Nida kishiyoyina complete Hausa Novel

Author :  Sajida Niger Category :  Romance

Chapter   22 / 38

63K to 66K   out of 111.9K words

tunanin inda kika dosa dan Allah kice ba haka bane"

Aunty mamy ta karashe da rawar murya

Aisha sai ta kasa bud'e baki ta mata magana Ashraf kuwa sallati kawai yake ya dafe kansa.

Yaya mustapha kuwa a hankali ya juya ya fara k'ok'arin nufar d'aki

Aisha tayi saurin cewa "Yaya"

Ya daga mata hannu batare da ya juyo ba yace "Ba sai kin ce min komai ba nagane mai yake faruwa"

Daga haka ya shige dakinsa

Aisha kuwa ta kara rushewa da sabon kuka Aunty mamy kuwa cikin rawar baki ta daga hannu ta nuna Nana tana "Kina nufin Salisu mijinki shine mahaifin Nana shine Wanda yayi wa muhasim fyade ya Kuma karkata mata wuya"?

"Shine Aunty mamy Salisu ne mahaifin Nana shine ya mata fyade ya karkata mata baki"

"Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun innalillahi wa Inna ilaihi rajiun Aisha mai mu ka masa da muka cancanci haka daga wajen sa wanan wane irin zalunci ne wanan wane irin cin Amana ne ya rasa wacce zai yiwa fyade sai muhasim shekara sha biyar 'yata sai dai a kwantar a tayar da aure tayi yanzu da tana gidan ta da yaran ta biyu ko uku a gaskiya bazan tab'a yafe masa ba Allah ya Isa tskanina dashi,ko baki kwato mata hakkin ta ba ni zan kwatowa yata hakkin ta wanan zalinci da mai yayi kama?dama ashe fuska biyu ne dashi ba dan Allah yake zaune damu ba dama shine yayi wa muhasim fyade yasan zata iya tona masa asiri shine ya karkata mata baki Allah ya saka min bazan tab'a yafe masa tashin hankalin daya jefa nida yata ba"


Kuka Aunty mamy kawai take tana jin ciwon dake zuciyarta na dawowa sabo fil

Aisha kuwa mik'ewa tayi tabi bayan Yaya mustapha a hankali ta tura k'ofar ta same shi a kwance yayi ringingine idonsa ya Kada yayi jajjir duk jijjiyoyin kansa sun tattashi.

Aisha ganinsa a cikin wanan halin ya Kara karya mata zuciya ta zauna a gefen gadon tana "Yaya ban tab'a sanin haka Salisu yake ba ban tab'a kawo wa zai iya yiwa muhasim fyade har ya iya karkata mata wuya ba, Yaya Salis ya wuce duk yanda nake tunani a jiya daddare na gano mugayen halayensa,a jiya daddare Luba ta tona Masa asiri Ashe tasan shine yayiwa muhasim Fyade ko a fuska bata tab'a nuna min ta sani ba duk daukana ma bata san ya nake da nana ba Ashe duk tasan komai Yaya wlh wlh sai nayi karar Salis a yau ba sai gobe ba sai na kwatowa Muhasim hakkin ta Yaya kayi hakuri ban tab'a sanin Salis zai iya cutar da muhasim ba anjima kad'an zanje nayi kararsa"

Har ta gama magana Yaya mustapha bai ce mata komai ba illa ajiayar zuciya kawai da yake ta saki.

Tasan halin yayanta bazai iya magana ba a yanzu kila sai anjima

Mik'ewa tayi ta fito ta tarar da har lokacin Aunty mamy na kuka.

Umar dasu Kabir duk sun buga tagumi Nana Kuma ta takure waje daya muhasim na Kan keke.

Aisha wajen da mamy ke zaune ta nufa ta ruko hannun ta tana "Ki bar kuka haka Aunty mamy karki damu Insha Allahu karshen zaluncun da Salis yayi mana yazo, zanyi Sharia dashi har sai ya fito ya fadamin abinda yayi wa muhasim bakinta ya karkace tunda har kika ga na hakura da aurensa na rabu da yarana kinsan na shirya dan na kwatowa Muhasim hakkin ta ki bar kuka haka anjima kad'a zan fita nayi kararsa a yanzu kaina ciwo yake min Ina bukatar nutsuwa"

Aunty mamy gyada mata kai tayi.

Aisha ta mik'e tsaye duk da jirin dake dibarta haka taja keken muhasim Nana na biye da ita a baya har suka shige dakin su Muhasim din.


Suna shiga d'akin ta Kai keken muhasim kusa da katifa da dabara ta dagata daga kan keken ta kwantar da ita akan gadon.


Wani irin tausayin muhasim ke nukurkusarta a zuciyarta,sai da ta kwantar da ita ta ruko hannyen ta tasan duk abinda zata ce tana jinta magana ne kawai bazata iya ba
"muhasim zan tsaya miki har sai an yankewa Salisu hukunci da ya dace dashi a baya dama ya Dade Yana nemanki"?

Muhasim idonta ta lumshe ta sake bud'ewa.


Aisha lumshe idonta tayi hawayen da take ta san maida wa suka zubo mata.

Ta kwanta a gefen muhasim a yanda take Jin zuciyar ta ji take Kamar ta samo Salis ta raba shi da numfashinsa wani irin tsanarsa take ji a zuciyar ta,tafi jin ciwon abinda yayi wa muhasim akan Luba da ya aura.

Tafi minti talatin a kwance
Shigowar Umar da flask din shayi da kofi yasa ta bud'e idonta sai da ya ajiye flask din yana k'ok'arin fita tace masa ya taimaka mata da wayarta da ta bari a Palo.

Fitarsa da mintuna ya dawo da wayar ta a hannunsa ya mik'a mata wayar.

Ya juya ya fita

Ta kalli Nana dake kwance lamo kamar mai bacci ta bubuga kafarta tana "Tashi ki sha shayi Nana"


Da ido ta ringa bin Nanan har ta sauko daga kan gadon ta zuba shayin ta fara Sha.

Shekara da shekaru tana addua Allah ya tonawa Wanda yayiwa muhasim Fyade ko dan Nana tasan ma waye mahaifinta Ashe Salisu mijinta shine mahaifinta.

Lambar wata hajiya Hauwa ta Nemo a wayar ta,shekara shidda da suka wuce ta hadu da ita a saudiya da taje umara.

Suna mutunci da ita sosai duk da Luba ta koya mata hankali tsoron ma muamalla take da mutane amma hajiya Hauwa haka ta makale mata su ke dan zumuncin sama sama sau biyu ma tana zuwa wajenta,a cikin dan tarihin da ta bata mijinta babban lauya ne a wanan gab'ar ba Wanda zai taimaka mata sama da Hajiya hauwa da mijin nata.

Bugu biyu Hajiya hauwa ta d'auki wayar sai da suka gama gaisawa Aisha ta fada mata tana so ta shigo wajenta akwai taimakon ta da take so tayi.

Hajiya hauwa kuwa ta ce mata sai tazo yanzu zata turo mata address din gidan.

Godiya Aisha ta mata ta katse wayar tana k'ok'arin ajiye wayar yayanta ya turo k'ofar ya shigo.


Luba

A lokacin da ta isa gidan Hamza dak'yar mai gadi ya barta ta shiga dan dagewa yayi masu gidan basu san da zuwanta ba sai da ta hada da hankade shi ta shige ciki tayi cikin gidan da sauri


Gabanta ne ya yanke ya fadi a lokacin da ta hango Hamza ya fito daga gidan Sultan na daga gefensa hanunsa rik'e da wani jaka.

Rabon da ta saka Hamza a idon nata kuwa ta manta ko ba'a fada ba kana ganinsa kasan kudi sun zauna masa dan har wani tumbi ya ajiye.


Dake wa tayi a daidai lokacin da suka karaso wajen da take tsaye

Take murmushi dake saman fuskar sa ta gushe ya hade rai Yana "Baiwar Allah mai kike nema a gidana?

"Ikon Allah bangane mai nake nema a gidanka ba Mai kuwa zan zo nema a gidan ka wajen yarana nazo"

"Yaran da kika watsar dasu tun suna Yara Kika zo neman su a yanzu"?

"Hamza kaga baka fa isa ka rabani da yarana ba naga baka da burin daya wuce kaga ka rabani dasu Kuma ba mai yuwa bane dan ni na Sha wahalar cikinsu na haifesu wajen yarana nazo na musu kwana biyu"


Wani irin murmushi Hamza yayi Yana "Bazan rabaki da yaran ki ba amma ki bari su ringa zuwa wajen da kike ko ki tsaya daga waje su zo su Same ki daga yau kar ki Kara taka kafar ki ki shigo min gida kije daga waje yanzu zasu zo su Same ki"

"Ni hira nake so nayi da yarana na samu lokaci da su ko kwana biyune nayi dasu kafin na koma gidana"

"Sai dai ki tafi dasu bazan hanaki ba amma batun wai ki musu kwana biyu a gidana ba Mai yuwa bane dan Allah juya kifita"


"Umma mu je daga wajen bari na Kira ilham"

A takaice Luba tana ji tana gani Hamza ya koreta waje sultan da ilham kuwa suna gaisheta sama sama Sultan yace mata zai bi Abbansa zasu je unguwa daga haka ya shige cikin mota bai ma saurareta ba ballantana ta samu kudi a wajensa.

Ilham kuwa tana ganin Sultan ya tafi itama tacewa Luba zata shiga daga ciki tana taya Maminta aiki ne ta gaida gida.

Luba kuwa bata iya motsawa ba sabida tsananin bakin ciki ta kasa yarda yaran da ta Haifa a cikinta ne suke nuna mata halin ko inkula bata ga alamar soyayyarta a idonsu ba.

A yanzu wajen da zata kwana kawai take nema kafin gobe tasan yanda zata je gidan asabe ta bata kudadenta.

A.haka tayi ta bulayi a karshe sai a shagon abokin kaninta Sadi taje ta roke shi akan zata kwana dan a hanya ta had'u dashi Yana gaisheta ta roke shi akan ya nema mata wajen kwana kafin gobe.

Hakane yasa ya mata tayin shagonsa.


D'akin Nasa ba kintsi katifar wata mitsitsiya Luba kuwa har da kukan ta dan ko a mafarki bata tab'a kawowa wai zata tsinci kanta a cikin wanan halin ba.


Yunwar da take ji yasa bata tsaya cutar kanta ba ta d'auki furar da ya kawo mata ta kafa Kai ta kwankwade

Ya riga yace mata zai je ya nemi wani wajen ya kwana.

Tana Shan furar taji jikinta ya mutu a haka ta kwanta tana Jin bacci bacci.

Ido biyu ido rufe haka ta kwanta tsawon awa biyu tana kwancen ba bacci take ba amma jikinta a mace yake ko daga hannunta Bata iyawa.

Turo k'ofar dakin taga anyi a hankali a cikin duhun tana iya ganin gambon ya shigo cikin sanda ya hau tube kayansa.

Gabanta ne ya yanke ya Fadi so take ta mik'e tsaye amma ta kasa so take ta Masa magana yasan idonta biyu amma ta kasa kar dai saan dan cikinta ke san yi Mata fyade yaron jikinsa duk kyazbi ne hasali ma Almajirine.

Tana kallonsa ya gama tub'e kayansa yazo ya haye kanta.......


Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne, knuckles,wrinkles,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulun mg's batare da kunbukaci wani Mai b>?? Mai bukata should
Chat=?G?
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391

Team glow>???
@&?



Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne, knuckles,wrinkles,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulun mg's batare da kunbukaci wani Mai b>?? Mai bukata should
Chat=?G?
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391

Team glow>???
@&?


*WANAN LITTAFIN NA KUDINE BIYA 500 TA WANAN ACCT 0272061655 WEMA BANK NAFISA NUHU KO KATIN MTN KO AIRTEL TA WANAN LAYIN 08033719070 DOMIN KI MALLAKI NAKI KI MUTANEN NIGER KUMA KU TUNTUBI WANAN LAYIN*
*+227 96 82 89 84 DUK WACCE TA MIN SHARING NA BAR TA DA* *RABBI ZAI FIDDA MIN HAKKI NA DA IZININ ALLAH DOMIN BA YAFEWA NAYI BA*


*NI DA KISHIYOYINA*

*NA SADNAF*

*PAGE 24*

Gambo bidirin sa kawai ya ringa yi a kanta Luba ko hannun ta bata iya dagawa kukan zuci kawai take ta kasa yarda wai yau ita Gambo kazami da take aika idan taje gidan su har kudi take jefa masa akan yaje ya siyo sabulu yayi wanka,kiri kiri take nuna masa kyama sai gashi Wai yau itace ya haye cikinta Yana sarrafa ta kamar ya samu matarsa,doyin da take shakowa a jikinsa da bakinsa da yake dalolo mata da Sunan kiss kawai yasa ta kusa sumewa bazata iya lissafa tsawon lokacin da ya d'auka a kanta ba gashi har lokacin bata da k'arfi bude ma baki tayi magana wahala yake Mata,yanayi yana hutawa sai da aka kira Sallah asuba ya sauka daga kanta Yana "Hajiya na dade Ina adduar Allah ya kawo min ranar da zaki zo hannuna na dandana zumar ki tunda ga lokacin da kike kyamata ta kina nuna min ban isa na hada kafada da Sadi ba,nake addua Allah ya bani nassara akan ki ko jininki Ina addua Allah yasa na miki ajiyar da zaki ringa gani ki ringa tunawa dani,dan idan kika duba d'akin zaki ga ba kayana a yau naso komawa kauyen mu nabi motar dare sai Kuma Allah ya hadamu na samu cikar burina wanan ya zame miki darasi dan Adam ba abin wulakantawa bane na bar ki lafiya"


Luba hawaye kawai take tana kallon sa har ya fice daga d'akin.

Ta dau tsawon lokaci a haka kafin ta fara dan Jin kwarin jikinta har lokacin kukan zuci take wai gambo da bai wuce saa ilham.ne ya mata wanan cin mutuncin ko Ina na jikinta ma wari yake,yau ita ce rayuwa ya juya da ita haka har ace duk tarin dukiyarta da takardun filayenta ta rasa wajen kwana ta Fado hannun Gambo ya kwanta da ita.

Ba komai a d'akin sai tarkacen kwanuka allo da katifar da take kwance a Kai,taya zata iya fita batare da ta wanke jikinta ko zata daina Jin abinda take ji a kasan ta ba.

Da rarrafe ta hau birkita d'akin dan tsayuwar ma bazata iya ba dak'yar ta samu ruwa a wani karamin buta ba abinda ruwan zai mata a haka ta watsa a gaban ta ta cire dan skirt din ta ta goge duk jikin ta kyankaymin kanta kawai take tana tarar yawu a bakinta sai da ta kara awa daya a d'akin dan sau biyu tana gwada tashi sai taji Kamar iska zai d'auketa da alama magani mai k'arfi gambon ya sa mata a furar.

Sai da ta dan ji dama dama ta mik'e ta fice daga d'akin tana Shan alwashin Nemo gambo a duk Inda yake dan ba abinda zai hana ta daureshi har sai taga gatansa.

Babban burin ta yanzu ta samu wajen da zata cuda jikinta ta wanke jikinta da take Jin ya Kama warin jikin gambo ta samu ta canza kayan jikinta ta tafi gidan Asabe ta bata kudadenta dan bazai yu da uwar kudadenta ta ringa bulayi tana neman wajen zama ba kudin ta na wajen Asabe zasu ishet??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a ta siyi karamin gida ta juya sauran kudin ta yanzu wajen da zata fara zuwa tayi wanka ta canza kayan jikin ta take nema ko a mafarki bata tab'a tunanin Asabe zata juya mata baya ba,yanda Aisha ta Zama tamkar shashasha a wajenta ta ringa mulkarta haka Asabe ta ringa juyata tana mulkarta wani zubin sai taji Kamar ta rabu da ita sai Kuma ta fasa dan Asaben tana taimaka Mata sosai wajen samun cikar burinta,sai gashi daga mutuwar aurenta Asabe ta murzawa idonta toka,rashin basira da hauka ya Kai ta tonawa Salis asiri,sai gashi ita nata asirin ma yafi tonuwa daga lokacin da ya saketa har zuwa yanzu bata Kara samun kwanciyar hankali ba garari kawai take har da almajiri mai doyi da bai wuce saan dan cikinta ba ya mata fyade.

Ba inda zata je dai tayi wankan daya wuce gidan su tasan mahaifinta nada zuciya ko duk mutanen garin nan zata Kai akan a roke shi ya barta ta zauna bazai tab'a sauraran su ba da ace ta tab'a kawowa kan ta irin wanan ranar da ta zage wajen kyautata musu.

Gidan nasu ta nufa dan tasan a yanzu mahaifinta ya fita bazata same shi a gida ba ballantana ya hana ta shiga gidan.

A lokacin da ta isa gidan kuwa bata same shi ba sai Inna da yayarta Habiba da basa ko magana ballantana su hada inuwa daya dan rashin mutunci sosai ta karta mata da ta isheta da waazin abinda takeyi bai dace ba ya zaayi ace iyayensu ma bazata na mutunta su ba.

Ganin ta take matar mai kudi duk girman mutum yayi kad'an ya taka ta hakane yasa tayi wa habiba kaca kaca dan tasan sai dai habiban ta moreta ba ta da abinda zata bata, habiban kuwa ta Sha alwashin fita daga harkarta.

Inna ce kawai ta amsa sallamar da tayi habiba dankwalin kanta ta turo gaban goshinta tana "Mai matar Alhaji tazo nema a gidan talakawa baiwar Allah ko b'atan hanya kikayi"?

Luba ko kallonta bata yi ba ta fara k'ok'arin shiga cikin d'akin.

Inna ta dakatar da ita tana "Luba ki rufamin asiri kizo ki tafi karki jawomin dan wlh Baban ku yace idan har na sake na Kara barin ki kika zo gidanan bai yafe ba Kuma a bakacin Aurena"

Luba juyowa tayi cikin wani irin muryar masifa tana "Inna idan ban zo gidanan ba Ina kuke so naje"?

Ina da sama da kune shikenan dan Aurena ya mutu sai a nemi a wulakantani Inna ko Abba zai koreni ya Kamata ace ki biye mishi har Kina na rufa miki asiri nazo na fita,Ina da iyayen da suka wuce ku ne"


"A yanzu da aka sako ki Kika san kina da iyaye ai mallama kizo ki fice a gidanan ba abinda ya shafe mu da sakin da aka miki sai a yanzu da kika zama sakakiya kika San ma kina da iyaye har ma suna da gidan da zaki zo gidan da kike kyankyaminsa, gidan da idan zaki zo sai da turare,gidan da idan kika zo kike toshe hanci yau shine gidan da zaki zo ki zauna kiyi Zawarci ai wlh baki isa ba ko inna ta bar ki wlh sai na zuga Abba ya koreki ba dai duniya kika zaba ba wlh baki fara ganin komai ba"


"Sai ki bari idan akwai kudinki a gina gidanan sai ki koreni,idan kuma kina da k'arfi zaki iya zuwa ki fita dani, Abba Kuma ko ya koreni wlh sai na dawo ba inda zanje dan shine ya haifeni idan Kuma ya dage

22 / 38