Babanku".
Na ce "To Alla ya kaimu ya kuma kawosu lafiya".
Ta amsa da "ameen".
Washagari kuwa tare da Baba karami suka dawo. Na jima ina karewa Yaya Sulaiman kallo domin ya zama zabgegen saurayi na k'asaita .Kammanina da shi sun sake bayyana karara. A tsaye yake cak tamkar dai Yaya Asad, banbancin yafi Yaya Asad haske. Ba farine kamar ni ba, amma kuma ba za'a shi a sahun bakake irinsu Baban Bilkisu ba.
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Hoton fuskata na ga ni a fuskarsa sai banbancin gemu da kuma hasken fatata da sauran abubuwan da zasu banbanta jikin mace da na namiji. Amma tabbas muna matukar kama da juna.
Na tafi lissafin shekarunsa domin shekaru shida ya bamu. A lokacin shekarunsa talatin da uku. A wanccan lokacin gani ake yi ya zama tuzuru domin dukkan sa'aninsa da ma wanda ya girma sun yi aure har sun haihu.
Tun filazal Yaya Sulaiman dan gaye ne kuma dan bokone na gaske. Amma da ya dawo na fahimci ya samu cigaba mai yawa, ya goge da ilimi da kuma wayewar rayuwa.
Sadda suka iso ni da Abida muna farfajiyar harabar wajen adana motoci, gidan Yaya Faruk zamu je yini.
Da girmamawa muka gaida Baba karami.
Ya kalli Abida ya ce "Maryam kin huce, kin daina fishin?"
Ta dauke kai i tana fishi fishi kunya kunya ba tare da tanka ba.
Ya ce "Ato gara kisan matakin dauka dan kuwa tabbas babu maganar wata makaranta kuma sai a dakinki. Ke ko sha'awar yanuwanki da kike ganinsu da yaransu ba kya ji?"
Da shagwaba ta ce "To Baba sun duk sun samu mazan ni kuwa fa?"
Ya zabura ya mata dakuwa tare da yin kanta zai kai mata bugu.
Ta yi maza ta goce ta falfaala bata tsaya ba sai da ta bada tazara, sannan ta tsaya tana dan haki.
Ya ce "Mutane nawa suna zuwa wajenmu da sunan sun gan ki suna so, kina yin tsallen albarka kina fadin ba da yawunki suka zo ba?"
Ta kasa amsa masa. Ya yi kwafa ya ce "wannan karon kam ko ni ko ke na gaji da iyashegen ki, inma jinnul ashuq ne akanki zasu ci iyayensu dan kuwa na shirya yin arangama mai zafi da su".
✏️
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Daga ni har Yaya Sulaiman muka kwashe da dariya domin yadda Baba ya furta jinnul ashuq akwai ban dariya kwarai da gaske, yayin da ita kuma ta sha mur.
Haka muka tafi gidan Yaya Faruk tana ta gungunin ita bata da mashanshani, don kuwa duk wanda ake lissafin sun zo da sunan suna sonta ba jarumai bane ba kuma mijinta a ciki. Don ta yi imani da akwai mijin da kaddara ta zaba mata a cikinsu da tuni ta yi auren ai.
Muka isa gidan Yaya Faruk muka tarar yana shirin tafiya gidan gona. Ya dinga marabtarmu cikin barkwanci.
Haka ma matarsa domin a yanzu kam gaisuwar girma da arziki muke yi ta daina tsananta mini.
Ya zauna ya ce to ku gaisa da matar gidan ku sha ruwa sai mu tafi gidan gonar mu yini a can ko sarauniyar shaiba?"
A duk sadda ya ce hakan har cikin raina nake jin sunan. Tare da tasowar al'amura masu yawa a kansa.
A sanyaye na ce "To Yaya Faruk".
Ya saka hannu ya dauki mai sunansa da ya yi barci tun a hanya. Yana fadin my name sake tashi ka ga Yaya Faruk senior."
Na murmusa ba tare da na ce komai ba.
Ya kalli Abida ya ce "Autar momi wai har yanzu ba ki huce ba ne?"
Ta sake zumbura baki amma bata tanka ba.
Ya sassauta ya ce "Indai kin san akwai wanda yake sonki ki ba shi dama mana, ba fa wacce su Baba suka daga mata kafa irin ki. Ina jiye miki kada ki yiwa kanki sanadin da zaki ji sun bada aurenki ga wanda suka ga ya dace"
Ta murmusa ta ce "Ba maganar a mini auren dole Yaya Faruk. A wannan karnin? Da ilimina?"
Ta girgiza kai tabbacin ba mai yiwuwa ba ne.
Na zuba mata ido ba tare da na furta komai ba. Wato Abida asalin feminine ce.
Ya Farook ya kalle mu ya ce "Rigunan jininku sun mini kyau. Ban cika ganin abayas irin haka ba anan".
Abida ta ce "Bilki ta siya mana a wajen Umm Aslan &Asalah. Egyptian abayas ne kasan sune original. Ya ce gaskiya sun yi kyau sosai nima zan baki ki siyowa Jamila irinsu ".
201121544627 da +2349162662750 Kawai ta tuntube ta a WhatsAp sai ta zaba da kanta idan kun tura kudin, sai na karba muku a Kano tunda anan kayanta suke sauka.
Haka muka rankaya muka nufi gonar ladi farms da kwandon abincinmu matarsa ta hado mu da shi.
Yadda muka zo a motar Abida haka muka shiga ya ja muka yi gaba yayin da ya shiga tasa ya bimu a baya.
Gabadaya gidan gonar ya sake habaka, dukiyar dabbobi kala daban daban a ciki iya ganinka. Haka nan an gyara ta gyra na mussaman domin har zuwa ake yi da sunan yawon bude ido. Sosai ake hada hadar kasuwanci a ciki. Madara da yogurt din da ake sarrafawa a ciki na manyan kudade ne masu matukar nauyin gaske. Hatta kwai a kullum ana diban sama da dubu talatin ban da wanda suka fashe, shiyasa ma'aikatan wajen suma yawane da su tamkar me, an samu cigaba ta hanyar samarwa matasa masu yawa aikin yi
Yaya Faruk ya sake zama babban mutum kudi ya zauna masa duk da shi kadai ne a Funtua cikin yayyanmu. Amma yana cikin daula don idan kana gidansa ma sai ka zaci kana Abuja ne cikin rikunin uguwanni masu daraja.
Duk yadda nasan ladi farms girmanta ya kai kurewa amma a wannan ranar da na shiga cikin shekaru na hankali, ina kuma cikin nutsuwa sosai, na tsorata da irin girmanta da tarin dabbobi da shuke shuke. Don yanzu har 'katon runbun abinci an gina ta yadda ake adana kayan amfanin da aka nomawa a ciki.
Jikin mangwarori suka yi parking muka yi shimfida muka zauna. Gabadaya wajen yabanya ce ga danshin k'asa a dalilin duk safiya da maraice sai an jona tiyo a duk inda aka yi shuke shuke ko inda koriyar ciyawa take.
Duk yadda shekarun nan suke tafiya Yaya Faruk bai canja ba. Zama yake cikinmu a rak'ashe duk mai matsala ta zano masa, shi kuma zai saurare ka da kunnen basira ya kwantar maka da hankali ya kuma baka shawara ta gaskiya.
A yau kam Abida ce ta dinga jero masa laifukan Momi. Ashe duk yadda soyayyar Abida bata boyuwa a wajen Momi yanzu zaman nasu ya fara tsami bisa dalilai guda biyu. Ita Momi aure take so Abida ta yi, dan haka ta matsa lambar sai ta fito da miji, bayan haka mafi yawa bata bari ta yi dinkuna ko saka kayan alatu bisa hujjar wai maza zasu kasa dunfararta da sunan aure tunda suna ganin matsayin aikinta da matsayin gidansu, kaya masu tsadar gaske kuma zasu sake kaita kololuwar
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: matsayi.
Ya yi dariya ya ce "Hakuri za ki kara yi, lamarin iyaye dole a bisu yadda suke so. Sannan ni kaina so nake ki yi auren Abida! Menene ya rage miki ne? Aure kuma shine suturar mace. Duk zurfin karatun da zaki yi, matukar ba ki da aure kin rasa wata kariya ta mutuntaka da aure kadai ke bawa mace shi. Ki nutsu ki sassauta burinki, ba yadda za'a yi ki samu irin teste din ki, domin no body is perfect a cikin wannan rayuwar."
Ba walwala ta ce "Aure lokaci ne fa yaya Faruk. Kuma ni ba wani dogon buri ko wani tsatssauran ra'ayin na dauka ba. Kawai wanda zuciyata ta nutsu ne ban samu ba, amma ko yanzu idan na samu wanda na aminta da shi zan gabatar da shi. Akan me za'a matsa mini har sai na je na auri wanda ba mijina ba ne?.
Muka kwashe da dariya. Na kasa ce wa komai domin yanzu zata sauke mini fishinta da take fama da shi, na sani. Yaya Faruk ne ya ce "Dama ana auren mijin da ba naka ba ne autar momi?
Da dukkan zuciyarta ta ce "sosai ma domin idan na auri wrong person ai ban auri mijina ba domin na fada cikin garari da talajaurar duniya".
Ya gintse dariyarsa ya ce "Da ikon Allah na gari za ki aura albarkacin adalcin da iyayenmu maza suke yiwa iyayenmu mata ba za ki yi aure inda za ki wulakanta ba. Fatana ki kwantar da hankalinki. Ki bude zuciyarki ki fahimci manufar iyayenmu ".
Anan muka yi sallar la'asar.
Wajen karfe biyar sai ga Yaya Sulaiman ya iso akan machine.
Yaya Faruk ya kalle shi ya ce "Baka son yin tuki ne?"
Da walwala ya ce "Da kafata na yi rabin tafiyar.
Sai kuma na hau machine domin daga bakin gate din nan ma shigowa ciki ba karamin tafiya ba ce mikakkiya".
Yaya Faruk ya ce "Ka yi kokari, ka kuma motsa jikinka.
Na kalle shi na ce "Yaya Sulaiman sannu da zuwa dama na k'osa mu hadu".
Ya zauna yana ce wa "Ga ni "Bilkisu sarauniyar shaiba in ji Yaya Faruk ".
Muka murmusa gabadayanmu ban da Abida da dama ba wani jituwa suke yi ba tun filazal.
Ya kalle!ta ya ce "Autar momi saboda Allah har yanzu ma da kika girma ba zamu shirya ba? Tunda na dawo sau uku kika bude baki kika mini magana fa".
Yana rufe baki ta ce "To ai sau ukun muka hadu."
Ya ce" yau fa?"
*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*
*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*
*08163761797*
Kaitsaye ta ce "Dazu bamu gaisa ba? Yanzu kuma daga zuwanka sai na ce make me?"
Ya girgiza kai tare da ce wa "Ho Abida! To sannu da yammaci ".
Ta amsa da fadin"Sannunka dai Yaya Sulaiman".
Daga haka ta tsuke bakinta yayin da ni nake ta fadin "Allah Yaya Sulaiman ya kamata ka yi aure tun baka bari Ansar ya kutso da maganar aure zai yi ba".
Ya galla mini harara tare da ce wa"Ya yi mana an fada miki ni ina da gaggawa ne duka ma shekaruna nawa ne, haka kawai kun damu da maganar society akan aure aure, to wai idan mutum ya ce ba zai yi ba, shike nan ba zai shiga aljanna ba ne kome kuke nufi?"
Nan da nan Abida ta fashe da ce wa "Yauwa Yaya Sulaiman gara ka zo ka taya ni fahimtar da su. Wacce irin masifa ce haka da mutanen da suke da ilimi amma suke runtse idanuwansu da fahimtar komai lokacine. A yi ta damun mutum ya yi aure, ko ma ace ya ki yi gabadaya wai a dole sai sun barranta mutum daga shiga inuwar ma aikin Allah. Haba haba na gaji da ra'ayin hausawa akan aure. Zamana a Lagos shine mafi dadi a rayuwata domin ba yadda za'a yi a tsangwame ka akan aure."
Yaya Sulaiman ya tausasa harshensa ya ce "Yo ke ma da kike daka ta tasu kina bata ranki a banza. Ba ki samu wanda ya dace da ke ba, ba kuma zaki yi auren dole ba, shike nan ki tsaya akan ra'ayin ki fak'at!
Yaya Faruk ya ce "Kai kuma kalar na ga girman ke nan Sulaiman? Ana shawo hankalinta akan ta bawa masu sonta dama su kwankwasa kofar da ta kulle zaka sake ingizata akan ra'ayinta?"
Da dukkan gaskiyarsa ya ce "Ba zugata nake yi ba. Amma ban son a saka ta yi rushing."
Daga haka ya ce "Yogurt nake son sha".
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Nan da nan aka mika masa gabansa domin tun dazu an kewaye mu da shi.
Wajen karfe shida na yamma muka bar gidan gonar.
Yaya Sulaiman ya karbi mukullin motar Abida ya shiga mazaunin direba.
Na yi maza na shige baya domin a yanzu ban cika son na zauna gaban mota ba matukar ba ni zan ja ko Baban Amrah ke jan motar ba.
Na san Abida kuma tun filazal bata kaunar zaman gaba tafi gane ta hakince a owner's corner ana janta, dan haka na rigata shigewa baya.
Kan dole ta shiga gaban motar tunda ta sani a shekarun baya ma Yaya Sulaiman bai yarda ya zame mana direba ba, bare. kuma yanzu da ya sake wayewa ainun.
Maimakon ya bi ta cikin gari sai kawai ya bi ta bayan gari wanda nisan tafiyar ya sake nunkuwa. Sannu a hankali yake tukin. Ni da shi sai hira muke yi yana ta mamakin yadda Amrah ta yi tsawon kafa tamkar ba yar shekaru shida ba. Da kansa kuma ya ce ko da yake Babanta ai dogone na gaske, ke ma kuma ba'a magana ".
Na yi dariya tare da ce wa"Ga uwarta nan a kusa da kai, ni uwar Yaya Faruk ce kawai".
Ya ce "Hakane, amma idan an zo maganar kama ai dole a jinginawa Sahal ita don kuwa kamar ya yi kakinta ne".
Na yi shiru ban ce komai ba.
Jin haka sai ya yi gyaran murya ya kalli Abida da tunda ta zauna ba ta ce kala kanzil ba.
Ya ce "Dr ya ya dai?"
Ba sukuni ta ce "fine".
Ya murmusa tare da ce wa "Amma ba kya cikin yanayi mai dadi. Duk sai na ji nima am not in the mood."
Ta muskuta ta ce "Akan me za'a takura ni sai na yi aure akan dole? Bana son kowa. Ni hana ni tafiya karatun nan ma basu san sun sake nesanta zuciyata da son auren ba ne gabadaya ".
Da wata irin murya ya ce "To yanzu Autar momi kawai ki yi hakuri ki tsayar da miji a yi auren, ana yi sai ki tafi karatunki".
Murya a dashe ta ce "Ni ba wanda zan tsayar, duk zugugun da ake yi mini na ki tsayar da miji alhali ina samun masoya, ai duk basu cancanta ba ne. Ba wani jarumin gaske a cikinsu mitisew..! Ta ja dogon tsaki mai nuna kololuwar takaicin da ke zuciyarta.
Ga mamakina sai jin Yaya Sulaiman na yi cikin wata kankanuwar muryar da zata kai sako cikin zuciya ya ce "Autar momi ina ganin zan shiga sahun yan takara ko zan yi sa'a na zama jarumin kawai".
Gabana ya fadi sosai don kuwa nasan Abida sarai ba amince wa zata yi ba.
Ga shi na lura da gaske ya fada sonta ba kadan ba.
Tsawon lokaci muna dakon amsarta daga shi uban gayyar da ni yar tsurku.
Ya numfasa ya ce "Kin yi shiru autar momi."
A takaice ta ce "To me zan ce ne? Baba babba ne ya ce ka neme ni ko kuwa Baba k'arami?"
Da azama ya ce "Ko kadan Wallahi Abida! Zuciyatace ta harbu da son ki tunda na duro k'asar, har yau ban samu sassauci akan lamarinki ba. A farko na karaya da na ga yadda ake dauki ba dadi da ke akan aure. To amma zuciyata ta kasa jarumtar hakurin da na yi niyyar yi, don bana son na takura ki".
Ta numfasa tamkar zata yi magana sai kuma ta tsuke bakinta ta ki tankawar.
Cikin taushi da lallashi ya ce "Son ki nake yi tun ma ban gama fahimtar hakikanin son ba. Tun kuna Bakori. Idan za ki tuna ranar da Yaya Asad ya zo tare da y'ansanda suka kakkame muku ke da Baba da Bilki tun ranar na kamu da son ki. Ki bani dama, mu tattauna mu fahimci juna, idan akwai alheri Allah ya amintar da zuciyoyinmu, ba tsayawa zamu yi soyayyar shiririta ba, don kuwa dukkanmu ba yara ba ne, fatana dai ace mu dan fahimci juna".
Ga mamakina sai jin Abida na yi cikin murya marar amo ta ce "Allah ya tabbatar mana da alheri"
Murna ta kama shi ya ce "Ameen Ameen na gode."
Gabadaya kaina ya kulle. Me Abida take nufi? Ta amince ne ko kuwa amsa mai harshen damo ta bayar?
Na sani tana iya ce wa dan ta ce Allah ya tabbatar da alheri, ba shine nufin ta amince ko zata amince din ba.
Ya juyo kadan ya ce "Bilkisu ki taya ni fadawa kanwarki ina sonta da dukkan zuciyata, idan ta mini alfarma ta saka ni a zuciyarta to zan zame mata masoyi mai wuyar samu a yau".
[9/16, 3:19 PM] Salma Muhammad: Cikin karaya na ce "To Allah yasa ta amince domin lamarin nata kam babu sauki akan aure gabadaya."
Ya numfasa ya ce "Ni kuma ban fara sonta dan na daina, ko na fasa bisa karamin dalilai ko hujja marar k'arfi ba".
Na nisa na ce "Ubangiji ya tabbatar da alheri".
Ya amsa da fadin ameen ".
Har muka iso gida janta yake yi da zantuka da suka shafi karatunsu na likitanci. Sai ya yi magana uku sannan ta ba shi amsa d'aya a dunkule.
Ni dai na zuba ido ina nazarinsu, sun dace da juna sosai. Amma cike nake da zullumin yadda zata iya ce wa kyaunsa ya yi mata yawa. Domin kyakkwan gaske ne dogo mai cikken jiki. Kamarmu daya da shi sai dai na fi shi fari yayin da shi kuma ya fita haske tunda ita tana da duhu.
Da ya yi parking tana shirin bude motar ya tausasa harshensa ya ce "Tsaya mana ai bamu gama ba."
Ta koma ta zauna babu musu.
Ni kuma sai basirata ta toshe maimakon na fita na basu waje sai kawai nima na fasa fitar na gyara zama.
Ya juyo ya kalle ni ya ce "Saboda Allah Bilki sai na bude baki na ce "Ki dan yi excusing d'ina?"
Na diririce tare da bude murfin kofar ina ce wa "Afuwan!"
Na fita na yi sashen Mami tunda Yaya Faruk na can wanda shekarunsa hudu a lokacin.
Ban san ya suka kare ba, basu rabu ba, sai da aka yi kiran magariba, na ga yaà fito ya tafi Masallaci ita kuma ta shige shashinsu.
Ana idar da sallar ya shigo. Kaitsaye dakina ya wuce yana fadin"