaba da rayuwar shida ƙanwarsa, yayinda dangin mamansu kowa yayi watsi dasu, shikuwa Daniyel bai sake leƙowa garinba. Haka suka kasance har shekara biyu da daɗi ba daɗi.
Haka zaije cikin garin Bokon yayi buga-bugan sa ya dawo ita kuma titi idan tasamu wani aikin koda na nimane sai tayi. Haka dai har jarinsu yayi ƙasa kasan cewar aciki suke komai da komai. Bayan shekara ɗaya. Cikin sauri haɗi da murna titi ke kallon yayan nata da yace mata ”Yasamu jiran shago a cikin gari, saboda haka yanzu itama zata daina noma. Tin daga ranar titi ta daina yin aiki saide itace wanke musu kaya da kuma kula da gida, kokuma idan zasuyi girgi itace zata dafa. Sunyi wata ɗaya da yin haka sai Daniel ya dawo ɗauke da kakin soja ajikinsa, cikin mmk kowa dake garin ke binsa da kallo domin kowa'a karo na farko kenan da wani ɗan cikin garin yayi karatu har ya samu aiki kenan kuma aikin ma na soja. Kai zokuga murna gurin titi da dangin ubansu harda solo. Abunda ya ƙara baiwa mutane mamaki ma shine har star ɗaya ajikin rigar nasa, kasan cewar yayi dogon karatu sosai.
Haka dai al'ummar gari suka dinga zuwa kallon sa kai kace wani sabon halittane. Kwanan sa uku a garin yace da su solo da titi zasu bar wannnan ƙwauyan zuwa cikin bokon. Nan fa dangin ubansa sukace su basu yardaba, titi da solo kuwa sai murna sukeyi. Haka sai ya musu alƙawarin zai dinga zuwa yana dubasu idan ya samu hutu daga aikin nasa.
Eh tabbas sun samu sauyin rayuwa sosai, domin kuwa yanzu sun daina shan wahala irinta baya. Yayinda titi da solo suka fara zuwa school kasan cewar Daniyel ɗin yanada burin yaga ƴan uwan nasa sunyi karatu. Ɓangare ɗaya kuma solo yana zuwa gurin uban gidansa wanda yake zauna masa a shago, domin kuwa shima mutumin acikin Bokon yake. Lokacin da zasu fara zuwa school ya sanar dashi cewar yanzu sai ƙarfe huɗu zai dinga zuwa, shima mutumin ya ce babu damuwa kuma yana tayashi murnar.
Tabbas suna jin daɗin zama da juna tsakanin solo da mai gidansa domin kuwa solo yanada riƙon alƙawari, mutumin ya ɗauke shi da daraja dukda kuwa Addininsu ba ɗaya ba. Ɓan garan Daniyel kuwa bayan ya dawo dasu titi gidan da aka mallaka masane ya zuba musu kayan abinci sosai sannan ya biya musu kuɗin karatun su. Saida ya gama cinye hutun da aka bashi kafin akace zai koma cikin barikin sojoji da zama. Hakanne yasa ya ce dasu titi su zasu zauna ana shi kuma zai koma can. Haka kuwa akayi shine ya koma cikin barikin sojoji dake cikin bokon, sukuma suka zauna awannan gidan.
Alhaji Salisu gamji shine uban gidan solo wanda ko titi bata taɓa sanin saba, shikansa solo ɗin tsoran kar yayan nasa yasan cewar uban gidan nasa musulmine ya keyi. Domin kuwa bai mance gargaɗin daya musuba akan karsu sake wata alaƙa ta shiga tsakaninsu da wani wanda ba addininsu ba. Abinda Daniyel baisaniba shine solo ya daɗe da Alhaji Salisu, kuma shi babu ruwansa da cewar wai shi ba musulmi bane tundade yana riƙe masa amana.
Shekarar su ɗaya da dawowa wanda tayi dai-dai da ranar da Alhaji Salisu zai aurarr da ƴarsa. Hakanne yasa ya ce da solo yanason yazo gidansa gurin ɗaurin auran. Solo ya ce ya yarda zaizo. Wannan lokacin kuma Daniyel ya sake samun ƙarin girma agurin aiki, hakanne yasa ya dawo gidan nasu da zama, sannan ya tara ƙanyan nasa ya kallesu cikin ido ya ce "Ranar lahadi mai zuwa zaiyi aure sannan matar tasa agidannan zata zauna, kuma yana musu ƙargaɗi akan matarsa, sannan dukkansu ya basu wayoyi sannan ya ƙara tuna musu cewar karsuyi abota kokuma alaƙaga da kowa. Hakanne yayi dai-dai da auran ƴar gidan Alhaji Salisu. Ashe ɗaya daga cikin manya sojojinne ya baiwa Daniyel auran ƴarsa domin ganin juriyarsa dakuna hango kamar a kwai nasara a gaba ta rayuwar Daniyel ɗin. Daniyel Mutum ne mai tsananin kula da addininsa domin kuwa ya yarda da addinin nasa, dukda hk solo ya fisu ɗaukar addinin da serus. Ita kuma titi bata wani damu da addininbama domin kuwa cocima sai ranar Lahadi kawai take zuwa. Zaune suke su uku suna hira irinta yanda zasu ƙaru acikin family ɗin nasu...cikin sauri titi ta ce "yaya wai yaya sunan matar takane? Daniyel ya ce "Compot ne sunanta....sannan bata san raini ko kaɗai kuma bana son naji wani abu daga gareki domin nasan shi solo babu ruwansa...ya ci gaba da cewar yauwa solo inason zamu haɗu da wannan ogan naka saboda inaso kaima ka mayar da shagonka ka zauna da ƙafafunka? Cikin sauri solo ya ɗago kai ya kalli yayan nasa. Ga abun murna amma yazo da abun kuka. Ya ce "no ai kawai ka bani kuɗin sai na haɗa?. Daniyel ya ce "no inaso muyi shawa dashine. Babu yanda solo ya iya, dole ya gaiyato Alhaji Salisu izuwa gidansu kuma batare da ya sanar masa da komaiba.
Assalamu alaikum! Alhaji Salisu ya faɗa lokacin da shiga palon gidan su solo. Dukda kuwa yasan suɗin ba musulmai bane. Da sauri titi ta ɗago domin jin abunda baƙon ya ce. Da sauri solo ya rintse ido yana addu'a irin tasu ta coci. Kasan cewar yanzu solo da titi sun zama cikakkun ƴan gari saboda yanzu suna iya jin turanci har su mayar. Tin kafin Alhaji Salisu ya zauna Daniyel ya miƙe tsaye cikin mamaki da ɓacin rai ya nunashi da hannu ya ce "Idan ka sake ka zauna agidannan Walhi sai kayi nadama...✍️
*
*PAGE 25*
......Daniyel cikin ɓacin rai yaci gaba da cewa "Nace kafitamin daga gida yanzunnan kafin ranka ya ɓaci!! yana faɗa yana nuna masa hanyar waja. Shi kuwa Alhaji Salisu sai murmushi yakeyi yana ƙoƙarin zama acikin kujerun da ke cikin palorn. Da ƙarfi Daniyel ya sake daka masa wata tsawa wacce tasa dukkansu saida suka tsorata. "I see get aut in my home? Da sauri Alhaji Salisu ya meƙw tsaye cikin tsoro da jin irin tsawar da ya masa ya ce "Da ka tsaya munyi mgn cikinnutsuwa da ka faɗa min laifin me nai maka hk? "I don't like to see duk wani Muslim in my from I don't like you. Sai yanzu ya fahimci abunda yasa yake ta wannan ihun. A ƙalla Alhaji Salisu zai girmi Daniyel sosai amma ya kwantar da muryarsa ganin ya ɗauki lamarin da zafi, tabbas Alhaji Salisu yasa da yawa wasu arnan basa ƙaunar musulmai amma baiyi tunanin harda dangin solo ba domin ganin shi solo ɗin babu ruwansa.
Ya ce "Ko zan iya sanin abinda musulmai suka ai katamaka haka da yasa dukkansu kake ɗaukar su ɗaya? Cikin ɓacin rai Daniyel ya kamo solo ya jefashi jikin ahj Salisu ya ce "Walhi idan baibar gidannan ba zan sa a halakashi. Yana faɗa ya bargurin cikin cewa kafin ya fito yabar gidannan. Titi kuwa itama wani kallo tabi Alhaji Salisu dashi irin kallon nan na tsana kafin tabar gurin izuwa ɗakinta. Da sauri solo ya kamu hannun Alhaji Salisu suka bar palon yayinda Alhaji Salisu ke binsa da kallon mamaki.
Bayan sunje gidan Alhaji Salisu ɗinne ya ce "Mai gida dan Allah kayi haƙuri da abunda yayana yamaka, Walhi haka yake baya son musulmai ko kaɗan, Ni kaina hk nake, amma zamana da kai yasa na gane ashe duk abunda ake faɗa mann akan ku ba haka bane.domin gaskiya kuna bani mmmk musamman ma kai, saboda hk kayi haƙuri pls? Alhaji Salisu ya ce "Ai yanzu kaine abun tausayi, domin kuwa Allah ne kaɗai yasan idan ka koma gida me zai maka domin naga ransa ya ɓaci sosai, sannan kuma ɓangaran addini nima kaina kana bani mmk domin kuwa ni baka taɓa faɗamin komai game da yayanka ba. Solo ya ce "Eh kayi haƙuri a kwai abunda yasa ban faɗa maka ba.
Nan dai alhaji salisu yaci gaba da baiwa daniyel ha ƙuri a kan yayi haƙuri da ɗan uwansa. Kuma ya sanar masa da cewar duk abunda yace yayi to karya masa musu.saida solo ya tashi zai tafi kafin Alhaji Salisu ya ce "Shin ko zan iya sanin dalilin kiran da ɗan uwanka yaymin? Solo bai ɓoye masa komaiba ya sanar dashi akan wai zai bashi jarine shine zai shawarci mai gidana. Alhaji Salisu ya ce "karka damu dama nima na gama shawara da mai ɗakina a kan zan maka free domin kuwa ka cancanta, saboda hk yanzu kaje gidan duk abunda yafaru sai ka sanar min?. Cikin ruɗewa da mmk solo ke kallon uban gidan nasa jin abun dayace. Alhaji salisu ya ce "Addinimu wato Addinan musulunci yana da sauƙi haɗi da tsafta, sannan yanada dokoki haka kuma komai munayinsane cikin hukuncin Allah. Addininmu bai banbance mana kowaba wajan keytatawa, sannan bai sa muna kallon kowa a matsayin mai kuskureba, domin kuwa Allah ne mai shiryawa, mutuƙar mutum ya kyautata mk koda kuwa ba Addiniku ɗaya ba to kaima zaka iya kyautata masa, a koyarwar manzan Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ya ce koda mutum ya nufeka da sherri to kaikuma ka saka masa da alkairi, duk wani musulmin gaskiya to tabbas ya yarda da wannan. Solo yayi shiru yana jin wani annashuwa na shigarsa, idan ya tuno da kyutar da mai gidan nasa zaimasa, gakuma yanzu wani irin zance da yake masa wanda shi bai fahimci komai ba. Alhaji Salisu ya ce "Karka damu hankali zaka fahimci komai. Cikin bazata Alhaji Salisu yaji solo ya watso masa tambayar da baiyi zatoba.
"To ance wai ku musulmai idan mutum ya kashe wani wai shi ɗan aljannane shi yasa ku kashe mutane babu wahala a gurinku, sannan kuma ana faɗa mana cewar addinin musulunci kashe mutane shine aikinsu, sannan ana cemana wai ku ba Allah kuke bautawaba, wai wannan Muhammad (S a w) ɗin kuke bautawa, Ni kaina na yarda da hk amma zamana da kai sai abun yake bani mamaki domin naga halaiyarku ba hk takeba. Amma abunda ya bani mamaki shine bautar Muhammad (S a w) da kukeyi, ko yanzu naji da idan zakayi mgn shi kake cewa ba Allah ba , kuma naga Allah ne kaɗai abun bauta sai kuma wanda shine ya kamata ace kuna kalla wato jesus domin shine maganar Allah. Shin me yasa kuke bautar Muhammad? (S a w), bayan kuma yanzu haka baya raye, kuma shima mutumne kamar kowa, kuma idan an taɓa shi kuke ɗaukar fansa, me yasa tunda shi Allahnkune ba zai dinga kare kuba, kuma mai yasa..."Cikin sauri da mamaki haɗi da murmushi Alhaji Salisu ya katse shi sannan ya kalli solo jin irin fahimtar da wasu addinin sukewa addinin Musulunci.
Cikin muryarsa mai ɗauke da sanyin murya irin ta wanda yasaba da ambaton Allah ya ce "Duk wani musulmi da kasani aduniya to Allah yake bautawa, shima kansa Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama ɗin ma Allah ya ke bautawa, sannan shine ya koyar damu yanda za'a bautawa Allah ɗin. Sannan kuma shi abunda yasa kaka kamar muna bauta masa kuwa shine...shi wannan Muhammad ɗin da kake gani to duk duniya albarkacin sa mukeci harda shi Annabi Isa Alaihissalam ɗin wato jesus. Saboda Allah da kansa ya ce idan muka zo gareshi da soyayyar annabinsa to tabbas zai karɓemu hannu bibbiyu...
Duk wani musulmi da kasani to yana son Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama fiye da kansa, amma duk Allah muke bautawa Bama haɗa shi da kowa wajan bauta domin shiɗin shi kaɗaine, sallah da kaga munayi to Allah muje bautawa, azumi dakaga mukeyi shina ibadane. Solo ya sunkuyar da kansa izuwa ƙasa yana ɗagowa sai ga hawaye suna bin idonsa. Cikin zuciyar Alhaji Salisu ya ce "In sha Allah zuciyar ka irinta masu rabautane da yarda Allah sai Allah yasa ka gane gaskiya yau. Afili kuma ya ce "Solo lafiya kuwa? Cikin kuka ya ce "Walhi mai gida an ɓatar da zuciyoyinmu wajan saka mana ƙiyayar abinda bamuda masaniya akansa, tunda nake ban taɓa zama da wani musulmiba, amma an sakamin ƙiyayar su fiyeda yanda baka tunaniba, ko farkon haɗuwata da kai saida zuciyata ta haneni amma da yake alokacin ina buƙatar taimako sai kawai nace zan ƙwada zamada wanda ba ɗan addininmu ba nagani ko dagaske hk kuke.
Alhaji Salisu ya sauke ajiyar zuciya afili ya ce "Allah sarki, dama ai ba'a yankewa mutum hukunci sai ka zauna dashi kasan halinsa. Haka dai Alhaji Salisu ya ci gaba da nunawa solo cewar duk wannan abunda ake faɗa musu akan musulunci to duk ƙaryane, sannan ya ce masa musulmai basa kashe mutane haka kawai saide idan sunci mutuncin addinisu kokuma Allah da annabinsa, to idan hk ta faru to tabbas addinin musulunci ya tanadar da lada mai tarin yawa ga wanda suka kashe wannan mutumin koda kuwa shiɗin waye. Saida yaga jikin solo yayi sanyi sosai kafin ya barshi ya tafi. Bayan ya fitane allhji Salisu ya ɗaga hannu sama ya ce "ya Allah kasa wannan bawan naka yanada rabon musulumta acikin kwanannan, kuma kasa yayansa karya iya hanashi, shima yayan nasa idan yanada rabon musulumta kasa shi a cikin rahamar musulumci.
Koda solo yaje gida sai titi tahau shi da surutu da ihu a kan mai ya haɗashi da wannan mutumin. Baiko kulataba ya shiga ɗakinsa yana jin kansa na juyawa, kwanciya yayi yana kallon sama yana tunano abubuwan da mai gidansa ya faɗa masa akan addinisu. Tabbas ya yarda da wannan mutumin sannan shi kansa shedani ogansa baida damuwa baida abokin faɗa, yana cikin hk titi ta shigo ɗakin cikin sauri tana cewa "Solomon kamanta abinda Momy tace mana a kan yin alaƙa da wasu wanda ba addinimu ɗayabako? Cikin sauri solo ya miƙe zaune yana tunowa da nasihar mamarsu, hk titi ta cigaba da tuno masa da abubuwa da yawa. Da sauri solo ya ce "Pls titi is ok! Ya faɗa cikin ihu da yasa titi nutsuwa. Ya ce "ina yaya Daniyel? Cikin rawar muryar tace ya fita. Shima fita yayi yana cigaba da nazarin komai.
Yau ranar juma'a ranar da Alhaji Salisu yake aurar da ƴarsa, wanda kowa ke cewa tayi yarinya ganin a lokacin shekararta batafi sha huɗu zuwa sha biyarba, shi kuwa shi yasan dalilin aurar da ita ɗin. A ranar kuma bayan al'umma sun sheda aurarrne kuma solo yazo gurin mai gidan nasa da himmar shiga addinin Musulunci. Alhaji Salisu yayi mmk domin kuwa tun ranar da sukayi mgn bai ƙara ganin saba yau kwana biyar kenan. Cikin mmk yace "Solo kayi shawara da ɗan uwankane? "Idan mutum zai shiga sai yayi shawara da wanine dama? Alhaji Salisu ya ce "a'a ai ka mallaki hankalin kanka.
Babban malamin da ya ɗaura auran shene ya baiwa solo kalmar shahada kuma ya ƙarɓa. Ya ce "Ashi'hadu allailahaillallha wa'ashi'hadu anna buhammadur