abubuwan dai da bazan iya daukarsu ba ".
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Yayi kasa da kansa yayin da baba ya rasa me zai ce.
Da kyar ya ce ,"Wai ke wacce irin yarinya ce ne haka? Kin doshi shekaru talatin amma kina abu tamkar yar shekaru goma. Likita ce fa".
Ta ce "Da karatun likitancin zai dinga mini sai mu fafata. Amma ban da karya murya da kallo na daban mai tsanani, haba haba gaskiya Baba ni bana son a yi ta yin soyayyar nan ta masifa".
Dariya ta sosai ta kwacewa Baba ya ce"Allah ka taya ni son Maryam Abida!
Ta murmusa ta ce "Ameen Baba".
Ya wuce yana fadin "To kai Sulaiman sai ka je ka gaida Baba karami idan ya amince da nagartarka, ni da Asad sai mu nema maka aurenta a gabansa, Allah bar shi ka nemi soyayyarta idan an kai ta gidanka, tunda haka take so".
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: *Bojuwa herbs*
*Oder your kayan mata for women of class*
*Our products are healthy and original*.
*Tested and trusted*.
*Sanyi flusher dinmu zai raba ki da dukkan nau'in infection, ya kuma sabunta ki*.
*Ki zo ki saka order din ciccibin garari ko kazar sababi ki gode mini domin saiwowin da nake amfani da su na yi imanin ba kowa zai iya zuba kudi ya sarosu ba*.
*Duk wadda ta ci ciccibi sai tasan ta ci abu gangariya haka ma kazar sababi*
*Sanyi flusher kuwa best seller ne*
*Just DM for your order @08033773332*.
Baba na gama fadin haka ya wuce yayin da Abida ta yi wuf ta matso tsakiyar falon ta yadda zamu ga juna sosai.
Idonmu ya hadu nan da nan na diririce na kasa ce wa komai.
Ta bude murya sosai ta ce "Na rantse kin banu Sola. Tuni jikina ya bani kin biyo ni. Oh na ga ranar da za ki daina gana mini azaba matukar muna cikin gidan nan."
Na yi sukuri na kasa tanka mata.
Ta juya ga Yaya Sulaiman da yake fadin "Abida zo mu gama idan na tafi sai ku dora a inda kuka dakata"
Kan dole na ja jikina na shige daki ba tare da na jiyo matsayar da suka dasa aya ba.
Kamar wasa karamar magana ta zama babba don kafin na bar Funtua magana ta nuna har an saka aure watanni biyu masu zuwa a dalilin za'a yi gyara a sashen Hajiya kakarmu a nan zasu fara zama kafin a samu a mayar da Abida aiki asibitin cikin Katsina tunda a can angon yake aiki.
Amma sam Abida bata sauya ba don kuwa ba kasafai take ba shi dama su yi hira ba, idan ya kira waya nan ma bata yarda su yi doguwar hirar da ta zarta mintina goma.
Ni dai na zuba ido ina kallo tare da mamakin yadda Abida take kan sharafinta tare da gasgata dinbin soyayyar da Yaya Sulaiman yake yi mata. A duk sadda na kalli lamarin ko na tuna yadda aka yi auren sai na gasgata karfin kaddara da rabo. Domin ba dan karfin rabo ba, ban ga ta yadda suka dace ba, gabadaya hasashen yadda zaman nasu zai kaya nake yi matukar na zauna ko na kwanta da nufin na yi barci ba ni da wani lissafi ko hasashe sai mamakin lamarin Abida da Yaya Sulaiman nake yi.
Ba dan na ce a takaice zan hakaito muku rayuwarmu ta baya da komai da komai akansu zan binciko, idan kuwa na yi hakan to lamarin nasu zai mamaye labarin ba tare da mun nausa cikin alamarin da nake son ku fahimta ku kuma yi mini alkalanci ba.
A takaice kafin na bar Funtua an tsayar da lokacin aure watanni biyu masu zuwa. Mahaifiyarmu bata soki lamarin ko kadan ba, bare kuma baba karami da ya kambaba lamarin. Duk yadda na so mu tattauna da Abida akan wannan murdaddiyar soyayyar ta sha mur ta ki ba ni damar hakan. Amma na kulle tarin tambaye tambayen da nake son yi mata a hannun zanina don ba zai yiwu ta gama kushe kyawawan maza snanna rana tsaka ta tsayar da tsalelen saurayi na garari da sunan ta aminta su yi aure, ni na kuma kasa yi mata raddi duk sababinta kuwa.
Ana gobe zan koma Kano muka yi waya da Sahal nake fada masa gobe ya zo ya dauke mu. Ya gabatar mini da uzzirin gobe zai taro Baban zaria a airport zai dawo daga umrah. Na ce "To ka zo jibi, bai ce komai ba. Ni kuma na kudire goben dai zan tafi tunda na kwashe sati 2 maimakon 1 da muka zo da niyyar yi, dan haka na yi shiru ban ce masa zamu biyo motar haya ba a kokarina na yi masa bazata. Washagari na yi harama duk da ban samu an kai ni har Kano da motar gida ba, bisa hujjar Yaya Sulaiman na Katsina da motar gida da ake amafani da ita. Yaya Farouk kuwa ya je taron inganta saraffa Madara da kiwon kifi wanda yake gudana a birinin tarayya Abuja. Abida ta kai mu tasha,.sit din baya ta biya mana gabadaya ta biya kudin sannan ta wuce asibiti.
Na dawo Kano cikin matsanancin farinciki da zumudi.
Sai dai faricincikina ya koma ciki ne a dalilin tarbar da Sahal ya yi mini. Mun saba shi yake kai ni ya kuma koma ya dauko ni, amma jiya da na ce Zan dawo gobe sai ya ce mu shigo Mota ba zai samu zuwa ba baya jin dadi ba zai iya tuki na lokaci mai yawa ba.
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Zuciyata daya na ce to tare da fatan Allah ya ba shi lafiya.
Muna daf da shigowa Kano na masa waya akan ya zo ya taremu a tasha nan ma ya ce mu hau A daidaita sahu.
Jikina ya yi sanyi na shiga zullimin ko dai jikin nasa ya yi masa tsananine boye mini kawai ya yi.
Cikin sanyin jiki na isa gidan sai dai ga mamakina ba shi ba kuma motar da yake hawa.
Zuciyata ta dan yi rawa tare da tunanin wato ba a kwance yake ba, zuwa dauko ni ne ba zai iya ba, nan da nan na kore wannan zaton tare da fadin "To ko yana asibiti ma?"
Cikin kasala na kwantar da Yaya Farouk da yake ta faman barci. Na hadawa Amrah complex tare da kunna mata katoon na yi daki.
Na dauki wayata da nufin kiransa sai na ji karar bude gate tabbacin ya dawo.
A sukwane na dawo falon na zauna.
Sai da ya rufe gate din sannan ya shigo bakinsa dauke da sallama.
Amrah ta ruga wajensa. Ya dauke ta cak yana fadin "Ai da yau na yi nufin na daukoku ke da Farouk".
Kalamansa suka alamta mini yana fishi da ni a dalilin na kara kwanakin akan sati da ya ce mu yi. Abin da ya ba ni mamaki sai da na fada masa zamu kara kwanakin tunda hutun makarantar yara bai kare ba.
Haka nawa hutun bai kare ba. Bai yi inkari akan hakan ba.
Ya zauna ya kalle ni fuska ba yabo ba fallasa ya ce "Na yi zaton ba za ki dawo ba ne, har na fara tunanin zan je na debo yarana".
Na kalle shi cikin kasala na ce "Ban yi zaton zan maka abin da ranka zai sosu ka boye mini ba, ban taba hakaitowa hakan ba Baban Amrah".
Ya dauke kai ya ce ",Nan muka yi sati guda zaku yi na zo na daukoku, amma ana gobe za ki cika satin kawai kika ce mini kina ganin ba gobe zaku dawo ba ,kada na taho zaku kara kwanaki! Ya juyo da fuskarsa gare ni ya ce me kike so na ce miki tunda kin zartar da abin da kika ga ya kamace ki, sannan fada mini kika yi ba wai izini ko alfarmar hakan kike so na yi miki ba".
Na ce "To ka yi hakuri ban yi da gayya ba, wani alamarine yake faruwa da ya sanya ni farinciki da zumudi tare da tsurkun komai ya wakana a gabana ".
Ya daure fuska ya mike ya ce"Ko dai kina ganin yanzu ke kike da abin duniya, bana iya wadata ki da komai dole na yi biyayya akan abin da kika zartar a zamantakewarmu!
Gabana ya yanke ya fadi na kafe shi da manyan idanuwana na ce "Baban Amrah haba dan Allah wacce irin bahaguwar maganace haka?"
Ba damuwa ya ce "Maganar gaskiya kenan idan har ba hakan ba me zaisa ki mini irin wannan wulakancin?"
Na hadiye komai na sake ce wa "Ka yi hakuri, tunda wannan ne karon farko da na saba maka akan zuwa gida to daure ka yafe mini hakan ba zai sake maimaituwa ba ".
Ya saki ajiyar zuciya tabbacin ya huce.
A hankali ya ce "Ya wuce".
A hankali na furta "na gode".
Na tashi na shiga kicin don samar mana abinci tunda yamma ta yi sosai. A nutse nake aikin tunda akwai kayan miya a freezer da duk abin da zan bukata.
Amma kasan zuciyata ta ya yi nauyi.
Menene hujjar Sahal na ce wa "Don ba shi da shine ya sanya na yi masa abin da na yi din?"
Na furta hakan a bayyane ba tare da na shirya ba.
Bamu zauna cin abinci ba sai da ya dawo daga sallar magariba, duk da zucoyoyimu a jagule suke sosai muka ci abinci a dalilin kowannenmu yana da dauke da yunwa don ni dai tun karin kumallon safe ban sake kai komai bankina ba.
Ban saka ran zan samu tagomashi a shimfida ba tunda na riga na gane sha'awarsa mai raunice ainun.
Sai dai kuma ya nema din ya yi iya abin da zai iya, da ya samu nutsuwarsa ya bingire yana haki ba jimawa na fara jin saukar numfashinsa tabbacin barci ya murkushe shi.
Na yi lamo. Duk da a cikin duhu nake haka na tsurawa saman saman cilin ido, gabadaya idanuwana sun cika da k'walla, Ni kam haka auren yake ne ko kuwa dai ni kadai ce?
Kowanne namijine yake yin haka ko kuwa nawane kawai a hakan?
Na dinga kukan sharbe, hawaye ya dinga keto mini yana kwaranya a kan filo.
Tsawon lokaci na kasa barci don na fara gane matsaloli masu nauyi sun yi mini kawanya a gidan aurena sannu a hankali. Nauyin gida ya dawo mini, sannan kuma babu samun biyan bukata wanda wannan matsala ce da take tun farkon zuwana illa girma da take yi, kuma itace matsalar da tafi damuna don kullum ina k'ara fahimtar cutuwa nake yi sosai.
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Washagari na tashi sukuku, na gyara gidan a daddafe don gaskiya bana iya aiki sosai. Ina aikin ina tunanin dole na samo mai aiki tunda dai wanccan tawa bata dawo ba, sai daga baya nake jin labarin an tura ta Abuja.
Alti kuma da aka kawo mini ita lokacin haihuwar Farouk ta tafi garinsu wacce ta aurar da ita ce take jinya, shine ta tafi jinyarta.
Mun kai sati kafin ya warware ya dawo mini sak yadda yake. Na ba shi labarin soyayyar da ta kullum tsakanin Yaya Sulaiman da Abida. Yana bude baki sai ce wa ya yi "Tabdi jam! Wacce irin karfaffar kaddara ce haka? Yarinyar da bata ganin kowa da gashi kuma mai kafirin isgiline yaya Sulaiman zai so har ya aure ta?"
Na kalle shi na kasa ba shi amsa domin dai tabbas dole ya yi mamakin amma kuma har cikin zuciyata ban ji dadin yadda ya kausasa harshensa akan Abida ba, duk da nasan tsakaninsu da tsakuwa amma ita tunda ya aure ni bata sake aibata shi a gabana ba. Asalima yanzu yabonsa take yi tare da ce wa ya zama raina kama. Ashe dattijone a zuci ba yaro yadda yake a gangar jiki da shekaru ba.
Sanin ba zai taya ni farinciki ba sai na kame bakina na bar murnata a ciki tare da bin lamarin da adduar alheri.
Har yara suka koma makaranta nima na koma bakin aikina.
Kullum shi muke bari a gida ya bar mini kai yara da daukosu. Duk safiya zan fice da yara bayan na tanadar masa abin karyawa yayin da shi yake nade a gado yana sharar barcinsa kaitsaye babu damuwar komai.
Kwanci tashi asarar mai rai har bikin Abida ya zo. Tuni kuma na aika mata ingantaccen sanyi flusher da Bojuwa herbs (08032773332 what'sapp only)suke yi da ingantattun saiwowin da suke dagargaza sanyin mara ya wanko dattin mahaifa. Bridal package na siya mata cikin zullimin ko zata yarda ta yi amafani da su. Tuni na tura mata kayan, kazar sababi ta amare ce sai zan tafi zan kai mata na tisata a gaba har sai ta ci.
Fadin irin rawar ganin da na yi a bikin ma kauyancine da asarar lokaci.
A cikin gidanmu aka tsantsara mata jere a bangaren kakarmu wanda aka yi masa gyara na mussaman ya koma ire iren gidajen Germany.
Ginin mai ban sha'awar gaske.
Haka nan Yaya Asad ya fitar da mahaukatan kudade wajen yi mata kaya na garari har lefe ma shi ya yiwa Yaya Sulaiman. Takanas ya turasu Dubai ita da matarsa suka siyo komai, tunda ya hana Yaya Sulaiman yin lefe ya ce zai masa.
Gidan Yaya Sulaiman da Abida na cikin jerin gidajen da na ga ni na alfarma a tsawon rayuwata gabadaya.
Murna kan murna nake yi musu tare da fatan mutuwa ce zata rabasu.
Biki ya yi kyau duk da iya rana daya aka yi domin ko kamu sai ranar yini aka fesa mata nono da turare. Amma komai yar raayin ta ce na za'a yi ba.
Dan haka yinin da iyayenmu mata suka shirya ya isa bata son bidia da tsokanar shari'a a matsayin bikin murnar aure.
Ni da Yaya Munira da ta zo bikin daga Spain uwar y'ay'a biyu mata.
Mun zubawa hakimar ido don mun riga mun san halinta na ra'ayin rikau.
Rabon da na saka Yaya Asad a idona gaskiya idan har lissafina daidai ne tun aurena shekaru kusan tara don ko aurerarakin da aka yi bayan nawa bamu hadu ba duk da ya kan zo daurin auren rana daya. Wannan bikin ma daga shi sai matarsa suka zo a dalilin ba'a yi hutun makaranta ba, sun bar yaran da kanwarta da take ruk'onta tunda mahaifinsu ya rasu. Da yarinyarta Noor mai shekaru biyu kad'ai suka taho, zuwa yanzu y'ayansu shida.
A lokacin da na gan shi sai da zuciyata ta buga da karfin gaske. Yana nan kamar yadda na san shi ba wani alamun shekaru sun ja, a tsaye yake cak, ko da yake tun filazal shi mai motsa jikine sai kuma ya zama sadaukin jami'in tsaro.
Da girmamawa na gaishe shi, ya amsa gaisuwar ta hanyar sara mini tamkar yadda ya sha yi mini a shekarun baya. Dadi ya kama ni na murmusa cikin kunya kunya na ce "Anya kuwa zan karbi gaisuwar nan Baban Bilkisu?"
Ya yi waiwaiye ya ce "A a Maigado ai ba zamu yi haka ba, daure dai ki karba kada ki sace mini iska mana, wannan gaisuwar ai ba a yiwa garabitins mutane."
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Na kwakkwabe fuska na ce "Ba dama na kira ka dan na gaishe ka, ka dauki wayata? Ba dama a yi maka haihuwa ko k'arin girma ko wani abin jaje ya same ka, ko iyalinka na kira ka amsa mini, ba kuma zaka biyo ni daga baya ba tabbacin ka manta da ni, ka shafe ni gabadaya a zuciayrka da tunaninka alhalin ina da hakkin zumunta a kan ka!
Na fada idanuwana na tara kwalla.
Ya dan diririce ya ce "Oh no Maigado kin sani, ba yadda za'a yi na manta ki bare na shafe ki, asalima ke ce kadai a kullum nake tunawa sau ba adadi kullum yaumin, ko kin manta ina da Maigado junior a gidana? Kullum sai ance Bilkisu sama da sau goma a gidana. Kin tabbatar kuma ba yaudara ko dadin baki zan miki ba, sunanki na sanya mata. To a duk sadda aka kirata Wallahi sai na tuna ki, wani lokacin na murmusa, wani lokacin na tausaya".
Na yi kasa da kaina don na gasgata shi. Murya ba amo na ce "To amma me yasa ka yanke hulda da ni Baban Bilkisu?"
Kaitsaye ya ce "Na yi kuskure ki mini uzziri zan gyara, amma ki sa ni ba wai yadda kike so haka zan miki ba domin kowa da yadda yake managing abubuwan da suka dabaibaye shi a wannan rayuwar."
Na saki gauron numfashi na ce "Amma dai ni ce kawai ka takaita yadda zaka mu'amalance ni, ko na na ce ka datse mu'amalar bakidaya"
Nan ma ba ja in ja ya ce "Hakane kada kuma ki dauka tsana ce ko wani abune a raina marar dadi, kawai haka na tsinci kaina amma zan yi iya kokarina na gyara din kamar yadda na yi alkawari."
Hawaye ya zubo mini na goge da tissue na ce "Na gode ".
Ya kasa ce wa komai kawai sai na ga ya yi gaba ya bar ni cikin karfaffan takunsa amma bai iya furta kalma ko guda ba.
Washagarin da aka kaita kuwa sai ga shi sun shirya kasaitaacciyar walima ta abokansu da mu ahalinsu da bamu tafi ba.
Kana ganin yadda aka shirya walimar da nau'ikan abinci da nama da kifi hade da lemuna kasan sun shirya abinsu tuni.
Cikin nutsuwa da walwala aka gudanar da walimar, an ci, na sha, aka yi nasiha taro ya tashi, suka tafi gidansu, muma muka shige namu gidajen wadanda suka zo daga waje ma'ana abokan arzikinsu suka tafi nasu gidajen suma.
Ni dai na kasa daina mamakin wanna kasafi na Abida da Yaya Sulaiman. Kallo d'aya zaka masa ka gane ya gama rasuwa a kanta, yayin da ita baka isa gano alkiblarta ba. Kawai abin da nake kallo daya ne, da bata sonsa ba zata yi alkunya ko Kawaicin aurensa akan dole ba, ba da Abida za'a yi kawaicin cutar kai ba.
Surayya Dee
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: *Na kammala wannan shafin na ji rasuwar da ta girgiza