Addininmu Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  S Reza Category :  Love

Chapter   14 / 37

39K to 42K   out of 109.2K words

Cikin muryar shaƙwaɓa ta ce "Dan Allah Hajiya ki dawo Walhi min yi kewarki Pls and pls dan Allha mun gaji, waima kuna inane? number ki bata shiga tun lokacin da kika tafi. Hajiya ta ce "Ina lafiya very soon zaku ganni..."Waima to Hajiya inane kikaje? Bakince Abuja zakujeba wai ma dan Allah yanzu kina ina? Cikin son kawar da zancen Hajiya ta ce "Ina Salis? Dama de yana zuwa aikin bai tsaya wasa ba? Cikin ƙwantar da hankali ta ce....

"Hajiya ai Salis ya zama ɗan soyayya, domin kuwa yasa rayuwarsa a cikin damuwar da tafi ƙarfinsa. Cikin sauri ta ce "Ban gane ba? Wacce irin matsala? Laɗifa ta ce "Yanzu haka yana hannun Daniyel... "zumbur Hajiya Babba ta miƙe tsaye haɗi da cewa "Wani Daniyel? Laɗifa da take jin ita ai hakan shine samuwar muradinta ta ce "Comandar Daniyel dai Daddy brother. Cikin wani tashin hankali Hajiya Babba ta ce "No no karna ƙara jin haka daga bakinki, Walhi ƙarya yakeyi bai isa a karo na biyu yaci mutuncina na barshiba. Cikin Muryar da tasa ita kanta laɗifar tsorata Hajiya Babba ta ce "Menene ya haɗasu? Shi Salis baisan waye Comanda Daniyel bane, kodai bashi da hankaline baisan me yakeyiba kodai ya manta da abunda Daddy yace muku ne? Laɗifa ta ce "Haba Hajiya wannan fa ba wani abun tashin hankali bane, ai shima Comandar Daniyel ɗin ai ya isa da mu...."Ya isa da uwarki nace ya isa da uwarki! Walhi laɗifa kikiyayeni banza mara mutunci ke idan har kinada hankalima har zaki ƙara kallon wannan ƙatin arnan da idon mutunci, mutumin da ya kasha ɗan uwansa saboda ya bar addinin ƙarya izuwa na Gaskiya, to Walhi ki shiga hankalinki, kuma ina hanyar dawowa gobe gobe in Sha Allah!, Wlhi wannan karan sai yasan dadayanzu ba ɗaya bane,.

Tana gama wayar ta kashi tana haɗa wani uban zufa, kallon wayar tata tayi ta danna kiran numbar Salis amma bata shiga. Kallon AJ tayi tace gobe zamu koma 9j. AJ tin lokacin da Hajiya Babba take yin wayar ya nutsu yana jin me take cewa. Lokacin da yaji sunan Comandar Daniyel sai yaji kamar yasan mai wannan sunan amma ya kasa tunawa, yana da niyar idan tagama shima yayi waya da Innah ko Nana kokuma Sarah wacce izuwa yanzu kullum sai yayi mafarkin ta. Amma yanda yaganta cikin ɓacin rai yasa ya fasa tambayarta. Cikin wani murya ta ce "Walhi wannan mutumin sai yagane cewar yanzu bada bane, da ba dan yamma tayiba da yau zamu tafi, bazan barshiba Walhi. Shidai sai kallonta ya keyi yana jin shi a wani yanayi, shin murna zaiyi kodai baƙin ciki, yanzu kenan idan sun koma sai sunyi wata biyar ɗin kafin yaci kuɗin! (Kai AJ sarkin son kuɗi) afili ya ce "Hajiya mubari mu kammala sati biyun mn kinga ai komai zaifi tafiya saiti ko? Cikin tsananin fushi da bai taɓa gani a fuskartaba ta ce "Kasan wacce masiface ta tasomin a gida!? Kasan me yake shirin faruwa? To gobe zamu tafi bazan iya zamaba. Tana faɗa ta shiga ɗaki ta ciro masa wayarsa ta bashi tace ga wayarka nann zaka iya kiran kowa. Ganin haka yasa AJ yin shuru yana buɗe wayar yasa sabon layin nasa na wannan ƙasar kafin ya shiga kiran numbar Nana.

*ABDALHA POV*

Kuka Mommy keyi taƙi ta tsaya ta saurareshi ganin haka yasa ya miƙe tsaye sauran ƙannan nasa suka bishi da kallon mamaki, yayinda Sadiya tayi ƙarfin halin cewar "Yaya me zaisa ka sace..."hannu ya ɗaga mata yana barin ɗakin cikin tsanani ɓacinrai, domin kuwa ransa yayi mugun ɓaci sosai, harma baisan meye abunyiba. Tunawa yayi da maganar daddy "Kaje ka fito musu da yarinya a duk inda ka ɓoyeta kuma mun gama magana da baban yarinyar da na zaɓa maka, indan kaga damar zuwa ruwanka idanma bakajeba to bazamu fasa daga ranar da muka yankeba...Na gaji da maganganu da mutane keyi a kanka, idan kai bai damunka toni yana damuna...Kin gaji ko to idan kin gaji daga ke har yaranki ai ga hanya nan kunada damar zuwa duk inda kukaga dama acikin ƙasarnan.

Ajiyar zuciya ya sauke yana shiga motarsa, tafiya ya keyi yana tunanin abunyi. Nan ma maganar Mommy ta dawo masa kansa. "Komai ɗaya Al'adar mu ɗaya, yarenmu ɗaya Allahnmu ɗaya Annabinmu ɗaya, ADDININMU ɗaya Amma kunɗauki tsana kun ɗora a kan junanku, Walhi kuji tsoran Allah domin wannan abun ba addini bane.

"Kallon agogon hannusa yayi sannan ya koma gidan sa domin shiryawa zuwa gurin su.

"Haba mlm yanzu dawanne kakeso muju da ɓatar ƴata kakeso kokuma da wannan masifar naka!? Shi wannan yaron da kuketa zargin shine ya saceta shin kunyi magana dashi ya ce shine ya saceta ne? Kudinga yiwa kanku a dalcifa, ni yanzu damuwata kawai yarinyata ta baiyana koma waye yaje shida Allah, kaikuma Walhi idan na ƙarajin kace wani abu a kan wannan yaron to Walhi sai na saɓa maka, banza mara zuciya. Mama ta faɗa tana nuna gurin da Isa yake staye yana ƙara zuga mahaifin nasu akan cewar Abdalh ne yasaceta shi kuwa mlm dama a sama yake ya tsani mutanann baya son duk abunda zai haɗa shi dasu, yanzuma jiyake da yanada dama da ya tashi duk wani ɗan aƙidar su Abdalh ɗin gaba ɗaya kowa ya huta. Mama ta ci gaba da cewa ...."Gashi tunda abunnan ya faru kuna gida babu wanda yafita domin nemanta amma kunzo kuna ta zancen banza a kan yaronda inada tabbacin baima san suwaye suka ɗauketaba. Ni dai Allah ya bayyana min yarinya.

Cikin tsananin faɗa da yasa muryarsa har rawa takeyi mlm ya ce "Walhi kin yi ƙarya ba a gidannan ba! Dama na lura dake bakison kuji ana faɗar laifin wannan yaron ko? To Walhi bari kiji kotu ce zata rabamu da wannan yaron mutuƙar yarinyata bata dawo gida yauba, ga alamu sun nuna cewar shine ya saceta, kuma har yanzu daga shi har uban nasa wanda shine mai ɗaure masa gindi babu wanda ya fito yayi magana. Shegu dangin tsiya munafukan Allah, Walhi sai sun tozarta idai irin wannan rayuwar satar yaran mutane itace halaiyarsu. Caraf isa ya cafe da cewar...

"Walhi haka sukeyi, kwanakin baya ma haka yaran da suka ɓata a hanyar school ance sune suka sacesu. Momy ta ce "wallhi kuji tsoran Allah domin wannan abun da kukeyi ba shine mafitaba, dama kishin neman ilimi kukeyi da Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama yayi alfahari daku, bawai zagin juna kuba, idan anyi magana kuce kune nagari, Walhi addinmu bai koyar damu cin mutuncin ɗan adam ba, ɗan adam ɗin ma wai musulmi. Kuma yanzu gashi ai kunju daɗi tinda gashi sai raba kawunan al'umma kukeyi, kullum tashin hankali kuma duk kune dalilin hakan, yara marasa sanin ciwon kansu sai zage-zage sukeyi a gari. Cikin ɓacin rai mlm ya ce "Walhi ki kiyayeni ki fita daga idona "Nidai a je a nemomin yarinyata shine kawai, ai ADDININMU baiyi hani da sace yaran mutanebako? Kuma Walhi sai munje kotu. Yana kaiwa nan ta rushe da kuka, isa da mlm suka fita suna cewa ai shine ya saceta kuma sai ya fito da ita.

*ABIN DUBAWA. TUNANI MAI KYU*

Waya ya ɗauka ya danna kira, sai da ta kusa tsinkewa aka ɗaga. Kafin ayi mgn ya ce "Gani nazo gurin wani gidane? Ya ce "Ok gani kubuɗe min get ɗin ina ƙofar gidan. Bayan ya shiga da motar tasa ya fito ya nufi wata ƙaramar hanya da ita ce kaɗai zata sadaka da cikin palorn gidan. Yana shiga ya ƙara kiran numbar taso suka ce ya dawo baya, ba'a wannan gidan sukeba dama sun kwadashi ne ko tafe yakeda ƴan sanda, cikin mamaki ya ce "Bayan munyi mgn daku maizaisa nayi ƙarya? Ta cikin wayar a kace ayi haƙuri shek ɗan gidan Shek kasan yanzu duniyar ce ba'a yarda da kowa. Ya nufi gurin da sukace masa, bayan yaje ɗaya gurin da suka cemasane ya shiga gidan domin ƙofar gidan a buɗe take, ya ce "Ina take? Da sauri sukace tana ciki! Ya ce "Damade baku taɓataba?, nann suka fara sun guyar da kai alamar aikin gama ya gama. Yana tura ɗakin da tage ya tsaya chak cikin mamaki haɗi da zaro ido waje.

Da sauri ya fito daga motar ransa a ɓace ya shiga kiran matar tasa "Elixa!!! Kafin ya rufe baki idonsa ya sauƙa a kan wasu samari guda biyu, zaune a cikin palorn nasa. Cikin tsananin mamaki ganin harda musilmi a cikinsu ya ce "Meya kawo su? Mommy ta ce "wai kuɗin Samuel sukazo biya shine nace sujira ka kadawo. Cikin mamaki daddy yake binsu da kallo haɗida zubawa shigar wannan ba haushen da kallon tsana domin kuwa doguwar riga ce a jikinsa sai hula mai kyin gaske. Ya ce "Suwaye kuɗin? menene haɗinku dashi? kuma yaushe ya baku aron kuɗinsa?.

Kowa yabar gida tabbas gida ya barshi! Yau dai ga Hajiya Babba tareda AJ a ƙasar 9j. Kana kallon fuskar Hajiya Babba kasan babu annuri ko kaɗan, harma wani jajaja fuskarta keyi. Yayinda shi kuwa AJ ya buɗe ido yana kallon ƙasar tasa wacce bai taɓa barintaba koda kuwa na kwana ɗayane Amma yanzu harna kwanaki biyar. Mota suka shiga izuwa gida, yayinda AJ yake kallon komai kamar a mafarki. A ƙofar gidan Hajiya Babba sukayi parking ta ce "Ya fita yaje gida in yazo anjima zata kirashi, kuma zata tura masa kuɗin idan ta shiga gida. Kasan cewar da yamma ne sai kawai AJ ya ce "To angama dama nimanna matsu naga Innah da Nana. Saida tafiya wani shafi yayi musu soyayya mai yawa kafin ya nufi unguwar tasu.

Tin daga bakin layin unguwarsu yaga ana ta kallonsa sai kawai ya bar hakan akan irin kayan dake jikinsane yasa, yana tafiya baya ko kallon kowa kamar yanda ya saba a da bare yanzu da yake ganin shima wanine, suma ƴan uwarsa da yake sun san halinsa na ɗaukar kansa yafikowa yasa babu wanda tanada mgn sai kallonsa da sukeyi. Kallon ƙofar gidan nasu yayi a buɗe, sai kawai yasa kai ya shiga yana sallama haɗida zabgawa Innah kira cikin muryarsa dake nuna cewar yayi kewarsu sosai.....✍️






*Abin tambaya. Shin meye tsakanin su Hajiya Babba da Comandar Daniyel? Shin ina ne Abdalha yaje? Shin da gaske shine ya sace Zainab? To gadai AJ ya sauƙa a 9j? Me zai faru? Yanzu komai zai warware. KUKASANCE da S REZA. Domin jin me zaifaru.*


*

*Kafin kufara karanta wannan page ɗin, inaso kutuna abunda nace a page ɗin farko, Pls* 🙏


*PAGE. 2️⃣1️⃣*

......... Innah! Innah! Innah! Cikin murna da ɗokin son ganin Innar tasa yake ranƙaɗa mata wannan uban kiran kai ka rantse da Allah irin ya hangota daga nesane amma bata jisaba. Saboda tsabar ɗoki da AJ keyine yasa bai ko kula da kurarr da gidan ya ɗanyiba, sai kawai ya nufi ɗakin Innah da sauri yana cigaba da kiran sunanta, wannan karan harda sunan Nana yake haɗawa. Cikin mamaki yake kallon ƙofar innar tasa abuɗe gakuma kwanukan abinci da sauran abincin dake ciki alamar dai andaɗe ba'a cikin gidan, da sauri ya fito daga ɗakin Innah ya nufi ɗakin Nana. Yana zuwa itama yaga ƙofar ɗakin abuɗe, har yanzu bai daina kiran sunan Nana ba, yana shiga idonsa ya fara sauƙa a kan kadonta, sai ya hango wayarta a kan gadon, ai kuwa da sauri ya ɗauka yana ƙoƙarin kunnawa, amma wayar taƙi kunnuwa, domin kuwa babu caji. Fitowa yayi da wayar izuwa tsakar gida jikinsa har rawa yakeyi domin kuwa izuwa yanzu jikinsa ya fara aiyana masa mugayan abubuwa a kan su innah. Sai a lokacin yabi ko'ina na gidan da kallo yaga tabbas babu kowa a gidan. Afili ya ce "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, ina su inna suka tafi!? Cikin zafin rai ya ɗauki wayarsa ya shiga kiran Hajiya Babba, ai kuwa kira ɗaya ta ɗaga, tana cewa "Pls ina zuwa zan kiraka. Tana gama faɗa ta kashe wayar batare da tajira abunda zaiceba.

Sai a lokacin kuma ya fashe da wani irin kuka ya ce "No no no yana faɗa yana girgiza hannunsa yana jabaya, ya ce "Noooooooo! tabbas bai yarda da abunda zuciyarsa take cemasa akan su innha ɗinba, hakanne yasa yayi waje izuwa ƙofar gidan su, yana zuwa kuma ya tsaya yana kallon al'ummar gurin cikin rikicewa yarasa abunyi sai kawai ya nufi gurin taron samarin da ke kusa da wani ɗan shago, wanda shi a tunaninsa dai idan bai mantaba bai taɓa zama a gurinba ko kuma yayi musu mgn ko sallama aganin sa su ƴaƴan talakawa shima haka to me slamar zata ƙara musu, saidema idan yazo hucewa ya dinga musu kallon banza yayinda sukuma suka ɗaukeshi mai gyrman kai, domin kuwa sunsan bai ajiyeba kuma bai baiwa kowa a jiyaba sai shegin iyayi da nuna shi wanine.

Ko sallama baiyiba ya ƙarasa gurin tsabar a rikice yake ya ce "Ina kuka kaimin Innah ta da Nana Pls? Yayi maganar ne baisan cewar abunda yafito daga bakinsa ba kenann yaci gaba da cewa...Dan Allah ku fito min dasu sune kaɗai gareni pls dan Allah kuyi mgn Walhi zan iya shiga wani hali, idan laifi nayi muku a kaina zaku sauƙe basuba. Kamar haɗin baki yana kaiwa aya duk samarin gurin suka watse suka barshi babu wanda ya tamka masa sai wani guda ɗaya wanda daga gani kasan yafi kowa jin haushin Aj ɗin ya ce "Kai amma Walhi kama raina mana wayo, watoma mune ɓarayin da zamu sace maka u'wa ko? To me suke dashi da har zamu sacesu, kaje can gurin da ka aikata satar ka kanemesu amma ba nann ba. Kasan cewar sunji wai-wai AJ ɗin sata yiyi daga bakin duniya. Saurayin na gama faɗar haka ya bar gurin cikeda jin haushin AJ ɗin.

Shiru yayi yana tauna maganar yaron ta ƙarshe wai sata! sata! sata! Haka yaketa mai-maita sunan sata ko zai tuno lokacin da yayita amma ya kasa ya ce "Nine nayi sata!? To a ina! Kuma yaushe! ƙaryane walhi ƙaryane ni ban taɓa sataba saide wani amma baniba. Ya ɗaga kai domin tambayar gayan amma ko alamarsa bai hangoba, ya juya izuwa hagunsa sai yaga yara suna klonsa kamar wani mahaukaci. Tabbas sai yanzu yasan cewar ashe abokima wani ɓangarene da zai dinga taimaka maka a rayuwa, shi baida abokai duk yaci mutuncin su, ya koresu wai abota ƴaƴan talakawa a tare batada amfani. Chak ya tsaya bayan ya tuno da abokinsa Kamal, Wanda babu irin cimutuncin da bai masaba amma kamal ɗin yaƙi haƙura domin yana zuwa nemansa kokuma yaje su haɗu a gidan bredin da yake aiki a da. Da sauri yatashi domin nufar gidan su kamal ɗin amma ya ji ankira sunansa AJ.

Chak ya tsaya yana juyowa fuskarsa duk ajiƙeda hawaye, idonsa yayi ja duk ya fita a haiyacinsa. Kadija ce ƙawar Nana wacce itama ta samu labarin abun daga bakin ƴan unguwar domin kuwa kowa yaji lokacin da sojojin suka shigo unguwar kuma suka tafi da su Nana ɗin. "Sojojine sukazo suka tafi da Innah da Nana yau kwana huɗu kenan basu dawo ba kuma bamusan inane suka kaisuba. Ya manta da cewar yarinyar ta ce masa basu san me su Nana sukayiba amma tsabar ruɗewa ya ce "Sojoji! mai sukayi, ya faɗa yana ruƙo hannun kadijar kamar itace zata sanar masa da komai. Ta sake cewa Walhi abunda na sani kenan. Tafaɗa cikin rawar murya domin riƙon da ya mata. Kafin aj yayi magana wani saurayi da yasan AJ tare da Sarah ne ya ce...

"Wannan sojan baban wannan arniyar budurwarka ɗain ne yazo ya tafi dasu harda duka da zagin duk wani musilmi dake duniya bama iya kan ƴan unguwaba kuma harda yarinyar a kazo da alamar dai itace ta nuna musu gidan naku, kuma sunzo basu gankaba shene sukayi ram da tsohuwar Allah da batasa hawaba bare sauƙa...sau rayin ya ƙare da cewar damade ba ciki kamataba domin naga itama sai kuka takeyi da alamar dai itama an ɗan samota kafin su fito, kasan fa sojoji basuda tausayi harta ƴaƴan suma tafka sukeyi bare ƴaƴan wasu.

AJ ya saki hannun Kadija wanda shi baima san ya riƙetaba, afili ya ce "Soja Sarah baban ta kenan ya kamata ita kuma ta zo nunani. dalla-dalla zuciyarsa ta faiyace masa komai shikuma baisan cewar a fili yake faɗaba, acikin minty ɗaya zuciyar sa ta sanar masa da duk abunda ya faru, kuma yasan hakanne. Rasa wani irin tunani zai farayi daga ciki domin kuwa yasan yakamata yayi tunani amma ya kasa, sai kawai ya miƙe ya nufi gidan su Sarah cikin dakiyar zuciya, yana tafiya yana tuno irin wahalar dasu Innah suka sha a hannun wannan baƙin kafirin da kowa yayi shedarsa wajan cin mutuncin Addinin Musulunci koda kuwa babu dalili bare kuma a ce akwai dalil. Yana tafiya hawaye na wanke masa ido na tausayin su Innah da Nana.

*ABDALHA POV*

Da sauri Abdalha ya dawo da kallonsa izuwa gurin samarin dake cikin gidan ya ce "Me kuka ai kata mata? Yayi tambayar cikin rikicewa, kafin su bashi amsa yayi gurin da take kwance kamar macacciya ya ɗago fuskarta yaga idonta a rufe, sai kawai ya ɗauketa izuwa matarsa, bai ko ƙara kallon samarinba, ɗaya daga cikin samarinne ya ce "Mlm Walhi taci albarkacinka badan hakaba da daga yau idan akace ta ƙara zagin malamammu a ciki waƙa bazata ƙaraba shegiya kuma har yanzu zamuci gaba da bibiyarta shege ka fasa mara kunyar banza ƴar tasha kawai. ɗaya daga cikin kuma yana ganawa cikin ihuu!. Abdalha baiko bi takansa ba ya hanyar barin gidan. Kasancewar yanzu nemanta akeyi kuma ko ina hotontane ke yawo sai kawai ya kaita gidan likitan sa domin sirri. Tun kafin ya isa gidan ya kira likitan ya sanar dashi cewar yazo gida idan baya gida yanada emergency, likitan ya sanar masa da cewar yana gida yau domin madam ɗinsa bata jin daɗi. Haka kuwa a kayi ABDALLAH ya huce da Zainab gidan likitan nasa.

Shine ya ƙara ɗaukarta har cikin gidan bayan likitan ya taimaka masa, likitan mai suna Musa bai ganetaba domin kuwa yanda ta fita a haiyacinta ga kuma rama da

14 / 37