Dingishin Kwado Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Salma Category :  Adventure

Chapter   6 / 37

15K to 18K   out of 110.8K words

ni, ban san shi ba, amma nasan Haj Rabi Sani madakin Gini*

*Allah ka jiqan Hon Mamuda Sani madakin Gini! Allah yasa aljanna makoma*

*Taaziya ga Anty Rabi Sani*

*16/06/25*

Washegari har azahar basu bude sashinsu ba. Mun so zuwa ni da Yaya Munira amma muka hakura.

Again washegari ina ta son na je amma na kasa tunda angon bai fito ba, ga shi da yamma Sahal zai zo mu tafi.

Yaya Hamida sai mita take yi akan bare baren da nake yi na son sai na je ganin kwakwaf. Ban tanka ba domin itama na ga a cike da ni tana mini kallon na fi son su Yaya Munira a kanta. Wanda ba hakan ba ne ko kadan illa shakuwa da muka yi da su, tunda tare muka taso.

Ana fara kiraye kirayen sallar azahar ta karfe daya na ga fitowarsa da ke sashinsu ne a kusa da tsakiyar tafkekekiyar harabar gidanmu. Na yi maza na fito tare da ce wa mami bari na yi sallama da amarya na ga maigidan ya tafi masallaci.

Cikin sauri nake tafiyar tamkar za'a dakatar da ni.

Yaya Munira ta kwalla mini kira tana daga sashensu. Na daga mata hannu tare da ce wa yi mini hakuri Yaya Munira yanzu zan zo".

Na murda kofar da ba'a rufe da mukulli ko jamlock ba.

Kamshi turare da na spice's din Amreesh spicy kana.... Ya bugi hancina. Na zauana a falo ina kallon aljannar duniya. Kafatalin ya'yan gidanmu ba wacce ta samu rabin kayan Abida duk da mu din ma kowa an mata na ke ce raini tunda iyayenmu masu wadata ne kwarai da gaske basa yi mana kwange kuma.

Na dinga jin karar hand dryer, sanin baya nan ya sanya na doshi dakin nata kaitsaye. Na yi turus a dalilin daga ita sai tawul ga gadon a yamutse kayan barcinsu a waste a kasa.

Ta zuba mini ido ta bude baki zata yi magana sai kuma na ga ta yi maza ta hadiye ta cigaba da taje gashinta.

Na ce "Amarya kina sha'aninki, kin ga irin annurin da yake fita a dukkan jikinki kuwa?"

Daidai lokacin ta kammala ta zare dryer daga jikin soket ta dauki comb tana kara taje wa, sannan ta saka ribbon ta kame shi daga kasa ba'a tsakiya ba. Na sake ce wa "yanzun ma ba za ki kama gashin a tsakiyar kai ba ta yadda daurin kallabin zai fi tafiya da yayanmu?"

Ta rausayar da kai ta ce "Hmm Maigado zan ga ranar da za ki daina nausa mini kuttu. So kike na tufke gashi a tsakiyar kai na siffantu da matan da Annabi ya siffanta masu tozo a kansu ya kuma tsine musu albarka. Dan ina son na burge shi, ko dan na yi kyau sai na yarda na shiga sahun matan da Annabi ya kwashe musu albarka shekaru dubu da y'an kai da suka shude ko?"

Na ce "Ai na ga mijinki kawai za ki yiwa kwalliya ne".

Da sauri ta ce "Idan sai na yi artificial abu da na burge shi, ko na yi masa kyau to tabbas ba zan taba burge shi ba. Na riga da nasan ko karkashin tsinuwar babanka ka shiga ko ta limamin unguwarku ai ka gama lalace wa bare ta ma'aikin Allahu."

Na yi maza na ce "hakane Abidan Baba."

Daga haka ta mike na zuba mata ido a bubbude take tafiya, ta bude wadirof ta fito da kaya, ta shirya a gabana. Sannan ta kwashe kayansu da nake da tabbacin gogan ne ya watsosu kasa. Ta gyara gadon tsab. Na kalle ta na ce "sannu Abida."

Ta murmusa ta ce "Kai Bilki sake ce mini sannu, wato abin nan da yake zama sanadin samun baby's babu sauki fa, bare idan ka hadu da karfaffan namiji mai jarumta kwanaki uku kacal har na gundura ina tunanin zan iya kuwa?

Amma da zarar na tuna na hau turbar da zan haifo miki da ko diya sai na yi maza na hadiye komai na kara jarumta".

Da azama na isa gare ta, na rungume ta ina jin sonta na huda duk wani sashe na jikina. Aurenta da Yaya Sulaiman sai ya sake ninka soyayyarta a zuciyata da gangar jikina gabadaya, a wannan ranar na gane manufarta na son na auri wani cikin yayunta don ta yi mu'amala da gidana sosai.

Ta dago ni tana share mini kwallar idona ta yi murmushin gaske ta ce "Yadda kike sona haka nake son ki Maigadona!

Na murmusa na ce "Na dade ban ji farinciki mai yawa irin yau ba Abida na gode sosai Allah ya zaunar da ke lafiya a dakinki, Ubangiji ya ninka soyayyarki da tausayin ki a zuciyar mijinki ya baku lafiya da zuria mai albarka ".

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: A hankali ta ce "Ameen dear. Amma fa idan ya so ni fiye da hakan zai susuce ne, a dai kara masa tausayina da hakuri da ni kawai Maigado"

Muka kyalkyala da dariya gabadaya.

Can ta tsuke fuska sosai alamun ba wasa zata yi ba, ta ce "Idan kin tafi ki aiko mini da sanyi flusher din nan, na Bojuwa herbs, na rantse miki na ji dadinsa sosai na gamsu da shi."

Wannan karon ni na kwashe da dariyar na ce "Ni wacece ta dinga sababin ba zata sha ba? "

Kaitsaye ta ce Abida ce amma ai kinsna a likitance bamu yarda da shan maganganuwa gargajiya barkatai ba, to shi sanyi flusher din na gamsu da tsabtarsa an riga an dafa shi duk wani bakteriya da ido ba zai iya ga ni ba ya kone. Haka nan kaza da ciccibi suma sun dahu sannan tare ake dafasu da saiwowin maganin dan haka suma na yi accepting dinsu da dukkan zuciyata."

Na murmusa na ce "To da su da kazar sababi din za'a hado ke nan?"

Ta dauke kai ta ce "Idan kin so ki hado da ita".

Na tsananta kallonta na ce "Tsumin saiwowin fa? Shima ai ya dahu don shi sai ya kwana ma a kan murhu yana shan wuta ".

A takaice ta ce "Hado da shi Bilki!

Na dinga tuntsura dariya sosai, don kuwa ba karamin sababi ta yi mini ba da na aiko mata da bridal package akan wai ita nake nufin za ta sha maganin gargajiya?"

Sai ga shi da kanta ta nema tun ba'a je ko ina ba. Na sani kuma yadda ta ga sabbin robobi da containers ake zuba magungunan ya yi matukar nutsar da zuciyarta mai kyankyami.

Da yake tana bukatar kayan da gaske sai ta k'i yarda ta hasala ta ce "Na ji dadin marata ne da na sha sanyi flusher din sosai, yanzu kuma da ake zuba maka abu kullum, bayan idan ya je Katsina yana shiga toilet din da ba shi kadai zai shiga ba, dan haka dole na dinga yin rigakafi. Har antibiotics zan tanadar mana".

Na murmusa na ce "Na fahimce ki Dr matar likita".

Na kankance murya na ce "Da dukkan alamu dai Abidan Baba ba dakila ba ce, sannan yayana jarumine a komai".

Ta yi maza ya dauke kai tana fadin "Kin banu da son irin wadannan zantukan sola".

Na kwashe da dariya don da gaske kunya ce ta yi mata k'awanya.

Daga haka muka fita zuwa dayan dakin muka yi sallah.

Mun fito muka zauna ta ce "Maigado tashi ki lalubo mana abin kusa da baka mana".

Na ce "Wai yaushe zaki fara ba ni girmana ne Dr Abida?".

Ta yi murmushin nan nata mai burge kowa ta ce "Yaya Maigado wai da yake ke din y'argidace a zuciyata da gangar jikina ba zai yiwu kuma na mayar da ke bakuwa a gidana ba" .

Nan da nan ta kashe ni da dadin kalamanta na ce "Kin yi gaskiya Abidan Baba".

Na ajiye mayafin na shiga kicin, girman kicin din ya kai kurewa haka nan kayan da aka zuba mata sun sake mayar da shi na garari.

Shauki ya debe ni kawai na ji so nake na yi musu snack da girki.

Dan haka na fara aiki sosai tunda duk abin da nake bukata akwia tunda ga kan kifi da nama da kaji shake suke a freezer.

A shekarun baya kowa yasan yadda Funtua take da isasshiyar wutar lantarki.

Na fito da naman saniya na debi iya tsoka na ajiye a gefe, na ciro kaji biyu tare da kifi.

Da yake tana da na'ura kala kala nan da nan aikin nawa ya tafi, na yi grinding nama don samosa da meat pie zan yi masu dama na yi musu frozen, gefe kuma na dora ferfesun kaji, kifi kuwa na cikin oven ina gasawa. Jollof rice kuma tana daf da kammala a rice cooker.

Ina cikin kwashe shinkafar na ji shigowarsa. Zuciyata ta buga da na ji ya shigo da wakar you're my queen.

Na sandare a tsaye cikin mamakin Yaya Sulaiman.

Na tsinci kaina da lekensu, ya zauna daf da ita ya jata jikinsa yana tambayar ta shafa maganin ko su je ya shafa mata tunda dazu ta ce sai ta yi wanka.?"

A hankali ta ce "Na shafa tun dazu har yanzu kuma bai daina zugi ba, ga tafiyata a bude".

Ya shafa bayanta yana fadin sorry zuwa gobe za ki zama normal, nima zan daure na yi hakuri har zuwa goben".

Ta ce "zuwa gata dai gaskiya".

Cikin wata kalar murya ya ce "A a ban yi alkawari ba, mu bar shi dai zuwa jibin ".

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Daga haka ya dagota ta zauna sosai ya mike yana fadin ""me kike yi ne ya cika gidan gabadaya da kamshi mai taso da dukkan tsohuwar yunwa?"

Bai jira cewarta ba ya doso kicin din na yi maza na kauce daga saitin da nake lekensu.

Ya tsaya a bakin kofar da ya ganni ina faman nadin samosa.

Ya murmusa ya ce "Well-done Bilkina".

Ya yi maza ya yi waiwaiye don shine kalmar da shekarun baya take saka Abida ta hassala da shi.

Ta ce bari waiwaiye na jika sai dai ai ka tabbatar mini ni ce taka ba ita ba".

Ya fadada murmushinsa bai ce komai ba.

Yayin da na bishi da da wani irin kallon farinciki. Ina ta mamakin wai Yaya Sulaiman ne yake baza soyayya ni ban yi zaton ma zai iya kula mace ba, bare ya lalace mata irin haka.

Na ce "Oh Yaya Sulaiman ashe dai dama Abida ta dade da kanainaye mini kai"

Ya juya yana fadin "Ban son shiririta yi maza ki kawo mana abin da kike girkawa pls,".

Na shirya shinkafa da gashasshen kifi na kai musu. Na dawo à kalle ni tare da ce wa "Oya zo ki yi joining dinmu".

Na rausayar da kai na ce "a a ban kammala aikina ba".

Ban bar gidan ba sai kusan la'asar, da na kammala sai da na shirya musu a cikin leda sannan na saka a firiza.

Da zan tafi muka rungume juna muna hawaye sai na tuna haka muka yi lokacin aurena. Duk yadda auren Abida ya yi jinkiri da Allah ya kawo lokacin an yi an wuce wajen. Na tsinci kaina da yiwa matan da suke fuskantar jinkirin aure adduar Allah ya yanke musu ya kawo mijin aure na nagari.

A bangaren momi na iske Yaya Munira tana dakinmu. Zaune take dirshan kan gadon Abida na kyalkyale da dariya na ce "Kina son hawa gadon nan dai Yaya Munira! Ga naki ko kewarsa ba kya yi?"

Na fada ina zama akan gadon da shine nawa.

Ta murmusa ta ce "Gadon yar sababi ai tunda bata tafi da shi ba soyayyarta gare shi bai kai ba

Na ce "Ai ta ce zata dauki abinta ba zata rabu da shi ba har tsufanta".

Muka yi dariya gabadaya.

Daga haka na yunkura na ce Yaya Munira bari na je mu yi sallama da Yaya Hamida anjima zan wuce."

Ta ce ai kuwa sun fita da Yaya Salaha cikin gari".

Na koma na zauna ina ce wa "To bari na baki soyayyar da Abida suke barza ita da take fadin bata son soyayya ba kuma zata yi ba"

A yammacin ranar na koma Kano. Shi ya zo ya dauke ni.

Muna tafe ina ta yi masa hirar soyayyarsu Abida. Ya ce "sai suke burge ki ko?"

Da azama na ce "Sosai ma Baban Amrah!

Ya numfasa ya ce "Mun yi soyayyar da tafi tasu k'arfi, har yanzu ma ban yi zaton zasu kere mu ba, sai dai sabon abu sabone akwai wannan shaukin."

Na yi yake na kame bakina ina rasa ta yadda zan masa bayanin halin da nake ciki ya gane ya dauki mataki.

Lafiya muka isa Kano. Na cigaba da harkokin sana'ata haka aikina. Sannu a hankali Sahal ya daina fita ya yi dan bugebugensa sai ya yini a gida a kan gado sallah take fita da shi.

Idan na dawo na gan shi akan gado ko a zaune yana kallo ko karatun jarida sai na ji gabadaya kunci ya mamaye ni, sai dai ba halin na nuna tunda a wanccan lokacin ina jin tsoron kada ya ce dan ina aiki, ina masa hidima shiyasa nake yi masa gatsali.

Karshen wata kuma haka zai bini mu yo shopping din kayan masarufi da komai na bukatar yau da kullum kamar sadda muke yi da yana aiki. Haka zai kwasowa kansa inner wears da turaren da yake sanyawa har ma da abin yin askinsa (sheving stick).

Ban taba gajiya ko jin wani abu ba. Don ni da kaina nake siyo masa shadda da yadika masu tsada su yi anko da Yaya Farouk, haka na siyo namu ni da Amrah.

Bai gama rufa shekara da rasa aikinsa ba komai na dawainiyar gidansa ya dawo kaina, ya sakar mini gabadaya. Bana damuwa da hakan tunda yana yawan yaba mini tare da gode mini, a duk sadda na yi hidimar da ya kamata ace shi ya yi sai ya ce "Allah ya ba ni damar da zan jiyar da ke dadin da ya zarta wanda na jiyar da ke a baya, ina son na samu damar da zaki gane ni din namijine da yasan alheri."

A duk sadda ya ce hakan kuwa na kan yi murmushin da nake jinsa tunda ga zuciyata dan haka kullum nake sake yi masa hidima kan hidima da karfina da aljihuna. Kullum ina cikin mm lissafin abinda zamu ci da wanda zamu yiwa y'ay'anmu hidimar makaranta da sauran dawainiyar yau da gobe.

[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Shi kuma ya sake nadewa ya bar mini dukkan wahala babu tausayi, ga shi duk wahalar da nake kwana da yini wajen rike masa gida, ba zaisa da daddare na samu nutsuwar da ta dace da ni ba.

A haka har aka shafe watanni takwas da auren Abida sai dai shiru bata da ciki ta dai yi bari, watanni biyu da bikinsu har yanzu kuma wani bai samu ba .

Yanzu suna shirin komawa Katsina da zama gabadaya don a watan jiya ta samu sauyin aiki zuwa cikin babban asibitin Katsina.

Zaune nake a falona hannuna rike da kofin da na zuba masa sanyin flusher don tunda na shiga wani toilet da muka je wayar da kan mata masu juna biyu akan muhimmancin shan folic acid, matsuwa ta kama ni na shiga bayin duk da na kwara ruwan kafin na tsugunna amma sai nake ta jin marata ba daidai ba, haka nan na fara ganin farin ruwa na fito mini, shiyasa na yi maza na yi order dinsa don na gasgata kyaunsa, na kuma gamsu da ingancinsa tunda Dr Abida ta yaba shi. For your order 08032773332.

Ya shigo ya zauna kusa da ni ya ce "Ina son na gan ki sanye da wadannan material din na Malaysia suna yi miki kyau suna kuma dacewa da kowanne yanayi ga taushi ga rashin nauyi abin birgewa basa kodewa duk sadda za ki saka tamkar ranar a dinkasu."

Na murmusa na ce "Ai Malaysianfabricsng siyan kayansu ribace babba, ga sauki sannan Kano take turosu kai tsaye daga Malaysia Idan kuma ba a kano kake ba ma za'a tura maka kaynaka duk inda kake ka karba cikin aminci."

Ya ce "na gasgata ki Billyna!

Na ce kin sanya yadin yangayu irin na Yabin Bulkacuwa da Maigado ko kuwa? Idan ba ki taba sanyasu daure ki jarraba siyansu zaki mini hodiya saboda yadda zaki ji dadin sanyasu.

Materials ne masu aji, masu class, na masana sirrin gayu irinsu jacquard, luxe, viscose, dobby, embroidered jacquard da dai sauransu. Materials masu quality masu dadin sakawa a jiki basuda zafi basuda nauyi.

07020695644.

Ya mika hannu ya ce "me kike sha?"

Na mika masa ya ga ni ya kurba kadan ya mike mini ya ce "Dadina da maganin nan babu dacin da za'a ce wai ka zuba zuma shiyasa nake shansa".

Na yi murmushi don kuwa sanyi flusher kadai yake sha amma duk sauran maganganuwa da nake karba masa har da na karfi da kuzari da ya sha sau daya to ba zai sake sha ba, sai dai ya barsu sai na gaji da ganinsu raina na tafasa zan kwashe na zubar.

A haka dai rayuwarmu ta cigaba da gungurawa, tun yana dan fita yana y'an harkokinsa ya samo ko ba yawa har ya tsike ya daina fita da sunan neman kudi tunda kudadena sun wadacemu ba kuma na yi masa iyaka ko na jira ya ce mini yana bukatar kudi, don duk watan duniya sai na cika mana moticinmu da mai, sannan da hannuna na dauki daya daga cikin ATM dina na bashi tare da fada masa lambobin sirrin. Duk da dai a lokacin ce mini ya yi an turo masa kud'i.

Wani zuwa da Abida ta yi Kano daga Zaria zasu yi seminar a asibitin Murtala na kwanaki biyu, duk da an basu masauki sai ta taho gidana, bata sauka a inda aka basu ba cikin kwanakin biyun ta fahimci halin da nake ciki duk yadda ta so dauke kai ta kame bakinta kasawa ta yi. Ni kuma cike nake da zullimin kada Sahal ya yi mata abin da zaisa ta tunzura ta

6 / 37