Sooraj Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Maman Teddy Category :  Romance

Chapter   45 / 48

132K to 135K   out of 142.5K words

take iyakanta cinya, gaba ɗaya rigan showing take, ganin dare ne yasa bata wani da muba, kwalban turaren da Hajiya Arabi ta haɗota dashi ta ɗauka takuma shafawa ajikinta, sosai ƙamshin turaren ya cika ɗakin, 
Cikin nutsuwa ta taka harzuwa kan kan gadon, zama tayi abakin gadon tare da kai dubanta garesa, zuwa yanzu ya gyara kwanciyarsa inda yake fuskantar sama,  idanu ta zuba masa tana me kallon  kyakkyawar fuskarsa haɗi da lallausan sajensa, sauƙe idanunta tayi akan golding chain ɗin dake wuyansa sosai yayi mata kyau, hakan yasa taɗan saki murmushi,  cigaba tayi da kallon kyakkyawar fuskarsa, ahankali takai hannunta kan fuskarsa, so take ta shafa lallausan sajen dake kwance akan fuskarsa,  lumshe idanunta tayi alokacin da hannunta ya sauƙa akan tattausan sajen nasa, bazato ba tsammani taji yasanya hannunsa inda ya riƙe nata hannun, da sauri taɗan zaro idanunta waje, don kuwa koda wasa batai tsammanin idanunsa biyu ba,   ahankali ya buɗe lumsassun idanunsa, ya sauƙesu akanta, wani irin yarrr taji ajikinta sakamakon wani irin fitinannen kallo daya jefata dashi,  lumshe idanunta tayi ahankali tare da buɗewa,  cikin nutsuwa ya jawota jikinsa inda ta faɗa kan chest ɗinsa,  cikin wani irin yanayi yake ƙarewa kyakkyawar fuskarta kallo, wani irin kallo me matuƙar kashe jiki yakeyi mata, hakan yasa sam bazata iya jure ganin cikin ƙwayar idanunsa ba, domin kuwa wani irin maganaɗisun ƙaunarsane ke fusgarta, ahankali ya ɗago hannunta, kallon yatsunta da suka sha jan lalle yayi, cikin nutsuwa ya tura ƴan yatsun nata abakinsa, lumshe idanunsa yayi yayinda yasa harshe da laɓɓansa duka biu yana tsotsansu ahankali, wani irin matsanancin daɗi ne ke ratsa jikinta, sosai ɗumin bakinsa dake sauƙa akan yatsun nata, suka sanya taji gaba ɗaya jikinta yayi weak,  cikin wani irin yanayi yasake jawota jikinsa, bakinsa ya ɗaura adaidai saitin kunnenta, cikin unique voice dinsa mai sanya bacci yace.
"I MISS YOU!."

(Kuyi haƙuri yau ina azumi shiasa bansamu nayi muku editing ba)
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

          *SOORAJ!!!*

     *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*

                 *Wattpad*
         @fatymasardauna
#romance

                  *Chapter 56*

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da duban ƴar tasa,  tabbas ko kaɗan bayason tuna irin tsananin wulaƙancin da dangin Maryama sukayi masa, wato dangin mahaifiyarta kenan, sun tozartashi, sun kuma wulaƙantashi duk dan kawai saboda  bashi da kuɗi.
Cikin sanyin murya yace.
"Dangin mahaifiyarki ba suƙita don komai ba saidan aurena da tayi,  mahaifiyarki tasoni duk da kasancewata talaka,  takasance itaɗin kyakkyawar mace ce, don kuwa ko acikin sauran ƴan uwanta na shuwa arab, samun mai kyau kamarta sai an tona, asali mahaifiyarki ƴar garin Maiduguri ce, sannan takasance cikakkiyar shuwa arab,  awannan lokacin shuwa arab basa yarda su auri kowani namiji sai inyakasance daga cikin danginsu ya fito, idan kuwa har takai ga wani bare zasu aura tofa sai ya tabbata cewa shi ɗin mai kuɗine na gaske,    kamar yanda kika sani talaka baya zama akoda yaushe yana cikin fafutukan neman na kansa, sannan yakan iya tsallakawa yabar garinsa ya tafi wata duniya ta daban domin samun abun da zai rufawa kansa asiri, hakanne takasance agareni, inda nayi ƙaura daga garina na tsallaka zuwa garin Maiduguri dan nanemo kuɗi, zuwana Maiduguri shi ya haɗani da mahaifiyarki, inda soyayya mai ƙarfi tashiga tsakaninmu, ko kaɗan bata ƙyamaceni wai dan ina matsayin talaka ba, tana sona fiye da yanda nakesonta, hakan yasa bata sauraran kowa idan bani ba, koda gidansu suka nemi aurar da ita saita bayyana musu kan cewar tana da wanda takeso, sunyi baƙinciki sosai saboda sun so ta auri tsatsonsu, koda sukace takowani su ganni, sai batayi ƙasa a guiwa ba wajen sanar dani, zuciyata cike da fargaba haka na shirya don zuwa gidansu,  sam iyayenta da ƴan uwanta basu taɓa kawowa cewa da talaka take soyayya ba, saboda su atunaninsu wani hamshaƙin mai arziki zata kawo musu, ko kusa basu kawo cewa kamar yanda take da kyau zata iya tsayawa sauraran talaka kamarni ba, haka naje gidansu zuciyata cike da fargaba, koda suka ganni sun cika da baƙinciki haɗi da takaici, nanfa sukayi rantsuwa akan cewa ko mutuwa zatayi bazasu taɓa yarda ta aureni ba,  sunƙirani da maƙasƙanci, mafataucin talaka, sunƙirani da baƙauye, kuma marar ilimi, saboda kwata kwata ni banyi karatun boko ba, saidai kuma bankasance jahili ba saboda nayi karatun islama, dayawan mutane sukan ɗaukan mutum jahili don kawai baiyi karatun boko ba, bayan azahirance kuwa babu jahili sama da wanda baiyi karatun addininsa ba, ko kuma wanda yayi sani ya kuma take sanin,  haka suka ƙaremin cin mutumci da cin fuska, suka kuma gargaɗeni dana fita daga cikin rayuwar ƴarsu,
soyayyar da Maryama mahaifiyarki kemin tana da matuƙar yawa Zieyaderh, haka take wuni take kwana tana kuka, sannan takan hana cikinta abinci, ta kuma hana kanta sukuni duk dan saboda soyayyata, burinta shine iyayenta da ƴan uwanta su aminta ta aureni, sam sukuma idanunsu ya rufe, basaji aransu cewa zasu bari ta aureni, abu kamar wasa haka ta dinga rashin lafiya,  damuwa sukayi mata yawa, sosai tashiga halin tashin hankali,  ganin abun nata yayi tsamari ne yasanya suka ɗauki mummunan fushi da ita, mahaifinta da kansa ya zauna yace mata, tunda ta dage dole saini zata aura shikenan taje ta aureni amma tasani bada sa yawun bakinsa ba, saidai taje can wata uwa duniya aɗaura mana aure, sannan kuma daga ranan da aka ɗaura mata aure dani tasani babushi babu ita, komai yafaru da ita kada tazo masa gida, haka ma ƴan uwanta kowa yace babushi babu ita,  giyar soyayya dake ruɗan zuciyarta yasa tace ta amince, saboda ita dai burinta aduniya bai wuce zama dani ba,  haka tana kuka ta baro ƴan uwanta,  anan cikin garin na Maiduguri mukaje wani masallaci inda nasanarwa da limamin masallacin kaf abun da ke faruwa,  sam limamin baiyi ƙasa aguiwa ba yatara jama'arsa inda yace nabiya sadaki, nan nabada sadakin aurenta naira dubu goma shabiyar aka ɗaura mana aure, tabbas limamin yayi hakane saboda yana gudun mu faɗa halaka, saboda mafi akasarin masoyan da suka tsinci kawunansu a irin wannan yanayi,  sukan faɗawa cikin halaka aduk sanda akace an hanasu auren juna, baya ga kuma suna matuƙar son juna.
Haka aka ɗaura mana aure nida mahaifiyarki inda kaitsaye na wuce da ita ɗan ɗakin dana kama wanda ciki nake kwana, kwananmu biyar a Maiduguri naji gaba ɗaya bazan iya zaman garin ba, hakan yasa natattara ƴan abubuwana, muka taho garinmu Saminaka kenan,  tundaga kan neman auren mahaifiyarki har kama daga kan auren mu babu wani mutum ɗaya a dangina dana faɗawa, koda muka dawo Saminaka iyaye da ƴan uwana suka ganta nakuma gabatar da ita amatsayin mata, shikenan kuma tashin hankali yasoma, tsantsar tsana dangina ke nuna mata, babu ma kamar ya mahaifiyata,  sam basa sonta, acewarsu wai ita kaɗo ce baikamata ina cikakken fulani naje na auro musu ita ba,  auren ma kuma wai ni nayi gaban kaina, haka muke rayuwa watarana daɗi watarana akasin haka, awajena kaɗai Maryama kesamun soyayya, kowa bayasonta, ƴan uwana kyararta suke, har takai ga tsoron shiga cikinsu take, ahaka muka shafe shekaru huɗu da ita, acikin waƴannan shekarun babu wani ɗan uwanta guda ɗaya daya nemi sanin inda muke, sau dayawa nakan isketa tana kuka wanda na tabbata kukan nan na kewar ƴan uwanta ne takeyi, saboda akwai shaƙuwa mai kyau atsakanin su, wanda kuma ƙaddararren aurena da tayi ne ya raba hakan,  tsana da tsangwaman da ƴan uwana keyi mata ya ƙarune alokacin da muka shafe shekaru huɗu   sukaga babu alaman ciki atattare da'ita, nanfa bakin kowa akanta yake kowa sai yana ce mata juya,  sam mutane sukan manta cewa haihuwa da rashinta duk na Allah Ne, sannan Allah Yakan iya tawayan bawa ta kowani fanni, dayawan mutane ƙarancin ilimi da tunani kesa suyin gorin haihuwa, sun manta  ita haihuwa Allah Kan bawa wanda yasone ya kuma hana wanda yaso, hakan kuma bawai yana nuni da cewa Allah Ya hanaka don baya sonka bane, wataƙila hanakan dayayi shine mafi alkhairi agareka, kuma dama shi Allah Baya hana bawa abu dan haka kawai, saidai idan abun ya kasance ba alkhairi bane agareka, kuma komai na duniya yana da lokaci, sannan ƙaddara tana yawo akan kowa,  bayan munshafe shekara huɗu da ƴan watanni Allah Ya azurtamu da samun ƙaruwa, tahanyar bawa Maryama ciki, nayi farinciki sosai, duk da kasancewar awannan lokacin inacikin wani hali na takurar rayuwa, ma'ana talauci yayimin  tsanani, munzauna da mahaifiyarki lafiya koda sau ɗaya bata taɓa ɗaga muryarta akan tawa ba, munyi zaman daɗi da ita, takasance mace me tsananin biyayya da haƙuri, kana takasance me kyakkyawar zuciya, da kuma kyawawan halayya, takanci duk wani abun dana kawo mata komai rashin daɗinsa, aduk sanda bansamo ba kuwa takanyi haƙuri taɗanyi ƴan dabarbarunta wajen ganin tasama mana abun da zamuci,  sosai tasha wahala wajen rainon cikin da ke jikinta, kusan kullum bata da lafiya, amma haka take jurewa."
Ɗan numfasawa yayi tare da sanya hannu ya dafe kansa, zuciyarsa cike take da tsananin danasanin da yayi, haƙiƙa yabiyewa son zuciya, da ruɗin shaiɗan wanda yakaisa ya baro, ci gaba yayi da cewa.
"Cikin Maryama nada wata 5  nawayi gari da wani irin hali, wanda har kawo yau bansan meyasa halina ya canza ba, saidai nasan cewa hakan ma yana ɗaya daga cikin Ƙaddarata, hakanan nakejin wani irin masifaffen son ƙara aure ya shigeni, har takai ga inaji ajikina cewa idan banƙara aure ba hankalina bazai taɓa kwanciya ba,  wallahi nayi rantsuwa Maryama bata taɓa ƙuntatamin ba, hasali tanayimini biyayyya, sam kuma batacancanci zama da kishiya ba, amma saboda hali irin namu na maza hakanan naji ina sha'awar zama da mata biyu, duk da kasancewar bani da kuɗi, saidai dama ance ƙarin aure ajininmu yake mu maza, koda ana zaune lafiya, ko ana tashin hankali idan mukaso sai munyi,  haka naje na jajiɓowa kaina auren Ma'u,  babu wani fargaba bare ɗar haka nazo na tunkari Maryama da batun ƙarin aurena, ko da sau ɗaya banji tausayin halin da zata shiga ba, gashi lokacin da ciki ajikinta, sannan bata da kowa wanda ya wuce ni, akaina tabaro iyaye da danginta, ta zaɓeni sama da kowa, halacci take buƙata agareni akullum bawai butulci ba, amma kuma saidai me zuciyar ɗan adam bata da ƙashi, idanuna sun rufe ƙarin aure kawai nasa agaba, hakan yasa nadaina bata wani ingantacciyar kulawa,  ƴan uwana kuwa dama basonta sukeba, jin batun ƙarin aurena kuwa yasa suka cika da murna, nan fa suke ta yada mata haibaici, ita dai haka take rayuwarta sam bata tanka musu,  koda damuwa yayi mata yawa, saidai ta roƙi Allah Sassauci ko kuwa tashiga ɗaki ta ɓoye kanta tayi kuka, daga bisani kuwa tayi murmushi ta share hawayenta, saboda tasan ƙunci baya taɓa dauwama acikin rayuwar ɗan adam, dole watarana sauƙi zaizo.
Anyi bikina da Ma'u lafiya lafiya, inda na gina mata ɗakinta na laka agefen na Maryama,  satin Ma'u ɗaya agidana ta fara bayyana wasu halaye, sannan lokaci ɗaya yazamana inajin mugun shakkanta, idan tace eh bana iya cewa a'a, haka take juyani son ranta, saikuma taga dama nake kula Maryama.
Akwana atashi cikin Maryama ya cika wata tara da sati biyu cif, awata rana ta jumma'a ne nakuda ya tashi mata, rashin kuɗi yasa ta haihu agida, cikin iko da jin ƙai irin na Ubangiji kuwa ta haihu lafiya, inda ta haifo ƴarta mace,  wannan ƴar bakowa bace face ke Zieyaderh, haka Maryam tayi jegonta cikin rashin jin daɗi, don kwata kwata nadaina kulawa da ita, saudayawa takan sa kanta aɗaki tayi kuka sosai,    sanja halina danayi yasa gaba ɗaya ta rame ta fita hayyacinta, nikuwa ko ajikina, haka nake rayuwa ta da Ma'u, inda komai take buƙata inayi mata, tsananin son zuciya irin tawa yasa na manta da halaccin Maryama agareni.
Haka rayuwa take tafiya babu dadi, aɓangaren Maryama don ma saina ga dama nake shiga ɗakinta, haka take rainonki cikin so da ƙauna, sannu ahankali kike ƙara girma, yayinda kammanninki da Maryama ke ƙara bayyana, harma takai ga kinaso ki ɗarata fari da kyau,   sam namanta da wani haƙƙinku ko nauyinku dake kaina, rayuwata kawai nake gaba gaɗi, ɓangaren Ma'u kuwa kullum ƙara ganin ƙimarta nake, yayinda ita kuma takemin duk wani abun da taga dama,  tun kina ƙanƙanuwa ban baku kulawa keda mahaifiyarki ba, bansan meyasa zuciyata tazama butulu akan halaccin da mahaifiyarki tayimin ba."
Hawayen da suka cika idanunsa yayi ƙoƙarin shanyewa tare da cewa.
"Har mahaifiyata  ta rasu batazama mai ƙaunar Maryama ba, haka ƴan uwana suka dinga rasuwa da ɗai ɗaya,   akwana atashi asaran me rai, haka Maryama ta rasu ban zama mai kyautatawa agareta ba, sannan ko bayan rasuwarta da ƴan uwanta suka zo, sun nuna tsantsar tsana akaina saboda acewarsu talauci da zaman ƙuncine yayi ajalinta, inda suka barmini ke don sunce ke jininace sukuma bazasu karɓi jinina ba, har kawo yau kuwa basu sake nemanki ba, bankuma ƙara jin labarinsu ba, saidai akwai yayan mahaifiyarki Alhaji Ahmad Rufa'e wanda yake cikakken ɗan kasuwa, kana kuma babban  ɗan siyasa, shine ma wani lokaci nake ganin fostan sa, amma bayan haka har kawo yau babu wata alaƙa dake tsakanina dasu."

Hawayen dake tsiyaya bisa kan fuskarta ta sharce, tabbas taji ƙaunar dangin mahaifiyarta ya shigeta, saidai kuma sam abun da sukayi basu kyauta ba, baikamata ace sunyi watsi dasu har haka akan wani ɗan dalili nasu ba.
Duban mahaifinnata tayi cikin sanyin Murya tace.
"Amma Baba baikamata ace donsu sunƙi nemanmu mu muƙi nemansu ba, inasonsu Baba inason naje garesu, naji gaba ɗaya naƙosa don naga ƴan uwan mahaifiyata, tabbas nasan zuwa wannan lokacin sunyi nadama, marar amfani."
Murmushi Baban nata yayi tare da kai dubansa ga Inna Ma'u wacce keta gabzan apple, duk labarinnasu da sukeyi tanajinsu, amma dake kayan kwaɗayine agabanta, yasa komai da hankali garesu batayi ba, don koda ma tamai da hankali itace zataji kunya, don sam bata aikata alkhairi ba.
Girgiza kai baban yayi tare da duban ƴartasa yace.
"Kitambayi Mijinki idan ya baki izini, sai nayi miki jagora harzuwa garin na Maiduguri!."
Murmushi kawai tayi tare dayin ƙasa da kanta.
Sam su baban nata basu wani jima sosai ba suka tafi, dama sunzone dan su dubata, haka Oummu ta haɗa Inna Ma'u da kayan tsaraba Niƙi niƙi, amma sam haka Baban Zieyaderh ya hanata amsa, haka suka kama hanya zuciyar Inna Ma'u acunkushe sam bataso hanata karɓan alkhairin da Oummu tayi mata da yayi ba, ita aganinta kawai yana mata baƙin cikine,don ita dama asontane shine yabarta ta kwana, saboda ko kaɗan bata gaji da cin kayan daɗin da aka narka musu ba,  tabbas itakam Allah Yaga zuciarta tana tsananin son kuɗi, da kayan ƙyale ƙyalen dunia, haka dai tayita surutanta ƙasa ƙasa, kana tana wurgawa Malam Garba'n harara, can ƙasan ranta tace ɗan baƙin ciki.
***
Kwata kwata jikin Pharouk yaƙi daɗi, kasancewar yasamu wani irin mummunan buguwa acikin kansa, sakamakon haɗarin da sukayi, wanda shine sanadiyar komai,  sanadin mummunan buguwan daya samu hakan yasanya koda ya farfaɗo zai dinga yawan ciwon kai  matsananci,    yanzu haka likitoti suna iyaka ƙokarinsu wajen ganin sunshawo kan matsalan nasa, tsoronsu ɗaya shine kada abun ya shafi  brain ɗinsa, inda suka dage tuƙuru wajen yi masa aiki.

Yau amatuƙar gajiye ya dawo gidan kasancewar kwana biu yatarawa kansa aiki sosai a office, sannan ga ciwonsa dake matuƙar yi masa zafi, yana ƙarasowa cikin bathroom ɗin, ya aje briefcase ɗin dake hannunsa tare da sanya hannuwansa duka biu ya kama waist ɗinsa, sosai ya ƙarewa ɗakin kallo ganin babu ita babu alamunta, ahankali yashiga rage kayan jikinsa, inda ya buɗe drawer ɗinsa tare da zaro wani sabon blue ɗin towel,   ɗaura towel ɗin yayi akan waist dinshi, tare da nufar toilet, tsayawa yayi agaban shower tare da sakarwa kansa ruwa,  saida yaji gajiyan jikinsa yaɗan soma warwarewa kafun  ya kashe shower'n,  wani ɗan ƙaramin towel ya ɗauka, yana me tsane ruwan dake kansa.
Koda yafito daga cikin toilet ɗin sama sama ya shafa body lotion ajikinsa, kallon ƙaton agogon dake saƙale  jikin bangon ɗakin yayi, 8:00 pm daidai, drawer ɗinsa ya buɗe tare da ciro wani tree quater jeans ya sanya, da body spray ɗinsa me daɗin ƙamshi ya feshe jikinsa,  wani ɗan ƙaramin set na glass wanda aka matuƙar ƙawatasa ya buɗe, wani ɗan box mai kyau ya ɗauko tare da buɗewa, wata ƴar siririyar chain ne ta bayyana cikin ɗan ƙaramin akwatin irin ta maza, sosai sarƙan keda azaban kyau, duk da cewa siririyace kuma ta maza ne amma tana da kyau sosai,  akan kakkauran wuyansa yasanya sarƙan,  inda ya ƙarasa gaban ɗan madaidaicin fridge din dake cikin ɗakin,  kwalin fresh milk ya ɗauko, tare da bootle water wanda baida sanyi sosai, tablets ɗinsa ya ɗauko tare da ɓare kowanne ya zuba acikin bakinsa, kana yabi da ruwa, ɗaukan fresh milk ɗin yayi tare da ƙarasawa gaban gadon ya zauna, tunda ya ɗaura bakin goran fresh milk ɗin abakinsa bai cire ba, har saida yashanye sa tas, cikin durstbin ya wurga kwalin tare da shigewa bathroom ya wanko bakinsa, kasancewar yayi sallan isha tun kafun shigowarsa hakan yasa kaitsaye ya nufi kan gado, kwanciya yayi luf akan gadon tare da lumshe idanunsa, sosai yakejin gajiya ajikinsa hakan yasa bacci ke fusgarsa.

Zieyaderh kuwa tun da tayi sallan magriba tatafi ɓangaren Oummu, inda acan tasamu wata ƴar aminiyar Oummun tazo, nan Oummu tasa ƴar budurwan mai suna Zainab, ta zanawa Zieyadern jan lalle ayatsunta na hannu, domin kuwa Zainab ɗin ta iya sosae.
yanzuma can cikin ɗakin Oummun take tana shirya mata kayanta acikin trolly, don Oummun tasanar da ita cewa zata koma Kaduna yayinda su kuma zasu koma gidansu, sam Zieyaderh bataji daɗin hakan ba, saboda batason rabuwa da Oummu, Oummu ce tashigo cikin ɗakin fuskarta ɗauke da murmushi, duban Zieyaderh  tayi  haɗi da cewa.
"Shirya kayan ya isa hakanan ae dai ba yanzu bane tafiyan, yakamata ki ɗan sarara ki huta, kuma ma naga dare yayi, ya kamata kije ki kwanta, dan inama tunanin yajima da dawowa."

Kunyane ya rufeta jin abunda Oummun ta faɗa, hakan yasa tayi ƙasa da kanta, ahankali take wasa da ƴan watsunta wanda sukasha jan lalle, cikin sanyin murya tace da Oummun "Saida safe."
Fuska ɗauke da murmushi Oummu ta sa mata tare da binta da kallo harta fice,  sosai takejin ƙaunar

45 / 48