Dingishin Kwado Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Salma Category :  Adventure

Chapter   9 / 37

24K to 27K   out of 110.8K words

ba". Abida ta ce"Oh Yaya Munira ga ni kike zan kasa cika alk'awari ne? Ko kuwa so kike yanzun ma ki nuna kin fini son Maigado? Ki daina shigoa tsakaninmu don ke ce da kunya!

Aka kyalkyale da dariya gabadaya. Daga nan ta gaisa da Su Yaya Salaha aka mikawa Yaya Asad wayar, haka aka dinga bawa y'an mazan d'aya bayan d'aya sai da ta gaisa da kowa. Daga nan aka yi sallama da Yaya Munira da ahalinta.

Anty Rukayya matar Yaya Asad tana cikinmu tamkar ba suruka ba, Khadija da Aysha sun kammala sakandire a wannan shekarar. Yayin da Hafsina take aji biyar na sakandire sai kuma takwarata Bilki a aji uku na k'aramar sakandire.

Amal ta kammala primary, sai kuma Noor mai shekaru uku.

Kallo d'aya zaka yiwa ya'yansa da matarsa ka gane kud'i na amo a jikinsu domin ba ya yiwa iyalinsa k'wange, ado suke yi na alfarma k'warai da gaske.

Dukkanmu kowa na cikin wadata da rufin asiri.

A wannan zama aka yi maganar auren Ansari da yake so iyaye su shiga maganar.

Yaya Farouk yaransa biyar na Yaya Usman uku. Su Saddiqa da Anisa kowa da nata yaran.

Na kalli yadda muka cika harabar gidan namu mu da ya'yanmu mun zama gayya guda.

*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*

*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*

*08163761797*

Washegari Yaya Asad ya fara tafiya don Kaduna zasu je su hau jirgi zuwa Lagos don shine (D.P.C)Deputy police commissioner na jihar. Saddiqa da take Kaduna ta shiga motar da aka turo masa.

Kud'ad'e masu nauyi ya turawa kowannenmu a cikin asusun da sunan barka da sallah.

Kafin yamma kusan kowa ya tafi ni da su Abida ne muka rage akan sai gobe zan bisu mu tafi. Farha tunda ta ga Abida ta makale mata, idan kuma bata ganta ba to tana makale a jikina. Yayin da Abida take kawaicin kin daukarta har sai na ce "A a dauke ta mana kada ki saka mini yarinya kuka".

Washegari muka tafi muka bar iyayenmu da kewa.

Har gida suka kaimu sannan suka tafi nasu gidan.

Ga mamakina Farha bata yi kukan zata bisu ba.

Ranar alhamis da yammaci muka riski mummunan labarin da ya gigitamu gabadaya.

Baba Karami ya zo taron da ma'aikatrsu ta shiryawa tsofaffin Daraktocin da suka rike maaaktarsu. Yaya Farouk ne ya kawo shi tunda tuni ya yi ritaya ya koma gida Funtua gabadaya.

Sun kammala zasu koma juyin duniya motar ta k'i tashi. Ganin haka Yaya Sulaiman ya ce "Bari ya kaisu sai ya dawo, idan dare ya yi masa ya dawo gobe. Sun zo daidai... daf da Funtua Yaya Farouk ya sauka akan zai yi magana da masu yi masa aikin cire albasa, zai hawo mashin ya k'araso.

Ba jimawa da saukar Yaya Farouk wani mai amalanke ya taho a guje ya shigo musu take motar ta dinga walankeluwa bayan ta daki bijimin sa da k'arfin gaske. Motar bata tsaya ba sai da ta je ta bugi wata bishiyar mangwaro kafin ta hautsina gabadaya.

Kan ka ce kwabo mutanen k'auyen sun yi dafifi suna ta 'kok'arin ceton ransu. An ciro Yaya Sulaiman a sume jini na ta fita a hancinsa da bakinsa yayin da Baba karami aka kasa ciro shi. Ganin hakan ya sanya suka yi dabarar tarar wata mota aka sanya Yaya Sulaiman da wasu zuwa babban asibitin cikin Funtua.

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Baba karami kam sai da aka sare gaban motar sannan aka fito da shi sai dai Babu rai ya amsa kiran mahaliccinmu.

Wannan mutuwar na tsaya hakaito muku yadda ta yi mana mugun bugu bata lokaci ne mai yawa. Amma mutuwar Baba ya zama tamkar tafiya da dukkan nutsuwa da walwalarmune gabadaya.

Daidai nan kuka mai tsananin gaske ya k'wace mini, dama lallaba zuciyata nake yi sai kuma na zo inda duk dauriyata dole na koka, dole hankalina ya tashi domin an zo gabar da bana fatan masifar da ta sauko mana ta sauka kan kowanne ahali.

Mutuwa da ciwo da tonon silili take. Allah ka jikan makabantanmu.

Da yake dab da magariba aka yi hadarin labarin mutuwar sai bayan magariba ya riskemu. Cikin tashin hankali na isa gidan Abida.

Kuka muke yi kan kuka ita kam ta tubure a lokacin zamu tafi tunda Yaya Sulaiman na asibiti rai a hannun Allah.

Da k'yar da sudin goshi Yaya Asad ya dakatar damu akan gobe da asuba zai saka a zo a kaimu Funtua.

Barci barawo a wannan ranar bai iya satarmu ba. Gabadaya ni da Abida a rikice muka ainun ba mai bawa wani hakuri. Sai dai na yi imanin Abida ta fini rikicewa. A fili cikin kuka take ce wa "Allah ka kaddara mini na ga Yaya Sulaiman da ransa, Allah na tuba kada a yi mana biyu innalillahi wa inna ilaihir raji'un!

*Bojuwa herbs*

*Oder your kayan mata for women of class*

*Our products are healthy and original*.

*Tested and trusted*.

*Sanyi flusher n zai raba ki da dukkan nau'in infection, ya kuma sabunta Ki*.

*Ki zo ki saka order din ciccibin garari ko kazar sababi ki gode mini later domin saiwowin da nake amfani da su na yi imanin ba kowa zata iya zuba kudi ta saro masu daraja irinsu ba*.

*Duk wadda ta ciccibi sai tasan ta ci abu gangariya haka ma kazar sababi*

*Just DM for your order @08033773332*.

Kuka nake yi mai tayar da hankali sosai amma da zarar na kalli Abida sai na ji tashin hankalina na sake rub'anya mussaman idan tana gunji tana rokon Ubangiji kada ya k'addara mata yin takaba a yanzu.

K'arfe shida na asuba motar y'ansanda ta zo ta kwashe mu.

Muka isa muka tarar da kofar gidanmu tamkar zai stage da jama'a.

Haka muka kutsa muka isa. Idanuwan kowa ya yi jajur tabbacin an sha kuka an gaji. Baba Babba kuwa gabad'aya ya rikice baya um baya umum ya zama wani iri k'arfin imani ya hana shi ya shiga cikinmu ya yi ta rafsa ihu, don tabbas an masa mutuwa mai gigitarwa. Mami kuwa sosai take sowa da k'yar aka samu ta koma yin na sharb'e.

Hankalinmu bai dawo ba sai yamma aka tafi asibiti wajen Yaya Sulaiman. A can muka tarar da Abida tana zaune duk ta fige ta lalace. Kasancewarta likita kuma ta yi aiki a wajen ya sanya ba'a shata mana layi wajen shiga wajensa ba. Jikinmu ya sake yin sanyi a lokacin da muka halin da yake ciki. Yana kwance bai san inda kansa yake ba.

Yanzu haka sun tura shi asibitin

K'ashi na dala. Don ya bugu sosai.

Tashin hankalin da muke cikinsa k'warai ya tsananta.

Ranar da aka yi sadaka uku aka tafi da Yaya Sulaiman asibitinn Dala cikin Kano.

Cikin k'ankanin lokaci gabadaya aka gigita mana nutsuwa da walwalarmu gabadaya, don Baba Babba ma a kwance yake ana ta kara masa ruwa.

Dukkan ahalinmu kowa ya bar inda yake ya taho gida. Daga Funtua kuwa aka d'unguma Kano nemawa Yaya Sulaiman da har lokacin ba'a san matsayin lafiyarsa ba, tunda asibitin dala ma sun ce sai an hada masa da ganin likitan kwakwalwa don ya bugu a kai. Ganin hakan Yaya Asad ya ce Farouk da Abida su shirya zasu tafi Germany ya ga likitoci a can, tunda a can ya yi karatu ya kuma yi aiki na shekaru zai samu kulawa ta mussaman.

Wata guda yana asibitin cikin coma sannnan aka samu visar tafiyarsu. Gabadaya bama cikin nutsuwa sai dai su Yaya Asad sun koma wajen aikinsu. Kan dole muka hakura muka bi Baba

da adduar rahama, aka mayar da hankali wajen neman lafiyar Yaya Sulaiman da a yanzu muke cikin tashin hankali ganinsa tamkar gawa.

*Dafatan zaku gyra zama don yanzu ne zamu kutsa cikin danbarwar labarin. Ku nutsu sosai, ku bi sannu a hankali har zuwa inda zn karkare don kuwa yanzune abin da labarin yake tafi da shi zai fara.*

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Su Abida sun isa ƙasar Germany tare da Yaya Sulaiman, sun dai yi waya damu sun sanar damu isar su amma tun bayan nan ba mu sake ji daga gare su ba, ni kaina idan na k'ira wayar Abida ba na samu, da man Yaya Faruku ne ya kira ni a lokacin da suka sauka a k'asar. Su suna can mu kuma muna nan amma zullumi bai bar mu ba, mun san ce wa mun rasa Baba ƙarami ya tafi in da har abada ba zai dawo ba, amma zullumin da fargaban halin da Yaya Sulaiman ke ciki ke nurƙurkusan dukkanmu, kowa ka yi waya da shi jikinsa a sanyayaye ba karsaashi ba farinciki.

Mami kusan ko da yaushe muka yi waya da ita cikin kuka take, haka muke ta kwantar mata da hankalin ce wa ta cigaba da addua in sha Allahu Yaya Sulaiman zai warke. Amma ita ga ni take yi kamar shima ɗin kamar Baba karami ne rasa shi za mu yi, ni kaina karfin hali na ke yi amma a yadda aka tafi da Yaya Sulaiman bai san wanda ke kansa ba kowa ma ya sare amma saboda kar na zama raunin Mami ya sa na ke daure zuciyata ina nuna mata da ikon Allah Yaya Sulaiman zai tashi da ƙafafunsa.

"Umh Bilki, shima rasa shi zan yi, rasa shi za mu yi kamar yadda muka rasa Babanku."

Kalaman Mami ke nan a duk lokacin da muka yi waya da ita shi ya sa in muka gama waya sai na zauna na ci kukana na ƙoshi ba mai lallashina. Domin Har da tausayinta ke nuk'urk'usata, mutuwar miji da rashin sanin makomar rayuwar d'a tashi guda ba k'aramin alamari ba ne.

Baban Amra lokacin farkon faruwan lamarin ya kula da ni, ya tausaya mini,amma tunda aka fara nisa da mutuwar shike nan ya janye tausayawar. Kullum sukuku na ke, ga ciwon mutuwar mahaifi ga zullimin makomar lafiyar Yaya Sulaiman.

Amma sai ya kalle ni ya ce

"Ki k'arantawa kanki wannan damuwar fa duk ba mafita ba ce, hakuri da addu'a shi ne mafita. Allah ya jiƙan Baba shi kuma Sulaiman Allah ya tashi kafaɗun sa."

Na sani gaskiya ya fada, kuma shi zuciyarsa d'aya yake fadin hakan. Amma ni so nake ace cikin taushi da laushi tare da kulawa zai dinga fada mini, ba wai ya fada ya cigaba da uzzirinsa ba.

Tun da na dawo ba na cikin sukuni da walwala, hakan bai hana shi kallo ko charting ba, har ga Allah na ji zafin sa ko dai bai taya ni kuka ba ai ya taya ni alhinin halin da na ke ciki ni da zuciyata amma bawan Allah nan da wuri ya wartsake.

Alhalin lokacin da nasa tsohon ya kwanta dama mun shafe fiye da wata ko talabijin bamu kunna ba. Ba Shi da sukunin yin kallo dan haka nima na haramta mana ni da yara dan taya shi jimami, amma abu ya zo kaina, na ga daban. Matsanancin mamakinsa kullum k'ara ara yi mini tsamari yake yi tare da tunanin mene matsalar ne?

Basmae kullum sai ta kira Ni a waya tana sake kwantar mini da hankali. Duk bayan kwana biyu sai ta zo ta debe mini kewa tare da ba ni hakuri tabbas ita ɗin ƙawar alheri ce.

Baba Babba duk dakiyarsa wannan lamarin ya raunana shi ya gaza, ko a waya na k'ira shi yadda na ke jin sa wani sanyi sanyi ba na jin daɗi, yana gida ba ya zuwa ko'ina lalle mutuwar Baba karami ta raunana kuzarinsa sosai Momi ce ma in muka yi waya da ita na ke jin karfin gwiwa domin ƙwarin da tabbaci ta ke bamu da cewa Yaya Sulaiman zai warke, mu ma kuma muna fatan haka in sha Allahu.

Tun tafiyar su ba a sake jin su Yaya Faruƙu ba, sai bayan kwana goma sannan Yaya Asad ya kira Baba Babba ya sanar da shi halin da suke ciki, ashe shi suna magana da shi, mune suka rufe hanyar sadarwa da mu, shi kuma da ya ke da aljihunsa ake yin komai, sannan a matsayinsa na babba suna k'iransa suna kuma sanar da shi halin da ake ciki.

Alhamdulillah likitoci sun yi gwaje-gwaje akan ƙwakwalwar Yaya Sulaiman jini ne ya taru a wani gefe in da aka gode ma Allah bai taɓa ƙwaƙwalwarsa ba, tuni an yi masa aiki

sannan in da ya ke da karaya sun ɗora shi sun kuma ba da tabbacin a kowani lokaci zai iya farfaɗowa, a bakin Yaya Muneera na fara jin labarin sosai n samu sassaucin zullimin da nake ciki ba ma ni kaɗai ba dukkan mu wannan labarin ya wanke kaso mafi girma daga cikin damuwarmu. Sai bayan kwana biyu na samu mgana da Abida yadda na ji muryanta cikin sukuni ya sa na samu tabbacin labarin da muka samu gaskiya ne.

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: "Maigado an gano matsalar Yaya Sulaiman na masa aiki a kansa sannan an masa na k'afa dazu!

Abin da ta fara faɗa mini ke nan ko gaisawa ma ba mu yi ba, farinciki ya cika ni na yi hamdala a fili da sarari, mun ɗan jima muna hira, tana tambayana ya su Mami da mutanen gida?

Na ce "kowa lafiya da godiyar Ubangiji, a baya dai muna cikin zullimi amma yanzu sai godiya. Ta tambayi yara, na ce su suna nan lafiya, mun ɗan jima muna hira ta ce mini za ta ɗan kwanta tun zuwan su ba ta samu barci ba.

Ranar yini na yi murna da farinciki na kira Basma na faɗa mata itama sai murnar farinciki take yi. Baban Amra ma da rawan jiki na tare shi da labarin har sai da ya ɗan rumgume ni yana faɗin" Alhamdulillah."

Nima na riƙe shi ina mai bayyana farincikina har fararen haƙorana suna bayyana tsabar murna.

Yara ranar kaf sun san Mahma na cikin farinciki saboda yadda na yini tare da su. Mutuwar Baba karami ta gigitamu k'warai da gaske mussaman da ba jinya ya yi ba. Sai kuam aka had'a mana da kila wa Kala na rayuwar Sulaiman dole dukan sai ya yi mana yawa, ace ba Baba ƙarami sannan ba Yaya Sulaiman, tabbas zukata za su raunana sai dai da ya ke Ubangiji ne mai yin abin da ya so, idan ma hakan ne ya so ya faru sai dai mu yi haƙuri ba mu isa mu ja da hukuncin Ubangijinmu ba. Labarin farfaɗowar Yaya Sulaiman ya zo mana da kwana ashirin da isar su ƙasar Germany. Yaya Faruku ne da kansa ya kira ni ya sanar da ni, bayan shi Abida ma ta sanar da Ni an kawo shi ɗakin hutu amma dai yana ta barci ne ba su samu shiga wajen nasa ba. amma tabbas ya dawo hayyacinsa. Na samu K'warin guiwar tafi ganin Mami tunda an samu cigaba sosai . Hakan ya sa na ce wa Baban Amra gobe ina son zuwa gida bai hana ni ba. Washegari na tattara yara muka zo Funtua kamar na sa ni gida cike da matansu Yaya Faruku da yara ana ta barka da arzikin da aka samu.

Baba Babba kuwa kofar gida ya fito aka tara masa almajirai ya riƙa rabon kuɗi sadaka domin godiya ga Ubangiji, mu kam mu a cikin gida kowa ka ga ni ya d'an samu k'warin jiki har Mami na ga ta d'an samu kuzari.

Yaya Asad daga can lagos ya nemi visa sai dai kawai da suka kira mu Video call suka haɗa mu da Yaya Sulaiman muka gan shi a can kwatsam ba tare da kowa ya san tafiyarsa ba. Allahu Akbar Allah mai gagara misali, sai ga Yaya Sulaimam zaune a kan gadon majinyata ga rigarsu ta asibitin kafafunsa da ya samu karaya an ɗora shi kansa da wani bandeji, amma yana zaune yana mgana kamar ba shi ne aka kai shi rai ƙwaƙwai ba, kowa ya gaishe shi kuma ya amsa sannan ya kira sunan kowa alamun dai ya dawo hayyacins sosai a Allah abin godiya.



Ni ina ganinsa sai kawai na ji kuka ya zo mini. Farha na jikina ta lafe. Abida ta leƙo da kanta tana kallona ina ta sharan ƙwalla, sai kawai ta kaɗa kai kafin ta ce" Sola ke wai me ya sa ba kya girma ne? Gaban ɗiyar ta ki, kike b'are baki kina kuka?

Ina jin ta ce haka sai na sake fashe wa da kuka don gabad'aya tausayinsa ya yi mini k'awanya Bai san mahaifinsa ya rasu ba.

Baba Babba ne ya kalle ni kafin ya ce" Bar kuka Maigado yi magana da ɗant'uwanki kin ji!

Na gyaɗa masa kai, kafin na yi magana Yaya Sulaiman ya murmusa kafin ya ce" Bilkkina ba ga ni kin ganni ba? Ki daina kuka kin j! Kar ki saka Farha ta fara gata nan idanuwanta ya kawo ruwa." Sai da ya faɗa na juya ina kallon Farha ta kusa kukan itama.

"Ya jikin ka Ya Sulaiman?

"Na ji sauƙi Bilkina. Alhamudulillah mun gode ma Allah"

Kallonsa kawai nake yi duk ya rame ya yi baƙi sai na tuna dr rasuwar Baba ƙarami kawai sai na sake fashewa da kuka kamae wata ƙaramar yarinya na ɗauka bai sani ba ashe ya sani sai ji na yi yana ce mini "Maigado ya ƙarin haƙurinmu!? Allah ya jiƙan Baba da gafara Allah ya kyautata makwancinsa"

Gabaɗaya muka amsa da Amin Yaya Usman ne na ji yana faɗa mini Yaya Asad ne ya sanar da shi bayan ya isa a jiya. Su Abida ba su samu wannan ƙarfin zuciyan sanar da shi rasuwar Baba ƙarami ba.

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Har wayar ta gama zagayawa hannun kowa ban daina kuka ba, Mami da Momi suna ƙwalla amma na farinciki ne Baba Babba faɗi yake yi" Allah na gode maka da ka karɓi ɗan'uwana, sannan ka bar mini ɗana Ubangiji na gode maka."

Muryarsa ta karye mutuwar Baba ƙarami ta sake dawo mana sabuwa dama tana jika, ba ta gama fita ba, kuma har abada ba za

9 / 37