tayi sosai, nan take yace da Abdalha zai fara mata al'lura kafin yaje asibiti yadawo zai ɗauko kayan ƙwaji, nan ya tafi yabar Abdalh zaune kusa da ita yana ƙura mata ido cikin tausayi.
*ZAINAB VOP*
Tinda aka zuba mata wani abu a fuska bata farkaba sai cikin dare. Ihu takeyi tana tambayar a ina take domin kuwa ɗakin yayi duhu. A haka ta kwana a cikin ɗakin babu wanda ya kulata. Washe gari ma sai misalin ƙarfe tara na safe kafin ta ga wasu samari guda huɗu, kowanensu ya rufe fuskarsa da baƙin ƙyelle. Tambayarsu ta farayi cikin kuka domin kuwa harga Allah ta tsorata. "Suwaye ku? Me naimuku Pls Dan Allah karku cutar dani pls? Babban cikinsune ya ce "Tambayarmu ma kikeyi cewar me kike mana ko? To kafin muci ubanki bari mu fara nuna miki dalilin kawoki nan da mukayi shegiya mai kamar ubbanta, masu ƙaryar addini masu son rarraba kawunan musilman gaskiya. Yana kaiwa nann ya zaro wayarsa daga aljihu ya kunna mata waƙarta da tayi mai sunan buɗaɗɗiyar wasiƙa. Babu wanda ya sake yin magana harsaida waƙar ta ƙare har ƙarshe, kafin ya sake dawowa da ita akaro na biyu. Waƙar ta farayi kenan ya kashe ya kalleta ya ce "Daga yau bazaki ƙara yin wata waƙa irin wannan ba, kin zagi malamammu kinci mutuncinsu hakanne yasa mukace sai mun hukuntaki domin kisan cewar malamai ba mutanan banza bane.
Sannan ya ce "Zamu kunna miki waƙar ki dinga fassarata domin kuwa wani guri a har-harɗe tayi maganar. Take Saiyada ta haɗiyi wani yahu maƙot, tayi dauriyar cewar..."Walhi bada kowa nakeba kuma ni nayi waƙarne domin Allah. Saide kawai wani guri da nayi gargaɗi akan wasu, kuma nasan sunji kuma su..."Wani mari taji mai sauƙar ungulu daga gefenta, wanda yasa jinta tsayawa na ɗan daƙiƙu kaɗan, bataji ƙarar wani marin da aka ƙara mataba sai dai taji zafinsa sannan ga kuma bakunansu dake motsi wanda ke nuni da cewar wannan karan dukkansune suke mgn amma batajin me ceke cewa.
Tana kallonsu sai nunata da hannu sukeyi alamar dai zasu iya ai kata mata komai a wannan lokacin. Tana haka taji an ƙara mata mari, kafin ta ɗago ta gane waye anyi boll da ita, sake kamo kanta a kayi aka ɗago buskarta ido cikin ido yake mata mgn alamar gargadi dai, yanayi yana nuna mata hannu wanda ko kaɗan batajii abun da ya ce ba. Tunani takeyi shin abun da tace ne ya ɓata musu rai haka da suke mata wannan dukan. Yana gamawa ya ƙara mata mari aɓarin da aka mata na farko.
Hakanne yasa taji wani abu shuuu ya huce ta kunnanta ta faɗi agurin ta fashe da kuka. Cikin mamaki taji yana cewa "tsabar raini ki kalli idonmu kice wai wani guri ne kikayi gargaɗi ga wasu! wato malaman mune wasu ko? sai kinsan kinyi da malamanmu mahaukaciya babu wanda zaisan ina kike har gaba da abada dan ubanki, dama nifa na tsaneki walhi ban samu damar ɓatar dake bane tun da sai yanzu, yana kaiwa nann ya barta agurin suka tafi. Haka Zainab taci gaba da zama a gurin har yammma kafin aka zomata da abinci ɗan kaɗan babu ruwa. Bayan nan bata sake ganin suba sai washe gari, wato dai kwananta biyu a gurin.
Yauma da safe sukazo kamar ranar farko, suka tarar da abincin da suka kawo mata ko kallonsa batayiba. Babban ya ce "Good Saiyada haka mukeso kar kici abinci kinji? Ya faɗa yana sakin dariya. Kallonsu takeyi cikin wata murya tace "Dan Allah ku barni na tafi gida me kukeso dani kusanar min idan kuɗine zan baku Walhi zan baku koda kuwa nawa kikeso....sannan dan Allah waye yasa ku kumin wannan zalunci? Duk tayi maganar ne babu ko haɗiyar yawu. Ya ce "Ubanki ne ya turomu! Ji kake tass tass tass har sau uku yaci gaba da cewa..."Ke yanzu har kin kai a ce wani ya turomu gurinki! Mune muka turo kannmu, kuma bari kiji ko uban ki wannan mai kama da aljanunnan baida kuɗin da zai bamu bareke ƴar maula. Yana kaiwa ya ƙara mata mari yayi boll da ita, suka fita suka bar mata ɗakin. Tayi kuka har ta godewa Allah kafin ta tsagaita da kukan ta shiga nazari akan Abdalh ne zaisa a mata wannan aikin tabbas shine.
Washe garima haka wanda yayi dai-dai da kwananta uku kenan a gidan. Yauma saida taci uban duka kafin suka jawota zuwa parlon gidan ɗaya daga ciki wanda ba shine oganba ya ce "Munaso kibar wannan aƙidar taku daga yau ki dawo tamu ta gaskiya wato sunna, kuma kiyi mn alƙawarin bazaki koma waccar taku ɗinba koda kin koma gida, kuma kin daina aikata duk wani bidi'a da ubanki ya koya miki?
Sai a lokacin ta ɗago ta kalleshi, kana ganinta kasan ta jigata, kwana uku kenan ko abinci bataciba ko maganarta bata fita, tana son tayi mgn amma ta kasa hasalima biyu-biyu take ganinsu, tana son sanar masa cewar koda irinsu ɗari za'a taro bazaisa ta bar kan aƙidarta ba saide su kasheta, amma ta kasa. Ya buɗe baki zaiyi magana ogan nasu ya ce "what!!! Ya faɗa yana kallon wayar hannunsa.
Hoton Shek Abdalh Kabir kabugane tare da Zainab da kuma wasu rubutu dake nuni da cewar shine ya saceta, da sauri ya miƙi yana nunawa abokan nasa. Nan take hankalin su ya tashi jin yanda al'umma suka ɗorawa Abdalh, ai basuma naga komaiba saida suka buɗe fexxbookk suka dinga ganin kace na ce ɗin al'umma kuka kowa Abdalh yake zargi. Hakanne yasa ogan nasu dayake yanada numbar Abdalha sai kawai ya kirashi da yamma ya sanar masa cewar tana gurinsu, kuma abunbda yasa suka sanar masa saboda sunga kowa shi age zarg, sukuma suna giemamashi sosai.
Nann Abdalha ya tambaye su dalilin da yasa suka saceta, suka sanar masa saboda cin mutuncin malaman su da takeyi ne shine yasa, Abdalha ya musu faɗa sosai haɗi da cewar idan kunaso mutum ya ƙirmamq aƙidarku to kuyi masa nuni da abubuwan kirki da aƙidar taku taƙunsa na tsoran Allah bawai ku biye masaba yanzu wannan abunda kukayi kuna tunanin idan wani yaji za'a yarda cewar ƴan sunnha ne sukayi hk? Kasan cewar sa mlm kuma mai iya sarrafa kalamai yayin wa'azi hakanne yasa jikinsu yayi sanyi suka sanar masa da gurin da suke, yace zaizo washe gari.
Duk abunda akeyi Zainab na jinsu kasan cewar an saka wayar a amsa kowa. Suna gamawa ogan ya kallesu ya ce "Mun aikata kuskure Amma kuma ai mun koya mata hankali, ɗayan da waazan da Abdalh din yamusu ya shige shi ya ce "Muɗauketa mu kaita har gida mu nemi yafiyar iyayenta, ɗayan ma yace "Kunga ubanta malami ne yayantama hk itama haka zasu yafe mana? Ogan ya ce "No mubari har Abdalh yazo sai mu bashi ita kunga shi yasan ya zaiyi da ita. Wanda yaɗan ji wa'azin ya ƙara cewa...."to idan mukayi haka kuma ai al'umma zasu yarda cewar shine ya saceta kenan ko?
Ogan yace "Munsan yanda zamuyi har komai yayi dai-dai. Wannnan shawarin bayan sun komar da ZAINAB cikin ɗakintane sukeyi. Wani ya ce :"To idan Abdalh yazo da police fa? Oga ya ce "Kumafa hakane. Take ya sake kiran Abdalh ya sanar dashi akan kar yazo da Police. Abdalha yace shi kaɗai zaizo. Hakanma wasu daga ciki sukace basu yardaba sai sun kwada shi, shi dalilin da yasa suka fara nuna masa wani gidan. Suna gamawa kowa ya shiga ɗakin Zainab wacce ko kwance idonta alumshe, suka siyo mata abinci harda nama amma ta kasa ci. Haka suka kwana a kanta suna kallonta idan ta suma su watsa mata ruwa, har washe gari da tayi dogon suma wanda dukkansu suka shiga cikin damawa sunyi tunanin ta mutu, har Abdalh yazo suna tsaye a palorn....✍️
*
*PAGE.* 2️⃣2️⃣ *BABU EDITING*
......... Yana zaune agurin yana kallonta har Dr Musu y dawo, kallonsa yayi cikin mamaki ya ce "Har kadawo? Dr ya a'msa da cewa yasa an kawo masa ne. Bayan ya dawo palon gidanne ya zauna Dr ya kalleshi ya ce "Wai shin Abdalha meke faruwa da batun yarinyar da akace kaine kasaceta? Tabbas Dr Musu ya gyrmi Abdalh nesa ba kusaba amma kasancewar shi Allah ya ɗaukakashi fiye da Dr Musu ɗin, sai suka zama tamkar abokai. Abdalha ya ɗago kai babu alamar fargaba ya ce "Itace wannan. Yafaɗa babu alamar wasa. Dr Musa ya zauna daƙwas cikin tsananin mamaki ya ce "kana nufin kace Zainab ce wannan? Abdalha bai bashi amsaba ya ce "Idan ta farka kasa madam ɗinka ta taimaka mata tayi wanka kuma abata abinci sanan ka kirani. Yana gama faɗa ya bar gidan batare da ya tsaya amsa tambayoyin da Dr kesan masaba. Dakallo Dr yabishi cikin sabon salon mamakin lamarin Abdalha. Afili ya ce "kenann shine ya saceta! Sanin ba mai bashi amsane yasa ya koma ɗakin da Zainab ɗin ke ciki da sauri har yana cin karo da kujera.
*HAJIYA BABBA POV*
Kallon palon nata takeyi cikin tsananin mamaki da abun al'ajabi, ta ce "ooo ni Allah me laɗifa takezon zamane? Ma'aikatan da ke sunkuye a cikin palorn da basu san da shigowar taɓa sunan nan a yanda ta shigo ta samesu. Da ƙarfi ta ƙwaɗawa laɗifa kira wanda yasa ma'aikatan ɗagowa daga sunkuyan da suke suka kalleta, nan take suka fara mata barka da dawowa. Dai-dai Lokacin laɗifa tana sauƙowa daga sama waya kare a kunnanta alamar waya takeyi.
HAJIYA BABBA ta nuna gurin da ƴan aiki suke ta ce "Lafiya kuwa naga waɗannan a haka? Cikin wani ihuu da tsan-tsar farin ciki tanufi uwar tata tana cewa "oyoyo Hajiya Allah inace ba yau zakidawo duk na zaci wasa kikemin. Kafin Hajiya Babba tayi magana ta ce da ƴan aikin subar palorn yanzu nan kafin ta ƙirga uku. Haka kuwa suka shiga rige-rigen bar gurin cikin sauri. Hajiya ta dawo da kallonta zuwaga laɗifa ta ce "Me ya faru zaki sakasu irin wannan aikin? Ta ce "Wallhi Hajiya ƴan aikin nann duk ƴan raininn wayone, wai saboda bana gida sai kowacce ta ci wanka suka zauna suna hirarr wai kowacce son yaya Salis sukeyi harda sha warin yanda zasu mallakeshi, cikin mamaki Hajiya ke kallon ƴan aikin ta ce "Wato kuna sha warin yanda zaku mallake min yaro ko? Kuna matsayin ƴan aiki amma kun iya tunanin cutar da ɗan gidako? To dan uwar kowacce daga cikin ku kuhaɗa kayanku duk na sallameku ƴan iska kawai. Hajiya ta ƙarasa maganar tana nuna musu hanyar waje. Yayinda kallo ɗaya zaka mata kagane tana cikin fushine.
Nan fa ƴan aikin kowacce ta shiga bada haƙuri a kan cewar Walhi rabi ce ta zigasu( Rabi itace babbar ƴar aikin gidan) Hajaya da Laɗifa basu tsaya bin ta kansuba suka koresu. Yayinda laɗifa ta kira Iro mai gadi cikin isa da cewar ita ɗin itace ta ce "Walhi Iro idan har kabari yarannan suka ƙara shigowa gidannan to kaima a bakin aikinka.tana faɗa ta bar gurin. Shikuwa iro sanin cewar itace matar gidan yasa ya rufe gidan yana cewar in Sha Allah bazasu shigoba.
Laɗifa na shiga palor ta tararr da Hajiya na waya, amma tana zuwa ta kashe. "Tashi mutafu? Hajiya ta faɗa tana nufar ƙofar waje.
Laɗifa ta ce "Haba Hajiya ko hutawa bakiyiba? "Laɗifa bakida hankali bakisan waye wannan mutumin ba, Walhi zai iya kashe mutum mutuƙar ba addininsu ɗayaba, barinma ace mudulmine.
Laɗifa ta zaro ido waje ta ce "Wai Hajiya meyasa baya son musilmai ne? Kuma naga Daddy mudulmine?
"Cikin ɓacin rai ta ce "Shiga mota muje, wannan labarin bai shafekiba. Haka suka shiga mota laɗifa dai sai tunanin wannan lamarin takeyi. Batayi auneba sai ganin su tayi agidan su Samuel. Ta ce "Hajiya kekuma zamuyi anann? Hajiya ta ce "Walhi yau za'ayi ta taƙare fito mutafi. Tafaɗa dai-dai tayi fakin a bakin get ɗin ta waje, domin tasan bazata iya shiga gidan ba.
*GIDAN SOJA*
Umar ne zaune tare da wasu daga cikin abokan Daniyel mutum biyu wanda suka haɗa komai tare a kan sune zasu kawo kuɗin. Umar yayi wata irin shigar da bakowane zai iya ganeshiba, domin kuwa ɗinkin babbar riga yasha ga hula sai sheƙi ya keyi. Ɗaya daga cikin abokan Daniyel ɗinne ya ce "Sorry sir Samuel ba aron kuɗi ya bamuba kuma mu bawai munsan me yayi da ƙuɗin bane, kawai munji labarin abunda ya farune yasa muka haɗa kuɗi domin a sakeshi. Tabbas da kana kusa da Umar da sai kaji yanda cikin sa ke murɗawa, domin kuwa Daddy ya zuba masa ido kamar shine mai yin maganar, kokuma mai son gano wani abu.
Daddy babi takan maiyin maganar ba ya nuna gurinda Umar yake ya ce "Wannan fa shima abokin Daniyel ne? Cikin sauri Umar ya ce "A'a Walhi ni bamma sanshiba kawai naga zasu shigone sukace na rakasu, da sauri sauran suka kalli juna domin kuwa ba haka suka shirya cewa ba, ba haka laɗifa da Umar ɗin suka shiryaba. Da sauri Daddy ya kira ɗaya daga cikin sojojin yace ayi waje da Umar.
Ai kuwa babu ɓata lokaci sukayi waje dashi suna takashi da wannan ɗan banzan taƙalmin nasu, shikuwa sai ihu yakeyi. Daddy ya dawo da kallonsa izuwa gurin sauran ya ce "kawo kuɗin? Da sauri suka miƙa masa kuɗin a lede kafin ya ce "Elixa ta fito da Sarah da Samuel. Da sauri ta miƙe tayi ɗakin da su Sarah keci ta buɗe ta ce "Kuzo palor Daddy na jiranku. Da sauri Samuel ya meƙe domin kuwa yasan da cewar yau za'a sakeshi. Sarah kuwa kana kallonta sai ka tausaya mata, domin kuwa tashi kuka ta rame sosai, haka itama ta miƙe tana bin uwar Tata da kallon mamaki ganin ko ta kanta batabiba.
Nan fa a ka hau kallon kalo tsakanin Samuel abokansa. Daddy ya buɗe baki zaiyi magana kenann sai ga ɗaya daga cikin sojin nasa ya shigo palorn ya sara masa sannan ya ce "Gawani wai sunansa AJ yazo yana nemanka? Ba Daddy ba mommy Samuel da Sarah suka kalli sojan da kyu momy ta ce "Wani Aj? Daddy ya miƙe tsaye ya ce "Shigo dashi. Take sojan ya juya domin cika umarni. Yayinda Samuel ya kalli sara itama ta kalleshi sai ya sakar mata murmushi. Daddy ya kalli abokan Samuel ya ce "Sutashi subar gidannan yanzu kafin yasa ayi fata-fata dasu, danma sunyi Sa'a su ɗin yan addininsu ne. Haka suka fita cikin gudu harda faɗuwa. Daddy ya dawo da kallonsa izuwa gurin Sameul ya ce "Tashi kaje kayi wanka, sannan ya miƙa masa kuɗin aleda wanda a ka kawo, ya ce ya ƙirgasu zuwa anjima ya kawo masa. Ya kalli Sarah cikin tsananin jin haushin ta ya ce "Sarah sorry for you! Kirasa wanda zaki ɗauki kuɗaɗena kubaiwa sai Musulmi! Ya faɗa yana kafeta da ido. Dai-dai Lokacin aka shigo da oga AJ riƙe a hannun sojan. ( *Tofa yau ga aj ga Comandar kuma ga Sarah ga Mommy. Shin me zai faru?)*
Kowa miƙewa yayi a palorn harda Samuel domin shima soyake yau saiga waye wannan AJ. Daddy ya kalli Sarah ya nuna Aj ya ce "Shine AJ? Sarah da hawaye suka wanke mata ido ta kalli AJ wanda kana ganin sa kasan yasha kuka. Suna haɗa ido gabansu ya faɗa a tare alokaci ɗaya. Dukda irin halin damuwar da AJ keciki bai hana ya ƙurawa Sarah idoba, yana aiyana kodai rashi lafiya tayi. Tana son tace eh shine AJ amma tana tsoro. Aj kuwa kallon Daddy da mommy yayi na lokaci ɗaya ya ɗauke ido, domin kuwa yasan yau ya shiga hannun manyan arna. SAMUEL kuwa kallon AJ yakeyi cikin mamaki ya ce "Ashema yarone ƙarami, domin kuwa Samuel ɗin ya girmeshi, tawani gurin kuma kallo ɗaya zaka masa kagane shiɗin yana cikin hutu, domin yanayinsa ga kuma farar fatarsa da tasha hutu na kwana biyar a Morocco, haka dai Samuel yaketa bin Aj da kallon tausayi.
Bata ankaraba sai ji tayi an zabga mata bari wanda yasa ta rikice ta kurma wani uban ihuu, tana faɗuwa agurin riƙe da kuncinta. Daddy ya ƙara mai-maita tambarsa a karo na biyu. Ai kuwa da sauri ta ce "Shine!. Daddy ya kalli AJ a karona babu adaddi, sai yasa hannu a aljihu ya jiro waya. Kira ɗaya ka ɗaga ya ce "Asaki wannan matan guda biyu sannan kuhaɗa musu da duka. Yana kashewa ya ƙara kiran wani shima ya ce "Ya saki wannan yaron, amma shi kar a haɗa da duka.
Yana gamawa ya kalli matarsa cikin ɗacin rai ya ce "Luk at her? Kalli yaronda yake saka yarinyata sata? Wannan yaron, yafaɗa yana yin kan Aj ya shaƙeshi har saida taga ya fara kururuwa kafin ya sakeshi, aikuwa nann take Sarah ta fashe da kuka domin kuwa ta tsorata sosai da shaƙunda aka masa. Daddy ya kamo wuyan rigar AJ ya ce "Meye haɗinka da ƴata? Kai ɗan gidan uban waye a garinnani. Sannan kana musulmi meye haɗinka yarinyata, AJ ya ce "Ina Innah ta da ƙanwata? Yayi maganar cikin sadaƙarwa. Jin haka yasa Daddy kwasheshi ya kalli sojan ya mai a lama da ido, aikuwa ya jashi yabar palorn dashi yayinda Sarah ta kamo ƙafafun Aj tana kuka. Ganin haka yasa Daddy yin bool da ita harsaida ta daki kujerarr palorn aikuwa take goshinta ya fashe amma bata tsaya bi ta kansa taƙara kamo ƙafafun Aj, Daddy ya riƙeta da ƙarfi harsaida aka fita dashi kafin ya juyo da ita ya kwaɗa mata maruka har guda huɗu, ya turata cikin ɗakin da suka fito itada Samuel, sannan ya sa ki ya rufeta. Samuel kuwa na ganin haka ya bar gurin cikin sauri, yana jin tausayi Aj domin yasan yau sai aj ya kwammaci baisan Sarah a rayuwasaba. Itama kanta saran sanin gurinda za'a kai aj ɗin ne yasa ta wannan kukan da riƙe ƙafafunsa. Momy kuwa tayi muwar tsayar agurin tsabar mamaki ganin Aj ɗin ɗan yaro, ita tayi tunani zata ganshi babba ne.
Ɓangaren su Innah da Nana kuwa, suna zaune kamar yanda tunda aka sake musu guri suke, Innah na kwance a kan cinyar Nana wanda kana kallon Innah sai gabanka yafaɗi, domin kuwa ta fita