zo mana Bilkisu ".
Na tashi na bar su Ansari tare da Mami. Ya rike kunnena alamun kashedi ya ce "Kada ki sake na ji kin furta maganar nan a gaban mami ko yaran can. Sai mun gama daidaitawa zasu ji a bakina".
Na ce "In sha Allah kuwa! Amma ka ga alamun zata amince kuwa? Sannan sai ka yi hakuri da Abida domin tana da wani irin tsatssauran ra'ayi".
Ya murmusa tare da yin juyi sannan ya ce "Handsome guy kamata bata isa ce wa ban yi ba" .
Na yi dariya na ce "To ai ita bata son maikyau fa!.
Ya zabura ya ce karya take yi, kawai bata samu tsayayye irina ba ne, tunda kuma jarumi take so ai magana ta kare domin ni din jarumine ko cikin jarumai".
Na yi dariya na ce "Yabon kai dai babu kyau Yaya Sulaiman".
Ya fita yana fadin "Gaskiya na fada, ke ma kuma kin sani. Ra'ayinta kuwa idan akan gaskiya take ai ba ni da matsalar hakan, idan kuma na ga wanda ba zan daukesu bane ai tuni zan taka mata birki, don ba zan yaudare ta bare kuma na yaudari kaina".
Cikin doki na tafi sashen Momi. A dakinmu na tarar da Abida ta fito daga wanka tana zaune tana tsane jikinta da tawul. Amrah na gefenta tana cin Cheese wadda na ga ta siyo mata dazu a hanya, tunda sadda zamu tafi Ansari ya fita da ita gidan Yaya Usman.
Na zauna na kalle ta sai na ga ta yi kicin kicin da fuska. Jikina ya yi sanyi domin hakan alamace na ba zata tattauna komai a yanzu ba.
A hankali na ce "Abida ya ya batun Yaya Sulaiman kuwa, shi din ya yi?"
Na tambaya cikin tararrabi.
Ta matso manta ta hau shafawa tamkar ba magana na yi mata ba. Sai kuma ta numfasa ta ce "Kyaunsa ya yi mini yawa, inka cire wannan ba shi da wani nakasu, ya yi ".
Na saki ajiyar zuciya cikin kwantar da murya na ce "Ba shi da wani kyau fa Abida! Kin fi shi kyau ai".
Ta girgiza kai ta ce "Kin sani yana da kyau Maigado."
Na ce "amma ai kyaun bai yi wani tsananin a zo a ga ni ba Abida!
Ta dauke kai tare da ce wa "Kin san Allah kada ki nemi ki wani zake a harkar nan. Domin ba irin kamfen din da ban yiwa Yaya Asad ba kika shafawa idonki toka. Shine yanzu zaki zo kina mini wani rawar jiki?"
Na zabura na ce "Ai dai bai zo gabana ya furta mini soyayya ba. Haka ma Yaya Faruk din da nake so bai zo da nufin gaskiyar magana ba. Ki daina wannan maganar Abida!.
Ta numfasa ta ce "Na barta adalcin da nake yi miki ba wani wanda ya nuna jarumtar tunkarar ki da maganar soyayya sai kame kame. Nima kuwa duk wanda suke son nawa duk haka suke yi hannunka mai sanda shiyasa na ce babu jarumi a cikinsu ".
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Na kyakyale da dariya tare da ce wa ki ce "Yaya Sulaiman ne jarumin tunda ya dunfare ki kaitsaye."
Kafin ta ce uffan muka ji ana kwankwansa mana kofar dakin.
Ganin Abida babu kaya a jikinta ya sanya na tashi na nufi kofar.
Kawai sai ganin Yaya Sulaiman na yi a tsaye ya yi wanka ya sauya kaya, sai kamshi yake yi"
Na murmusa na ce "Da alama dai sosai muka shake wuyanka yayanmu".
Ya murmusa ba tare da ya ce kanzil ba. Ya yi baya ya ce "ki ce mata ina jiranta".
✏️
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Na dawo dakin na tarar tana zaune ba wani alamun motsin a tare da ita. A hankali na ce "Ya ce na fada miki yana jiran ki."
Kai kawai ta daga tabbacin ta ji abin da na ce.
Amma shudewar mintina talatin tana faman busar da gashinta da hand dryer, ba wani sauri ko gaggawar ana jiranta. Zuciyata sai tsallen badake take tare da fargabar Yaya Sulaiman bai samu karbuwa a zuciyarta ba.
Murya ba amo na ce "Abida Yaya Sulaiman fa na jiran ki".
Kafin ta bani amsa wayarta ta hau kuwwa. Amrah da take game a wayar ta mika mata da hanzari.
Ba walwala ta amsa. Ban ji me aka ce mata ba.
Na dai ji ita ta bada amsa da ce wa "Rigar da na yi nufin sakawa yau ashe na mance ban karbo a wajen matar Yaya Faruk ba".
Ta yi shiru tana sauraronsa.
Ta numfasa ta ce "Ina da wasu kayan da yawa ma kuwa, sai dai ba wacce nake son na saka a yanzu sai waccar da bata gidan nan."
Tsawon lokaci tana rike da wayar da alamu suka nuna magiya yake yi mata da rarrashi.
Ta numfasa ta ce "Tom!.
Tare da kashe wayarta ta kalle ni ta ce "Ya ce ki kai masa mukullin motata don wacce yake hawa fitilunta duka sun lalace."
Na zuba mata ido tare da mamakin yadda ta zabi ta aike ni alhalin ko Amrah zata iya kai masa tunda ta shekara shida.
Na dauki mukullin motar na ce "Amrah maza sauri ki kaiwa Uncle key ga shi can a kofar shigowa nan".
Wayar na hannunta ta yunkura.
Amma sai Abida ta zuba mini ido sosai ta ce "Ke ya ce ki masa, kuma nima ke nake son ki kai din".
Ganin ba wani wasa a fuskarta ya sanya na mike ina fadin "Idan na kai din Abida ba abin da zan ragu da shi".
Na fice da sauri. A bakin kofar shigowar sashen na gan shi yana tsaye cak da shi. Idan har da gaske bata son kyakkwan namiji to zai yi wahalar gaske ta karbi soyayyar Yaya Sulaiman.
Na murmusa na ce "Oh Yaya Sulaiman!
Da hanzarinsa ya miko mini hannu ya ce "Ba ni dan Allah sauri nake yi."
Na ba shi cikin madaukakin mamaki domin ban yi zaton yadda yake matukar kamewa a gabanmu zai so Abida irin haka ba.
Na juyo ina jinjina sha'anin Ubangiji don babu wani shiri ko jituwa a tsakaninsu asali Yaya Sulaiman irin mutanan da suka fi son rayuwa a wajen da babu hayaniya, amma aka jarabce shi da son murdaddiya kuma yar hayaniya irin Abida.
A fili na ce "Gidanku akwai kallo kuwa.
Na zabi na zauna a falon momi cikin shauki nake sosai domin na jima ban ji faricinciki irin wanda nake ciki a dalilin wannan lamarin ba.
Momi ta fito dauke da tiren da baba Babba ya ci abinci.
A tausashe ta ce "Maigado ke kadai a nan?"
Na fara kunkuni ina fadin "Gaskiyar magana Yaya Asad ya bata mini suna!
Ta murmusa ta ce "ban da Bilkisu wa ce ce mai gadon zinare duk duniya?"
Ta bawa kanta amsa da fadin "Babu sai sarauniyar shaiba".
Na murmusa na ce "Ai ina ga ba shii da lambata yanzu, tunda aka fada mini an masa karin girma zuwa A.C.P na jihar Oyo nake ta nemansa bana samunsa, sau daya dai ta yi ringing amma har kusan wata guda bai biyo ni ba".
Ta ce "Ki yi masa uzziri ayyukan da suke kansa masu nauyine kin san shi da kazar kazar ganin hakan ya sanya shugabanninsa suke sakar masa aiyyuka masu nauyi da yawa ".
Na ce "Hakane cikin gaskata ta domin tabbas Yaya Asad ya zama babban mutum ya yi kudi na gaske tun shekaru uku baya, ya samu manyan kudade na bada labari.
Matarsa da yayansa sun zama zarra duk da mu din ba talakawa ba ne. Amma dai shi kam ya yi kudi irin danyen kudaden nan ta bakin Abida.
Momi ta fito ta sake ganina a tukure a falon tunda na kasa na tsare ina dakon dawowar Yaya Sulaiman na ga yadda zata kaya.
Yayin da momi ta ce "Hala yar sababin ta rufe miki kofar?"
Na girgiza kai tare da fadin "ko kadan momi waya na yi".
Ta wuce tana ce wa "au to ba laifi ".
Ba'a wani jima ba ya shigo a gaggauce rike da leda a hannunsa, waya a kunnesa, sai dai duk da hakan sai da ya yi sallama, na amsa ina binsa da idanuwa.
Kaitsaye ya miko mini tare da ce wa "Ga ta nan zata kawo miki. Pls Abida mintina goma sun ishe ni. Ina son ganin kine kawai."
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Mamaki ya sake mini k'awanya dama Yaya Sulaiman zai iya doguwar magana haka?"
Ya katse wayar ya kalle ni ya ce "Da alamu dai Abida ta koya miki son jin kwakwaf ko?"
Na fadada murmushin da nake yi na ce "mamaki nake yi akan lamarinka da Abidan Baba".
Ya ce "oya wuce ki kai mata ban son tsurku"
Na wuce da azmaa ina faman kyalkyala dariya.
Na tarar da ita a tsaye da alamu dakona take yi. Na mika mata, ta karba ba tare da ta ce mini uffan ba.
Ta shige bayi bata wani bata lokaci ba ta fito sanye da riga.
Na bita da kallon tu'ajjibi, domin rigar irin ta shan iska ce, tabbas doguwace har kasa amma ba yadda za'a yi a fita da ita, domin irin yadin nan ne mai rawa a jikin mutum bayan haka hannun rigar irin armless din nan ne. Na zuba ido ina son ganin yadda zata fita da rigar a haka.
Ba zato na ga ta zaro katon hijab dinta mai matuk'ar kyau da ya sha guga ta dora a kan rigar, ya rufe ta ruf.
*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke dacewa da amsu jiki ko sirara.*
*08163761797*
da ke mun riga mun saba da kanbasa, mun saba sai mun yiwa kayanmu kafin mu shiryasu a wadirof, kamshin hijabin ya iso har hancina.
Amrah ta kalleta ce "Ammi kin yi kyau".
Ta murmusa tare da fadin "Thank you Amrah dear.
Ni dai ido na bita da shi, ko menene hujjar tura shi karbo rigar da ba za'a yi ado a fita da ita ba?
Asalima ta rufe ta da hijab, na numfasa ina dada bin ta da ido.
Na kasa hakuri na ce "Ni kam Abida dan Allah menene hujjar karbo wannan rigar duk zatona ta alfarma ce kwalliya za ki yi ta mussaman da ita ".
Ta galla mini harara ta ce "Bilki ki kame bakinki akan sha'anin nan, kinsan dai ke ba ki isa ki mini kanzagi ko taya shi neman yardata ba kamar dai yadda kika nuna ban isa na taya Yaya Asad neman yardarki ba".
Nan da nan na diririce na ce "me ya taso da wannan maganar kuma Abida? Ba ki ga rabon ya'yan da na haifa ba na Yaya Asad ba ne? Ashe ke har yanzu kallona kike yi da abin alhalin shi ya mance ma gabaya da ni?"
Ta ce "Hmm idan bai manta da ke ba, za ki aura miji biyu ne?"
Na ce "To ko dai shima a kullace yake da ni ne? Dan idan har lissafina daidai ne rabona da na amsa wayarsa tun haihuwar Amrah. Duk sadda na kira da nufin na gaishe shi kuwa wayar zata yi ta ringing amma ba zai dauka ba, ba kuma zai biyo bayan kiran ba! Na jijjiga kai na zarce da fadin "Ashe shata layi ya yi da ni, alhalin ni ya kamata na masa irin haka tunda ya yi mini sanadin rasa Yaya Farouk."
Na fitittike ina zayyano asarar da ya janyo mini ban da dai ina da taushin zuciya har na sake nemansa da nufin yin zumunta da shi. Amma lallai kina da son kai har ki kullace ni tsawon lokaci irin haka Abida? Babu damuwa na gode sosai amma ki sa ni, ni ba zan taba miki son kai ba. Idan zuciyarki ta amince da Yaya Sulaiman fine. Idan bata amince ba fine, don ba ni zan zauna miki ba, bare na nade kafar wandon tallata miki shi by fire by force ba"
Ganin da ta yi na dan motsa kwanjina ya sanya ta hadiye komai don tasan yana wahalar gaske na bude baki na kare kaina idan tana mini sababi, idan kuwa har na yi to ta kure ni ne, hakan kuma dabi'ata ce kowa ya sani kafin na yi korafi sai tura ta kai bango kwarai da gaske. Ba tare da ta sake ce wa kanzil ba tasa kai ta fice tare da janyo kofar sai dai bata rufe gabaya ba, na tabbatar kuma bata yi zaton ba zata rufu ba don ta tsani a bar kofar a bude.
Sai da na shiga bayi na fito na kalli Amrah barci ya sure ta ga wayar Abida na gefenta. Na girgiza kai domin nan duniya Amrah kadai ke da lasisin taba wayar Abida ba yaron da ya isa ma ya tunkarevta da nufin ta ba shi wayarta, ko ni bata yarda ta ara mini tunda can bare yanzu.
Na tabbatar da dukkan zuciyata take son Amrah.
Na nufi falo a hankali tamkar munafuka.
Na tsaya ina sauraraon Abida na ce wa "Na kyautar da abin da zan fara haifa tun shekaru goma da suka shude ga Bilki".
Na ji Yaya Sulaiman ya yi guntuwar dariya ya ce "Funny girl! Yanzu ki yi kyautar da d'a babu yardar babansa, kuma wa ya ba ki tabbas din za ki haihu ne?"
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Na kasa kunne ina murmushin jin dadi.
Ba wani kunbiya kunbiya ta ce "Na dai sanar maka ne dan ka sani akan wannan alk'awarin nake rayuwa".
Yadda kike so haka za'a yi Abidan Baba."
Yaya Sulaiman ya fada a takaice.
Daga haka ta ce "To gobe ka je wajen Baba k'arami ko baba Babba ka ce a daura auren".
Na kasa gane nufin Abida daga zance daya sai aure, na tabbatar ba sonsa ta afka mai nauyi ba.
Ilai kuwa sai jinsa na yi ya ce "Aure Abida! Ban hango soyayyata irin soyayyar da nake miki a idanuwanki ba, ban gan ki cikin shaukina ba, sai ki ce aure kamar wasan yara?"
Yana rufe baki ta ce "oh bata mini lokaci ka zo yi ke nan?
Ka ce kana sona, kana son aurena, na fada maka cewar abin da muka haifa a farko ba namu bane, ka ce ka amince babu matsala, na ce to ka fito sai kuma ka ce baka ga soyayyarka a tare da ni ba? To shike nan nemi wacce zaka ga soyayyar ". Ta mike tsaye da nufin tafiya.
Ya yi maza ya mike shima ya ce "Ba hakan ba ne Abida wai da so nake mu dan fahimci juna ko ya ya ne, sai maganar auren ta biyo baya."
Ta juya da nufin barin falon ya yi maza ya sha gabanta ya ce "Ba fa abin fada bane Abida ki fahimce ni mana"
Ba walwala ta ce "Na fahimce ka da kyau amma gaskiya ba ni da lokacin yin soyayyar da zaka ganta a idanuwana a yanzu dai, is better ka nemi wacce zaka gane hakan."
Ya ce "Abida kamar dai kora kike mini da hali. Harshenki babu laushi a kaina ko kad'an"
Kafin ta ba shi amsa baba Babba ya shigo don tunda ya tafi sallar Isha bai shigo ba.
Ganinsu tsaye cirko cirko ya sanya ya ce "A a Sulaiman da Abida yau a tsaye babu fada?"
Ta zabura ta ce "Ai kuwa fadan zamu yi da yafi na baya muni Baba".
Nan da nan baba ya ce Assha Abida ba za'a yi hakan ba da ikon Allah ".
Shi dai Yaya Sulaiman ya kasa ce wa komai.
*Kun tuna Umm Nihla mai yadinkan Yan gayu da Yabin Bulkacuwa ta yi ta kece raini da su?*
*Tana nan tana kawo muku Su Zuka zuka, na alfarma, amintattu, akan farashi mai rahusa*
*Malaysianfabricsng*
07020695644.
Baba ya zauna ya ce "Ku zauna na ji ba'asin fadan da zai barke bayan yanzu kin yi hankali".
Abida ta yi fit ta ce "Tunda ya dawo yake bina da kallon da yake takura ni, na so na kawo kararsa sai na hakura tunda ba ni da hujjar kawo karar. Kwanaki biyar da suka shude ya tsananta bin diddigina tare da fara yi mini magana, yanzu kuma tunda ya ga Bilki ta zo ya sake tsananta shiga shirgina na yi hakuri ban ce komai ba. Yau sai ya zo ya ce yana sona, yana son ya aure ni. Na fada masa na fa kyautar da abin da zan fara haifa ga Bilki, ya ce ya amince da hakan .
Sai na ce to ya zo wajenka, ko wajen Baba karami a daura auren."
Ba murna bare godiya sai kawai ya hau sarhutun wai bana sonsa, bai hango soyayyata a idanuwana ba da sauran maganganu masu nauyi har da ce mini bai ganni cikin shauki ba. Wato yaudarata zai yi a cikin gidanmu Baba?"
Baba ya tuntsure da dariya tare da fadin "Ho Abida!
Yayin da Yaya Sulaiman ya zama gunki ya kasa cewa komai.
Ta fara tafiya tana ce wa "To kada ya sake mini wani kallo na daban sannan tunda ba aure za'a yi ba, to ya rabu da ni,da zancen wata soyayya ban iya ba ".
Baba ya ruko ta ya ce "Ba haka za'a yi ba, ba ki fahimce shi daidai ba, yana nufin ku fahimci juna, ku dan tattauna har ku sami daidaito sannan ya sanar mana."
Nan da nan Yaya Sulaiman ya samu kwarin guiwar ce wa "Thank you Baba that is exactly what I mean".
Baba ya juya ya ce "kin ji ba? Zauna ku cigaba da tattaunawar ai ba za'a yi rikici ba, ahalin Allah yana shirin gwada karfin ikonsa a kanku, ko a mafarki a ka nuna mini hakan zai faru zan yi kokwanto bare a zahiri. Amma ikon Allah yafi ga hakan."
Yana rufe baki ta ce "Allah Baba ba zan iya ba, ban son kallon da ya tsiri yi mini irinsa, sannan idan ya kira ni a waya baka ji yadda yake yin kasa da murya ba, tamkar ta sabon mashayi ko mai shekarariyar mura. Na yi ta fadin ban ji ba, ban ji ba, kai